< Job 34 >

1 And he answered Elihu and he said.
Sa’an nan Elihu ya ce,
2 Hear O wise [men] words my and O [those who] know give ear to me.
“Ku ji maganata, ku masu hikima; ku saurare ni, ku masu ilimi.
3 For [the] ear words it tests and [the] palate it tastes to eat.
Gama kunne yana rarrabe magana kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci.
4 Justice let us choose for ourselves let us recognize between ourselves what? [is] good.
Bari mu zaɓi abin da yake daidai, bari mu koyi abin da yake mai kyau tare.
5 For he has said Job I am righteous and God he has taken away right my.
“Ayuba ya ce, ‘Ba ni da laifi, amma Allah ya hana mini hakkina.
6 On right my will I lie? [is] incurable arrow my not transgression.
Ko da yake ina da gaskiya, an ɗauke ni maƙaryaci; ko da yake ba ni da laifi, kibiyoyinsa sun ji mini ciwo wanda ba ya warkewa.’
7 Who? [is] a man like Job he drinks mockery like water.
Wane mutum ne kamar Ayuba, wanda yake shan ba’a kamar ruwa?
8 And he travels for company with doers of evil and to walk with people of wickedness.
Yana abokantaka da masu aikata mugunta; yana cuɗanya da mugaye.
9 For he has said not it profits a man when is pleased he with God.
Gama ya ce, ‘Ba ribar da mutum zai samu lokacin da yake ƙoƙari yă faranta wa Allah zuciya.’
10 Therefore - O people of heart listen to me far be it to God from wickedness and [the] Almighty from unrighteousness.
“Saboda haka ku saurare ni, ku masu ganewa. Ko kaɗan Allah ba ya mugunta, Maɗaukaki ba ya kuskure.
11 For [the] work of a person he will repay to him and according to [the] way of a person he will make find him.
Yana biyan mutum bisa ga abin da ya yi; yana kawo masa abin da ayyukansa suka jawo.
12 Also truly God not he acts wickedly and [the] Almighty not he perverts justice.
Ba zai yiwu Allah yă yi ba daidai ba, Maɗaukaki ba zai yi shari’a marar gaskiya ba.
13 Who? did he assign on him [the] earth towards and who? did he put [the] world all of it.
Wane ne ya ba shi iko yă lura da duniya? Wane ne ya ba shi iko kan dukan duniya?
14 If he will set to it heart his spirit his and breath his to himself he will gather.
In nufinsa ne ya kuma janye ruhunsa da numfashinsa,
15 It will expire all flesh together and humankind to dust it will return.
’yan adam duka za su hallaka tare, mutum kuma zai koma ƙasa.
16 And if understanding hear! this give ear! to [the] sound of words my.
“In kana da ganewa sai ka saurari wannan; ka saurari abin da zan ce.
17 ¿ Also [one who] hates justice will he govern and or? [the] righteous [one] [the] mighty [one] will you condemn as guilty.
Maƙiyin gaskiya zai iya yin mulki? Za ka iya ba mai gaskiya, Maɗaukaki laifi?
18 ¿ To say to a king worthless person wicked [one] to noble [people].
Ba shi ne ya ce wa sarakuna, ‘Ba ku da amfani ba,’ ya ce wa manya ‘Ku mugaye ne,’
19 Who not he lifts up - [the] faces of princes and not he regards a rich person before a poor [person] for [are the] work of hands his all of them.
wanda ba ya nuna sonkai ga’ya’yan sarki kuma ba ya goyon bayan masu arziki a kan matalauta, gama dukansu shi ya yi su da hannuwansa.
20 A moment - they die and [the] middle of [the] night they are shaken a people so they may pass away and people may remove [the] mighty not by a hand.
Suna mutuwa nan take, a cikin tsakiyar dare; an girgiza mutanen amma sun wuce; an taɓa manya amma ba da hannun mutum ba.
21 For eyes his [are] on [the] ways of everyone and all steps his he sees.
“Idanunsa suna kan al’amuran mutane; yana ganin tafiyarsu duka.
22 There not [is] darkness and there not [is] deep darkness to hide themselves there [those who] do wickedness.
Babu wuri mai duhu, babu inuwa mai duhu, inda masu aikata mugunta za su ɓoye.
23 For not on a person he will appoint again to go to God in judgment.
Allah ba ya bukata yă ci gaba da bincike mutane, har da za su zo gabansa don yă shari’anta su.
24 He breaks mighty [ones] not inquiry and he appointed others in place of them.
Ba tare da tambaya ba yana ragargaza masu iko, yă kuma sa waɗansu a wurinsu.
25 Therefore he is acquainted with deeds their and he overthrows [them] night so they may be crushed.
Gama yana sane da abubuwan da suke yi, yana hamɓarar da su da dare a kuma ragargaza su.
26 In place of wicked [people] he slaps them in a place of [those who] see.
Yana ba su horo, don muguntarsu, inda kowa zai gan su,
27 That there-fore they turned aside from after him and all ways his not they considered.
domin sun juya daga binsa, kuma ba su kula da hanyoyinsa ba.
28 To cause to come to him [the] outcry of [the] poor and [the] outcry of afflicted [people] he heard.
Sun sa kukan matalauta ya kai wurinsa yadda ya kai ga jin kukan masu bukata.
29 And he he will keep quiet - and who? will he condemn [him] as guilty and he may hide face and who? will he observe him and over a nation and over a person alike.
Amma in ya yi shiru, wa zai ba shi laifi? In ya ɓoye fuskarsa, wa zai gan shi? Duk da haka shi yake da iko kan mutum da al’umma duka,
30 From reigning a person godless from snares of a people.
yana hana wanda bai san Allah ba yă yi mulki, ya hana shi sa wa mutane tarko.
31 For to God ¿ has anyone said I have borne not I will act corruptly.
“A ce mutum ya ce wa Allah, ‘Na yi laifi, amma ba zan sāke saɓa wa wani ba.
32 Apart from [that which] I see O you instruct me if unrighteousness I have done not I will repeat.
Ka koya mini abin da ba zan iya gani ba; in na yi ba daidai ba, ba zan sāke yi ba.’
33 ¿ From with you will he repay it if you have rejected for you you will choose and not I and what? do you know speak.
Ya kamata Allah yă yi maka bisa ga abin da ka ce ne, sa’ad da ka ƙi ka tuba? Dole kai ka zaɓa, ba ni ba; yanzu ka gaya mini abin da ka sani.
34 People of heart they will say to me and a man wise [who] listens to me.
“Mutane masu ganewa za su ce, masu hikima waɗanda suka ji ni za su ce mini,
35 Job not with knowledge he speaks and words his not [are] with insight.
‘Ayuba ya yi magana cikin rashin sani; maganganunsa na marar hikima ne.’
36 Would that! he will be tested Job until perpetuity on answers among people of wickedness.
Kash, da za a gwada Ayuba har ƙarshe, domin yana ba da amsa kamar mugun mutum.
37 For he adds to sin his transgression between us he claps and he multiplies words his to God.
Ya ƙara tawaye a kan zunubansa; ya tafa hannuwansa na reni a cikinmu ya kuma ƙara yawan maganganunsa ga Allah.”

< Job 34 >