< Job 19 >

1 And he answered Job and he said.
Sai Ayuba ya amsa,
2 Until when? will you torment! self my and will you crush? me with words.
“Har yaushe za ku yi ta ba ni azaba ku kuma murƙushe ni da maganganunku?
3 This ten times you have insulted me not you have been ashamed you have ill-treated me.
Yanzu sau goma ke nan kuna wulaƙanta ni, kuna kai mini hari na rashin kunya.
4 And even truly I have erred with me it lodges error my.
In gaskiya ne na yi laifi, kuskurena ya rage nawa.
5 If truly above me you will magnify yourselves and you may argue on me disgrace my.
In kuwa za ku ɗaukaka kanku a kaina kuna ɗauka wahalar da nake sha domin na yi laifi ne,
6 Know then that God he has wronged me and net his over me he has closed.
sai ku san cewa Allah ya yi mini ba daidai ba ya kewaye ni da ragarsa.
7 There! I cry out violence and not I am answered I cry for help and there not [is] justice.
“Ko da yake na yi kuka cewa, ‘An yi mini ba daidai ba!’ Ba a amsa mini ba; ko da yake na nemi taimako, ba a yi adalci ba.
8 Way my he has walled up and not I will pass and on paths my darkness he puts.
Ya tare mini hanya yadda ba zan iya wucewa ba; ya rufe hanyata da duhu.
9 Honor my from on me he has stripped off and he has removed [the] crown of head my.
Ya cire darajar da nake da ita, ya kuma cire rawani daga kaina.
10 He has torn down me all around and I have gone and he has uprooted like a tree hope my.
Ya yi kaca-kaca da ni har sai da na ƙare; ya tuge begen da nake da shi kamar itace.
11 And he has kindled towards me anger his and he has considered me himself like foes his.
Yana jin haushina ya lissafta ni cikin maƙiyansa.
12 Together - they have come troops his and they have piled up on me way their and they have encamped all around tent my.
Rundunarsa ta zo da ƙarfi; suka kafa sansani kewaye da ni, suka zagaye tentina.
13 Brothers my from with me he has put far away and acquaintances my surely they have become estranged from me.
“Ya raba ni da’yan’uwana maza; abokaina sun zama baƙi gare ni.
14 They have ceased kindred my and acquaintances my they have forgotten me.
Dangina sun tafi; abokaina na kurkusa sun manta da ni.
15 [the] sojourners of House my and female servants my to a stranger they consider me a foreigner I have become in view their.
Waɗanda sukan ziyarce ni, da masu yi mini aiki mata sun ɗauke ni baƙo.
16 To servant my I call and not he answers with mouth my I seek favor to him.
Na kira bawana, amma bai amsa ba, ko da yake na roƙe shi da bakina.
17 Breath my it is loathsome to wife my and I am repulsive to [the] sons of womb my.
Numfashina yana ɓata wa matata rai;’yan’uwana sun ƙi ni.
18 Also young boys they reject me I arise and they spoke against me.
Har’yan yara suna rena ni; in sun gan ni sai su fara yi mini riyar reni.
19 They abhor me all [the] men of council my and whom I love they have turned against me.
Duk abokaina sun yashe ni; waɗanda nake ƙauna sun zama ba sa ƙaunata.
20 On skin my and on flesh my it clings bone my and I have escaped! with [the] skin of teeth my.
Ni ba kome ba ne sai dai fata da ƙashi, da ƙyar na tsira.
21 Show favor to me show favor to me O you friends my for [the] hand of God it has touched me.
“Ku tausaya mini, abokaina, ku ji tausayina, gama hannun Allah ya sauko a kaina.
22 Why? are you persecuting me like God and from flesh my not are you satisfied?
Don me kuke fafarata kamar yadda Allah yake yi? Ba ku gaji da yagar fatata ba?
23 Who? will he give then and they will be written down! words my who? will he give on the scroll so they may be inscribed.
“Kash, da ma a ce ana rubuta maganganuna, da an rubuta su a littafi,
24 With a stylus of iron and lead for ever in the rock they will be engraved!
a rubuta su da ƙarfe a kan dutse don su dawwama har abada!
25 And I I know vindicator my he lives and last on dust he will stand.
Na san wanda zai fanshe ni yana nan da rai, kuma a ƙarshe zai tsaya a kan duniya.
26 And after skin my people have struck off this and from flesh my I will see God.
Kuma bayan an hallaka fatata, duk da haka a cikin jiki zan ga Allah.
27 Whom I - I will see for myself and own eyes my they will see and not a stranger they are faint kidneys my in bosom my.
Zan gan shi da kaina da idanuna, Ni, ba wani ba ne. Zuciyata ta cika da wannan tunani!
28 If you will say what? will we persecute him and [the] root of [the] matter it has been found in me.
“In kuka ce, ‘Za ku ci gaba da matsa mini, tun da shi ne tushen damuwa,’
29 Be afraid yourselves - of [the] sword for rage [is] iniquities of [the] sword so that you may know! (that a judgment. *Q(k)*)
sai ku ma ku ji tsoron takobin; gama fushi yakan kawo hukunci ta wurin takobi, sa’an nan za ku san cewa akwai shari’a.”

< Job 19 >