< Jeremiah 30 >
1 The word which it came to Jeremiah from with Yahweh saying.
Ga maganar da ta zo wa Irmiya daga Ubangiji.
2 Thus he says Yahweh [the] God of Israel saying write for yourself all the words which I have spoken to you into a book.
“Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Ka rubuta a cikin littafi dukan maganganun da na yi maka.
3 For here! days [are] coming [the] utterance of Yahweh and I will turn back [the] captivity of people my Israel and Judah he says Yahweh and I will bring back them to the land which I gave to ancestors their and they will take possession of it.
Kwanaki suna zuwa,’ in ji Ubangiji, ‘sa’ad da zan komo da mutanena Isra’ila da Yahuda daga bauta in kuma maido da su ga ƙasar da na ba wa kakanninsu mallaka,’ in ji Ubangiji.”
4 And these [are] the words which he spoke Yahweh concerning Israel and concerning Judah.
Ga kalmomin Ubangiji da ya yi game da Isra’ila da Yahuda,
5 For thus he says Yahweh a sound of fear we have heard dread and there not [is] peace.
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Ana jin kukan tsoro, razana, ba salama ba.
6 Ask please and see if [is] giving birth a male why? have I seen every man hands his on loins his like [woman] giving birth and have they been changed? all faces into paleness.
Ku tambaya ku ji. Namiji zai iya haifi’ya’ya? To, me ya sa kuke ganin kowane mai ƙarfi da hannuwansa a kwankwaso kamar mace mai naƙuda, kowace fuska ta koma fari?
7 Woe! for [will be] great the day that from not [is] like it and [will be] a time of distress it for Jacob and from it he will be saved.
Kaito, gama wannan rana za tă zama mai girma! Babu kamar ta. Zai zama lokacin wahala wa Yaƙub, amma za a cece shi daga cikinta.
8 And it will be on the day that [the] utterance of - Yahweh of hosts I will break yoke his from on neck your and fetters your I will tear apart and not they will work by him again strangers.
“‘A wannan rana,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki, ‘Zan karya karkiya daga wuyansu zan kuma cire musu kangi; baƙi ba za su ƙara bautar da su ba.
9 And they will serve Yahweh God their and David king their whom I will raise up for them.
A maimakon haka, za su bauta wa Ubangiji Allahnsu Dawuda sarkinsu kuwa, wanda na tayar musu.
10 And you may not you fear O servant my Jacob [the] utterance of Yahweh and may not you be dismayed O Israel for here I [am] about to save you from a distant [land] and offspring your from [the] land of captivity their and he will return Jacob and he will be undisturbed and he will be at ease and there not [will be one who] terrifies.
“‘Saboda haka kada ka ji tsoro, ya Yaƙub bawana; kada ka karai, ya Isra’ila,’ in ji Ubangiji. ‘Tabbatacce zan cece ka daga wuri mai nesa, zuriyarka daga ƙasar zaman bautansu. Yaƙub zai sami salama da zaman lafiya, kuma ba wanda zai sa ya ji tsoro.
11 For [am] with you I [the] utterance of Yahweh to save you that I will make complete destruction on all the nations - where I have scattered you there nevertheless you not I will make complete destruction and I will discipline you to justice and certainly not I will leave unpunished you.
Ina tare da kai zan kuma cece ka,’ in ji Ubangiji. ‘Ko da yake na hallakar da dukan al’umma gaba ɗaya a inda na warwatsa ku, ba zan hallaka ku gaba ɗaya ba. Zan hore ku amma da adalci kaɗai; ba zan ƙyale ku ku tafi gaba ɗaya ba hukunci ba.’
12 For thus he says Yahweh [is] incurable fracture your [is] severe wound your.
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Mikinku marar warkewa ne, raunin da kuka ji ya sha ƙarfin warkarwa.
13 There not [is one who] pleads cause your to a sore [are] medications of healing there not for you.
Babu wanda zai yi roƙo saboda damuwarku, ba magani domin mikinku babu warkarwa dominku.
