< Judges 16 >

1 And he went Samson Gaza towards and he saw there a woman a prostitute and he went into her.
Wata rana Samson ya tafi Gaza, inda ya ga wata karuwa. Ya shiga wurinta ya kwana.
2 To the Gazites - saying he has come Samson here and they surrounded and they lay in wait for him all the night at [the] gate of the city and they were silent all the night saying until [the] light of the morning and we will kill him.
Aka gaya wa mutanen Gaza, “Ai, Samson yana a nan!” Saboda haka suka zo suka kewaye wurin suka yi kwanto dukan dare a bakin ƙofar birni. A daren nan ba su motsa nan da can ba, suna cewa, “Gari yana wayewa za mu kashe shi.”
3 And he lay down Samson until [the] middle of the night and he arose - in [the] middle of the night and he took hold on [the] doors of [the] gate of the city and on [the] two the doorposts and he pulled up them with the bar and he put [them] on shoulders his and he carried up them to [the] top of the mountain which [is] on [the] face of Hebron.
Amma Samson ya yi kwanciyarsa har tsakiyar dare. Sa’an nan ya tashi ya kama ƙofofin birnin, tare da madogarai biyunsu, ya tumɓuke, ya aza su a kafaɗarsa, ya kai su kan dutsen da yake a fuskantar Hebron.
4 And it was after thus and he loved a woman in [the] valley of Sorek and name her [was] Delilah.
Bayan ɗan lokaci, sai ya shiga ƙaunar wata mace, mai suna Delila a Kwarin Sorek.
5 And they went up to her [the] rulers of [the] Philistines and they said to her entice him and see how? [is] strength his great and how? will we prevail to him and we will bind him to humble him and we we will give to you each one thousand and one hundred silver.
Sai shugabannin Filistiyawa suka tafi wurinta suka ce, “Ki yi ƙoƙari ki ga ko za ki rarrashe shi yă nuna miki asirin ƙarfinsa da yadda za mu iya shan ƙarfinsa don mu ɗaura shi mu yi nasara a kansa. Kowannenmu zai ba ki shekel dubu ɗari ɗaya na azurfa.”
6 And she said Delilah to Samson tell! please to me how? [is] strength your great and how? will you be bound to humble you.
Saboda haka Delila ta ce wa Samson, “Ka faɗa miki asirin ƙarfinka da yadda za a ɗaura ka a yi nasara a kanka.”
7 And he said to her Samson if people will bind me with seven cords fresh which not they have been dried and I will be weak and I will be like one of humankind.
Samson ya ce mata, “In wani ya ɗaura ni da sababbin igiyoyin da ba su bushe ba, zan zama marar ƙarfi kamar kowa.”
8 And they brought up to her [the] rulers of [the] Philistines seven cords fresh which not they had been dried and she bound him with them.
Sa’an nan shugabannin Filistiyawa suka kawo mata sababbin igiyoyi guda bakwai da ba su bushe ba, sai ta daure shi da su.
9 And the ambusher [was] sitting of her in the chamber and she said to him [the] Philistines [are] on you O Samson and he tore apart the cords just as it is torn apart thread of tow when smells it fire and not it was known strength his.
Da mutane a ɓoye a cikin ɗaki tare da ita, sai ta yi ihu ta ce, “Samson ga Filistiyawa sun zo su kama ka!” Da jin haka sai ya tsintsinke igiyoyin kamar zaren da ya yi kusa da harshen wuta. Saboda haka asirin ƙarfinsa bai tonu ba.
10 And she said Delilah to Samson here! you have deceived me and you have spoken to me lies now tell! please to me how? will you be bound.
Sa’an nan Delila ta ce wa Samson, “Ka mai da ni wawiya; ka ruɗe ni. Yanzu, ka gaya mini yadda za a daure ka.”
11 And he said to her certainly [if] they will bind me with ropes new which not it has been done with them work and I will be weak and I will be like one of humankind.
Ya ce, “In wani ya ɗaura ni sosai da sababbin igiyoyin da ba a taɓa amfani da su ba, zan zama marar ƙarfi kamar kowa.”
12 And she took Delilah ropes new and she bound him with them and she said to him [the] Philistines [are] on you O Samson and the ambusher [was] sitting in the chamber and he tore apart them from on arms his like thread.
