< Joshua 23 >
1 And it was from days many after that he had given rest Yahweh to Israel from all enemies their from round about and Joshua he was old he had come in days.
An daɗe bayan da Ubangiji ya ba Isra’ilawa hutu daga dukan abokan gāban da suke kewaye da su. Yoshuwa kuwa ya tsufa, shekarunsa sun yi yawa,
2 And he summoned Joshua all Israel elders its and leaders its and judges its and officials its and he said to them I I am old I have come in days.
sai ya aika a kira Isra’ilawa duka, dattawansu, shugabanninsu, alƙalansu, da manyan ma’aikatansu, ya ce musu, “Na tsufa, shekaruna kuwa sun yi yawa,
3 And you you have seen all that he has done Yahweh God your to all the nations these from before you for Yahweh God your he [is] the [one who] has been fighting for you.
ku kanku kun ga dukan abubuwan da Ubangiji Allahnku ya yi da idanunku wa dukan ƙasashen nan, Ubangiji Allahnku shi ne wanda ya yi yaƙi dominku.
4 See I have made fall to you the nations which remain these an inheritance for tribes your from the Jordan and all the nations which I have cut off and the sea great [the] setting of the sun.
Ku tuna yadda na rarraba wa kabilanku ƙasashen nan su zama naku na gādo, dukan ƙasashen da suka rage, ƙasashen da na ci da yaƙi, tsakanin Urdun da Bahar Rum a yamma.
5 And Yahweh God your he he will drive out them from before you and he will dispossess them from to before you and you will take possession of land their just as he spoke Yahweh God your to you.
Ubangiji Allahnku kansa zai kore su a madadinku. Zai fafare su a gabanku, za ku kuwa mallaki ƙasarsu, yadda Ubangiji Allah ya yi muku alkawari.
6 And you will be strong very to take care and to do every [thing] written in [the] book of [the] law of Moses to not to turn aside from it right [hand] and left [hand].
“Ku yi ƙarfin hali, ku yi hankali, ku yi biyayya da dukan abin da aka rubuta a cikin Littafin Dokoki na Musa, ba tare da kun juya hagu ko dama ba.
7 To not to go among the nations these which remain these with you and [the] name of gods their not you must bring to remembrance and not you must cause to swear and not you must serve them and not you must bow down to them.
Kada ku haɗa kai da mutanen nan da suke zama cikinku; ba ruwanku da sunayen allolinsu, kada ku rantse da su. Kada kuwa ku bauta musu ko kuwa ku rusuna musu.
8 That except to Yahweh God your you will cling just as you have done until the day this.
Sai dai ku riƙe Ubangiji Allahnku da kyau, yadda kuka yi har zuwa yanzu.
9 And he has dispossessed Yahweh from before you nations great and mighty and you not he has stood anyone in faces your until the day this.
“Ubangiji ya kori manyan ƙasashe masu ƙarfi; har wa yau ba wanda ya iya cin ku da yaƙi.
10 A man one of you he puts to flight a thousand for - Yahweh God your he [is] the [one who] fights for you just as he spoke to you.
Mutum ɗaya a cikinku ya isa yă sa mutane dubu nasu su gudu, domin Ubangiji Allahnku yana yaƙi dominku, kamar yadda ya yi alkawari.
11 And you will take heed exceedingly to selves your to love Yahweh God your.
Saboda haka sai ku kula da kanku sosai, ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku.
12 That - except ever you will turn back and you will cling to [the] remainder of the nations these which remain these with you and you will intermarry with them and you will go among them and they among you.
“Amma in kuka juya baya kuka zama abokai ga waɗanda suka ragu suke zama a cikinku a ƙasashen nan, har kuka yi auratayya da su, kuka haɗa kai da su,
13 Certainly you will know that not he will increase Yahweh God your to dispossess the nations these from to before you and they will become for you a trap and a snare and a scourge in sides your and thorns in view your until perish you from on the land good this which he has given to you Yahweh God your.
ku tabbata cewa Ubangiji Allahnku ba zai kore muku mutanen ƙasashen nan ba, sai ma su zama muku dutsen tuntuɓe da tarko, za su zama bulala a bayanku, ƙayayyuwa a idanunku, har sai kun hallaka daga wannan ƙasa mai kyau wadda Ubangiji Allahnku ya ba ku.
14 And here! I [am] about to go this day in [the] way of all the earth and you know with all heart your and with all being your that not it has fallen a word one of all - the words good which he spoke Yahweh God your on you everything they have come to you not it has fallen of it a word one.
“Yanzu na kusa barin fuskar duniyan nan. Kun sani da dukan zuciyarku, da dukan ranku cewa, Ba ko ɗaya daga cikin alkawuran da Ubangiji Allahnku ya yi, da bai cika ba. Kowane alkawari ya cika; ba ko ɗaya da bai cika ba.
15 And it will be just as it has come on you every word good which he spoke Yahweh God your to you so he will bring Yahweh on you every word bad until has destroyed he you from on the land good this which he has given to you Yahweh God your.
Kamar yadda Ubangiji Allahnku kuwa ya cika kowane alkawari mai kyau, haka ma ba zai fasa kawo muku bala’in da ya faɗi ba, sai ya hallaka ku daga wannan ƙasa mai kyau da ya ba ku.
16 When transgress you [the] covenant of Yahweh God your which he commanded you and you will go and you will serve gods other and you will bow down to them and it will burn [the] anger of Yahweh on you and you will perish quickly from on the land good which he has given to you.
In kuka karya alkawarin Ubangiji Allahnku wanda ya umarce ku, in kuka je kuka bauta wa waɗansu alloli, kuka rusuna musu, fushin Ubangiji zai sauko a kanku, za ku kuwa hallaka da sauri daga ƙasan nan mai kyau da ya ba ku.”