< Joshua 16 >
1 And it went out the lot of [the] descendants of Joseph from [the] Jordan of Jericho to [the] waters of Jericho east-ward the wilderness going up from Jericho in the hill country Beth-el.
Rabon da aka ba wa Yusuf ya fara tun daga Urdun kusa da Yeriko, gabas da ruwan Yeriko, sai ya miƙe zuwa jeji, ya haura har zuwa cikin ƙasar tudu na Betel.
2 And it goes out from Beth-el Luz towards and it passes on to [the] border of the Arkite[s] Ataroth.
Ya ci gaba daga Betel (wato, Luz), ya zarce zuwa sashen Arkitawa na Atarot,
3 And it goes down west-ward to [the] border of the Japhletite[s] to [the] border of Beth Horon lower and to Gezer and they are (extremities its *Q(K)*) [the] sea towards.
ya sauka zuwa yammancin bakin iyakar Yalfetiyawa har zuwa yankin Bet-Horon wanda yake cikin kwari. Ya zarce kuma zuwa Gezer, ya gangara ya yi ƙarshe a Bahar Rum.
4 And they received their inheritance [the] descendants of Joseph Manasseh and Ephraim.
Wannan ne yankin da aka ba wa Manasse da Efraim zuriyar Yusuf gādonsu.
5 And it was [the] territory of [the] descendants of Ephraim to clans their and it was [the] border of inheritance their east-ward Ataroth Addar to Beth Horon upper.
Yankin Efraim ke nan bisa ga iyalansu. Iyakar ƙasarsu ta gādo ta kama daga Atarot Addar a gabas zuwa Bet-Horon,
6 And it goes out the border the sea towards Micmethath [is] from [the] north and it turns the border east-ward Taanath Shiloh and it passes by it from [the] east Janoah.
ta wuce zuwa Bahar Rum. Daga Mikmetat a arewa kuwa iyakar ta karkata gabas zuwa Ta’anat Shilo, ta wuce zuwa Yanowa a gabas.
7 And it goes down from Janoah Ataroth and Naarah towards and it touches Jericho and it goes out the Jordan.
Sai ta gangara daga Yanowa zuwa Atarot da Na’ara, ta bi ta Yeriko, ta kuma fito ta Urdun.
8 From Tappuah it goes the border west-ward [the] wadi of Kanah and they are extremities its the sea towards this [was] [the] inheritance of [the] tribe of [the] descendants of Ephraim to clans their.
Daga Taffuwa kuma iyakar ta bi yamma zuwa kwazazzaban Kana, ta ƙarasa a Bahar Rum. Wannan shi ne gādon mutanen Efraim bisa ga iyalansu.
9 And the cities the separate places for [the] descendants of Ephraim [are] in [the] midst of [the] inheritance of [the] descendants of Manasseh all the cities and villages their.
Gādon ya kuma haɗa da dukan garuruwa da ƙauyuka waɗanda aka keɓe wa mutanen Efraim daga cikin gādon mutanen Manasse.
10 And not they dispossessed the Canaanite[s] who dwelt in Gezer and he has dwelt the Canaanite[s] in [the] midst of Ephraim until the day this and he became a slave gang of laboring.
Ba su kori Kan’aniyawan da suke zama a Gezer ba, don haka Kan’aniyawa suna zama tare da mutanen Efraim har wa yau; amma Kan’aniyawa suka zama masu yin aikin dole.