Saboda haka Delila ta ɗauki sababbin igiyoyi ta ɗaura shi da su. Sa’an nan, tare da mutane a ɓoye a ɗakin, ta yi ihu ta ce, “Samson ga Filistiyawa sun zo su kama ka!” Amma sai ya tsintsinke su kamar zare.
13 And she said Delilah to Samson until now you have deceived me and you have spoken to me lies tell! to me how? will you be bound and he said to her if you will weave seven [the] plaits of head my with the web. (And you will strike with a pin to the wall and I will be weak and I will be like one man. *X*)
Sa’an nan Delila ta ce, “Har yanzu, ka mai da shashasha, kana mai da ni wawiya kana kuma yin mini ƙarya. Ka gaya mini yadda za a daure ka mana.” Ya ce mata, “In kin yi kitson gashin kaina guda bakwai kika ɗaura su da zare kika buga su da akwasha, zan rasa ƙarfi in zama kamar kowa.” Saboda haka yayinda yake barci, sai Delila ta yi kitson gashin kansa guda bakwai ta ɗinka su da zare,
14 (And she made sleep him and she wove seven [the] plaits head his with the web *X*) and she thrust with the pin and she said to him [the] Philistines [are] on you O Samson and he awoke from sleep his and he pulled out the pin of the loom and the web.
ta kuma ɗaura su da akwasha. Ta sāke yin ihu ta ce, “Samson ga Filistiyawa sun zo su kama ka.” Ya tashi daga barcinsa ya tumɓuke akwashan tare da zaren da aka ɗaura gashin kansa da su.
15 And she said to him how? will you say I love you and heart your not [is] with me this three times you have deceived me and not you have told to me how? [is] strength your great.
Sa’an nan ta ce masa, “Yaya kake cewa kana sona alhali ba ka yarda da ni ba? Wannan shi ne sau na uku kana mai da ni wawiya kuma ba ka nuna mini asirin ƙarfinka ba.”
16 And it was that she pressed him with words her all the days and she urged him and it was short self his to die.
Da irin wannan fitina ta tsokane shi kwana da kwanaki har sai da ya gaji kamar zai mutu.
17 And he told to her all heart his and he said to her a razor not it has come up on head my for [am] a Nazirite of God I from [the] womb of mother my if I was shaved and it will depart from me strength my and I will be weak and I will be like every man.
Saboda haka sai ya faɗa mata kome ya ce, “Ba a taɓa sa reza a kaina ba, domin ni Naziri ne keɓaɓɓe ga Allah tun haihuwa. In kuwa an aske kaina, ƙarfina zai rabu da ni, sai in zama kamar kowa.”
18 And she saw (Delilah *LA(bh)*) that he had told to her all heart his and she sent and she summoned [the] rulers of [the] Philistines saying come up this time for he has told (to me *Q(K)*) all heart his and they came up to her [the] rulers of [the] Philistines and they brought up the silver in hand their.
Da Delila ta gane ya gaya mata kome yanzu, sai ta aika saƙo zuwa ga shugabannin Filistiyawa ta ce, “Ku ƙara zuwa sau ɗayan nan, ai, ya gaya mini kome.” Saboda haka shugabannin Filistiyawa suka dawo tare da azurfa a hannuwansu.
19 And she made sleep him on knees her and she summoned the man and she shaved off seven [the] plaits of head his and she began to humble him and it departed strength his from on him.
Bayan ta sa shi ya yi barci a cinyarta, sai ta kira wani ya zo ya aske kitso guda bakwai nan a kansa, aka fara rinjayensa. Ƙarfinsa kuwa ya rabu da shi.
20 And she said [the] Philistines [are] on you O Samson and he awoke from sleep his and he said I will go out as time on time so I may shake myself free and he not he knew that Yahweh he had departed from with him.
Sa’an nan ta yi ihu ta ce, “Samson ga Filistiyawa sun zo su kama ka!” Sai ya farka daga barci yana tsammani cewa, “Zan fita kamar dā in miƙe jikina.” Amma bai san cewa Ubangiji ya rabu da shi ba.
