< Job 9 >
1 And he answered Job and he said.
Sai Ayuba ya amsa,
2 Truly I know that thus and what? will he be justified a person with God.
“Lalle, na san wannan gaskiya ne. Amma ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah?
3 If someone desires to conduct a case with him not he will answer him one [time] from a thousand.
Ko da mutum yana so yă yi gardama da shi, ba zai taɓa amsa masa ba ko da sau ɗaya cikin dubu.
4 Wise of heart and strong of power who? has he shown stubbornness to him and he has remained unharmed.
Hikimarsa tana da zurfi, ikonsa yana da yawa. Wane ne ya taɓa yin faɗa da shi har ya yi nasara?
5 The [one who] removes mountains and not they know [the one] who he overturns them in anger his.
Yana matsar da manyan duwatsu kafin su sani kuma yana juya su cikin fushinsa.
6 The [one who] shakes [the] earth from place its and pillars its they tremble!
Yana girgiza ƙasa, yana girgiza harsashenta.
7 The [one who] speaks to the sun and not it shines and behind [the] stars he puts a seal.
Yana magana da rana sai ta ƙi yin haske; yana hana taurari yin haske.
8 [one who] stretches out [the] heavens To only him and [one who] treads on [the] high places of [the] sea.
Shi kaɗai ya shimfiɗa sammai ya kuma yi tafiya a kan raƙuman ruwan teku.
9 [one who] makes [the] Bear Orion and Pleiades and [the] chambers of [the] south.
Shi ne ya halicci Mafarauci da Kare da Zomo, da Kaza, da’Ya’yanta da tarin taurari a sama, da taurarin kudu.
10 [one who] does Great [things] until there not [is] inquiry and wonders until there not [is] number.
Yana yin abubuwan banmamaki waɗanda ba a iya ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a iya ƙirgawa.
11 There! he will pass by at me and not I will see [him] and he may pass on and not I will perceive him.
Ba na iya ganinsa lokacin da ya wuce ni; ba na sani ya wuce lokacin da ya wuce.
12 There! he will snatch away who? will he turn back him who? will he say to him what? are you doing.
Wane ne ya isa yă hana shi in ya ƙwace abu? Wa zai ce masa, ‘Me kake yi?’
13 God not he will turn back anger his (under him *Q(k)*) they lay prostrate [the] helpers of Rahab.
Allah ba ya danne fushinsa; ko dodannin ruwan da ake kira ayarin Rahab ya tattake su.
14 Indeed? for I I will answer him I will choose words my with him.
“Ta yaya zan iya yin faɗa da shi? Ina zan iya samun kalmomin da zan yi gardama da shi?
15 [I] who Though I am righteous not I will answer to judge my I will seek favor.
Ko da yake ba ni da laifi, ba zan iya amsa masa ba; sai dai roƙon jinƙai zan iya yi ga mahukuncina.
16 If I called and he answered me not I believe that he gave ear to voice my.
Ko da na yi kira gare shi ya amsa mini, ban yarda cewa zai saurare ni ba.
17 [he] who With a storm he crushes me and he increases wounds my without cause.
Zai sa hadari yă danne ni yă ƙara mini ciwona ba dalili.
18 Not he permits me to bring back breath my for he surfeits me bitter things.
Ba zai bari in yi numfashi ba, sai dai yă ƙara mini azaba.
19 If to power a strong [one] there! and if to justice who? will he summon me.
In maganar ƙarfi ne, shi babban mai ƙarfi ne! In kuma maganar shari’a ne, wa zai kai kararsa?
20 Though I am righteous own mouth my it will condemn as guilty me [am] blameless I and it declared guilty me.
Ko da ni marar ƙarfi ne, bakina ya isa yă sa in zama mai laifi; in ba ni da laifi, zai sa in yi laifi.
21 [am] blameless I not I know self my I reject life my.
“Ko da yake ba ni da laifi, ban damu da kaina ba; na rena raina.
22 [is] one It there-fore I say [the] blameless and [the] wicked he [is] bringing to an end.
Ba bambanci; shi ya sa na ce, ‘Yana hallaka marasa laifi da kuma mugaye.’
23 If a scourge it kills suddenly [the] despair of innocent [ones] he mocks.
Lokacin da bala’i ya kawo ga mutuwa, yakan yi dariyar baƙin cikin marasa laifi.
24 A land - it has been given in [the] hand of a wicked [person] [the] face of judges its he covers if not then who? [is] it.
Lokacin da ƙasa ta faɗa a hannun mugaye, yakan rufe idanun masu shari’a. In ba shi ba wa zai yi wannan?
25 And days my they have been swift more than a runner they have fled not they have seen good.
“Kwanakina sun fi mai gudu wucewa da sauri; suna firiya babu wani abin jin daɗi a cikinsu.
26 They have passed on with ships of reed like an eagle [which] it rushes on food.
Suna wucewa kamar jirgin ruwan da aka yi da kyauro, kamar jahurma da ta kai wa namanta cafka.
27 If to say I I will forget complaint my I will let loose face my and I will be cheerful.
‘In na ce zan manta da abin da yake damu na, zan yi murmushi in daina nuna ɓacin rai,’
28 I dread all pains my I know that not you will acquit me.
duk da haka ina tsoron duk wahalata, domin na san ba za ka ɗauke ni marar laifi ba.
29 I I will be guilty why? this vanity will I labor.
Tun da an riga an ɗauke ni mai laifi, duk ƙoƙarina a banza yake.
30 If I washed myself (in water of *Q(K)*) snow and I cleansed with potash hands my.
Ko da na wanke jikina duka da sabulu, na wanke hannuwana kuma da soda,
31 Then in pit you will dip me and they will abhor me own clothes my.
duk da haka za ka jefa ni cikin ƙazamin wuri, yadda ko rigunan jikina ma za su ƙi ni.
32 For not [he is] a human like me I will answer him we will come together in judgment.
“Shi ba mutum ba ne kamar ni wanda zan iya amsa masa, har da za mu yi faɗa da juna a wurin shari’a.
33 Not there between us [is] an arbiter he may put hand his on [the] two of us.
In da akwai wanda zai iya shiga tsakaninmu, ya ɗora hannunsa a kanmu tare,
34 Let him remove from on me rod his and dread his may not it terrify me.
wani wanda zai sa Allah yă daina duka na, don yă daina ba ni tsoro.
35 I will speak and not I will fear him for not [am] thus I with myself.
Sa’an nan ne zan iya yin magana ba tare da jin tsoronsa ba, amma a yadda nake a yanzu ba zan iya ba.