14 All lovers your they have forgotten you you not they care for for [the] blow of an enemy I have struck down you [the] correction of a cruel [one] on [the] greatness of iniquity your they are numerous sins your.
Dukan abokanku sun manta da ku; ba su ƙara kulawa da ku. Na buge ku kamar yadda abokin gāba zai yi na kuma hukunta ku yadda mai mugunta zai yi, domin laifinku da girma yake zunubanku kuma da yawa suke.
15 Why? do you cry out on fracture your [is] incurable pain your on - [the] greatness of iniquity your they are numerous sins your I have done these [things] to you.
Me ya sa kuke kuka a kan mikinku, wahalarku da ba ta da magani? Domin laifinku da girma yake da kuma zunubanku masu yawa na yi muku waɗannan abubuwa.
16 Therefore all [those who] devour you they will be devoured and all opponents your all of them in captivity they will go and they will become [those who] plunder you plunder and all [those who] despoil you I will make into spoil.
“‘Amma duk wanda ya cinye ku za a cinye shi; dukan abokan gābanku za su tafi zaman bauta. Waɗanda suka washe ku su ma za a washe su; dukan waɗanda suka mai da ku ganima su ma zan mai da su ganima.
17 For I will bring up healing for you and from wounds your I will heal you [the] utterance of Yahweh that an outcast people have called you [is] Zion it [is one who] cares there not for it.
Amma zan mayar muku da lafiya in kuma warkar da mikinku,’ in ji Ubangiji, ‘domin ana ce da ku yasassu, Sihiyona wadda ba wanda ya kula da ita.’
18 Thus - he says Yahweh here I [am] about to turn back [the] captivity of [the] tents of Jacob and dwellings its I will have compassion and it will be rebuilt a city on mound its and a fortress on proper place its it will remain.
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Zan mayar da wadatar tentin Yaƙub in kuma ji tausayin wuraren zamansa; za a sāke gina birnin a kufansa, fadar kuwa za tă tsaya a wurin da ya dace da ita.
19 And it will go out from them thanksgiving and [the] sound of merry makers and I will multiply them and not they will diminish and I will make honored them and not they will be insignificant.
Daga gare su waƙoƙi za su fito na godiya da kuma sowa ta farin ciki. Zan riɓaɓɓanya su, ba za su kuwa ragu ba; zan kawo musu ɗaukaka, ba kuwa za a ƙasƙanta su ba.
20 And they will be children its like long ago and congregation its before me it will be established and I will visit [judgment] on all [those who] oppress it.
’Ya’yansu za su kasance kamar a kwanakin dā jama’arsu kuma za su kahu a gabana; zan hukunta duk wanda ya zalunce su.
21 And he will be noble [one] its one of it and ruler its from [the] midst its he will come forth and I will bring near him and he will draw near to me for who? that this has he pledged heart his to draw near to me [the] utterance of Yahweh.
Shugabansu zai zama ɗaya daga cikinsu; mai mulkinsu zai taso daga cikinsu. Zan kawo shi kusa zai kuma zo kusa da ni, gama wane ne zai miƙa kansa don yă yi kusa da ni?’ In ji Ubangiji.
22 And you will become for me a people and I I will become for you God.
‘Saboda haka za ku zama mutanena, ni kuwa in zama Allahnku.’”
23 There! - [the] storm of Yahweh rage it has gone out a storm staying as a sojourner on [the] head of wicked [people] it will whirl about.
Ga shi, hadarin Ubangiji zai fasu cikin hasala, iskar guguwa mai hurawa a kan kawunan mugaye.
24 Not it will turn back [the] burning of [the] anger of Yahweh until has brought about he and until has carried out he [the] purposes of heart his at [the] end of the days you will understand it.
Fushi mai zafi na Ubangiji ba zai kawu ba sai ya cika manufofin zuciyarsa gaba ɗaya. A kwanaki masu zuwa za ku gane wannan.