21 And they seized him [the] Philistines and they gouged out eyes his and they brought down him Gaza towards and they bound him with bronze fetters and he was grinding in [the] house of (those imprisoned. *Q(K)*)
Sa’an nan Filistiyawa suka fizge shi, suka ƙwaƙule idanunsa suka gangara da shi zuwa Gaza. Da suka daure shi da sarƙoƙin tagulla, sai aka sa shi yana niƙa a kurkuku.
22 And it began [the] hair of head his to grow back when it had been shaved.
Amma gashi kansa ya fara tohuwa kuma bayan an aske shi.
23 And [the] rulers of [the] Philistines they gathered to sacrifice a sacrifice great to Dagon god their and for joy and they said he has given god our in hand our Samson enemies our.
To, sai Filistiyawa suka taru don su miƙa hadaya ga Dagon allahnsu su kuma yi biki cewa, “Allahnmu ya bashe abokin gābanmu Samson a hannuwanmu.”
24 And they saw him the people and they praised god their for they said he has given god our in hand our enemy our and [the] desolator of land our and who he has multiplied slain [ones] our.
Sa’ad da mutane suka gan shi, sai suka yabi allahnsu, suna cewa, “Allahnmu ya bashe abokin gābanmu a hannunmu, wanda ya lalace ƙasarmu ya kuma raɓanya kisan mutanenmu.”
25 And it was (like good *Q(K)*) heart their and they said summon Samson so he may make sport for us and they summoned Samson from [the] house of (those imprisoned *Q(K)*) and he made sport before them and they made stand him between the pillars.
Yayinda suke cikin farin ciki, sai suka yi ihu, suka ce, “Fito mana da Samson yă yi mana wasa.” Saboda haka aka zo da Samson daga kurkuku, shi kuwa ya yi wasa a gabansu. Sa’ad da suka tsai da shi a tsakanin ginshiƙai,
26 And he said Samson to the young man who kept hold on hand his permit! me (and let feel me *Q(K)*) the pillars which the house [is] established on them so I may lean on them.
sai Samson ya ce wa bawan da ya riƙe hannunsa, “Ka kai ni inda zan taɓa ginshiƙan da suke ɗauke da wannan haikali, don in jingina a kai.”
27 And the house was full men and women and [were] there all [the] rulers of [the] Philistines and [were] on the roof about three thousand man and woman who were looking when sported Samson.
To, haikalin ya cika da mutane maza da mata; dukan shugabannin Filistiyawa kuwa suna a can, a bisan rufin kuwa akwai mutum wajen dubu uku maza da mata suna kallon Samson yana wasa.
28 And he called out Samson to Yahweh and he said O Lord Yahweh remember me please and strengthen me please only the time this O God so let me avenge myself vengeance of one from [the] two eyes my from [the] Philistines.
Sa’an nan Samson ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, ya Allah ka tuna da ni, ka ƙarfafa ni sau ɗaya nan kaɗai, ka bar ni da bugu ɗaya kawai in ɗauki fansa a kan Filistiyawa domin idanuna.”
29 And he grasped Samson [the] two - [the] pillars of the middle which the house [was] established on them and he supported himself on them one in right [hand] his and one in left [hand] his.
Sa’an nan Samson ya kai hannuwansa ga ginshiƙan waɗanda haikalin yake a kai, ya jingina jikinsa, hannunsa dama yana a ɗaya, hannun hagu kuma na ɗayan,
30 And he said Samson let it die life my with [the] Philistines and he stretched out with strength and it fell the house on the rulers and on all the people which [was] in it and they were the dead whom he killed in death his many more than [those] whom he had killed in life his.
Samson ya ce, “Bari in mutu tare da Filistiyawa!” Sa’an nan da dukan ƙarfinsa ya tura haikali ya fāɗa a kan shugabanni da dukan mutanen da suke ciki. Ta haka ya kashe mutane da yawa fiye da yayinda yake da rai.
31 And they went down brothers his and all [the] household of father his and they carried him and they brought [him] up - and they buried him between Zorah and between Eshtaol in [the] tomb of Manoah father his and he he judged Israel twenty year[s].
Sa’an nan’yan’uwansa da dukan dangin mahaifinsa suka gangaro don su ɗauke shi. Suka kawo shi suka binne tsakanin Zora da Eshtawol a kabarin Manowa mahaifinsa. Ya yi mulkin Isra’ila shekara ashirin.

< Judges 16 >