< Jeremiah 27 >
1 In [the] beginning of [the] reign of Jehoiakim [the] son of Josiah [the] king of Judah it came the word this to Jeremiah from with Yahweh saying.
A farkon sarautar Zedekiya ɗan Yosiya sarkin Yahuda, wannan magana ta zo wa Irmiya daga Ubangiji.
2 Thus he said Yahweh to me make for yourself fetters and yoke-bars and you will put them on neck your.
Ga abin da Ubangiji ya ce mini, “Ka yi karkiyar itace da maɗaurai ka ɗaura a wuyanka.
3 And you will send them to [the] king of Edom and to [the] king of Moab and to [the] king of [the] people of Ammon and to [the] king of Tyre and to [the] king of Sidon by [the] hand of messengers who have come Jerusalem to Zedekiah [the] king of Judah.
Sa’an nan ka aika da saƙo zuwa wurin sarakunan Edom, Mowab, Ammon, Taya da Sidon ta bakin jakadu waɗanda suka zo Urushalima wurin Zedekiya sarkin Yahuda.
4 And you will command them to masters their saying thus he says Yahweh of hosts [the] God of Israel thus you will say to masters your.
Ka ba su saƙo wa iyayengijinsu su ce, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, “Ku faɗa wa iyayengijinku wannan.
5 I I made the earth humankind and the animal[s] which [are] on [the] surface of the earth by power my great and by arm my outstretched and I give it to [those] whom it is pleasing in view my.
Da ikon mai ƙarfi da kuma hannuna da na miƙa na yi duniya da mutanenta da kuma dabbobin da suke ciki, na ba da ita ga duk wanda na ga dama.
6 And now I I give all the lands these in [the] hand of Nebuchadnezzar [the] king of Babylon servant my and also [the] animal[s] of the field I give to him to serve him.
Yanzu zan ba da dukan ƙasashenku ga bawana Nebukadnezzar sarkin Babilon; zan sa namun jeji ma su bauta masa.
7 And they will serve him all the nations and son his and [the] son of son his until comes [the] time of land his also he and they will work by him nations many and kings great.
Dukan al’ummai za su bauta masa da ɗansa da kuma jikansa har sai har lokacin ƙasarsa ya kai; sa’an nan al’ummai masu yawa da kuma manyan sarakuna za su kasance a ƙarƙashinsa.
8 And it will be the nation and the kingdom which not they will serve him Nebuchadnezzar [the] king of Babylon and which not it will put neck its in [the] yoke of [the] king of Babylon with the sword and with famine and with pestilence I will visit [judgment] on the nation that [the] utterance of Yahweh until have consumed I them by hand his.
“‘“Amma fa, duk al’umma ko mulkin da bai bauta wa Nebukadnezzar sarkin Babilon ba bai kuwa rusunar da wuyarsa ga karkiyarsa ba, zan hukunta wannan al’umma da takobi, yunwa da annoba, in ji Ubangiji, har sai na hallaka ta ta wurin hannunsa.
9 And you may not you listen to prophets your and to diviners your and to dreams your and to soothsayers your and to sorcerers your who they [are] saying to you saying not you will serve [the] king of Babylon.
Saboda haka kada ku saurari annabawanku, masu dubanku, masu fassarar mafarkanku, bokayenku ko masu maitancinku waɗanda suke ce muku, ‘Ba za ku bauta wa sarkin Babilon ba.’
10 For falsehood they [are] prophesying to you so as to remove far away you from on land your and I will drive out you and you will perish.
Suna muku annabcin ƙaryar ne kawai da za tă kau da ku daga ƙasarku; zan kore ku za ku kuwa hallaka.
11 And the nation which it will bring neck its in [the] yoke of [the] king of Babylon and it will serve him and I will let remain it on land its [the] utterance of Yahweh and it will work it and it will dwell in it.
Amma duk al’ummar da ta rusuna da wuyarta a ƙarƙashin karkiyar sarkin Babilon ta kuma bauta masa, zan bar al’ummar ta zauna a ƙasarta ta noma ta, ta kuma zauna a can, in ji Ubangiji.”’”
12 And to Zedekiah [the] king of Judah I spoke according to all the words these saying bring necks your in [the] yoke of [the] king of Babylon and serve him and people his and live.
Na ba da wannan saƙo guda ga Zedekiya sarkin Yahuda. Na ce, “Ka rusunar da wuyanka a ƙarƙashin sarkin Babilon; ka bauta masa da kuma mutanensa, za ka kuwa rayu.
13 Why? will you die you and people your by the sword by famine and by pestilence just as he has spoken Yahweh to the nation which not it will serve [the] king of Babylon.
Me ya sa kai da mutanenka za ku mutu saboda takobi, yunwa da annoba waɗanda Ubangiji ya yi barazana wa duk al’ummar da ba za tă bauta wa sarkin Babilon ba?
14 And may not you listen to [the] words of the prophets who say to you saying not you will serve [the] king of Babylon for falsehood they [are] prophesying to you.
Kada ku saurari maganganun annabawa waɗanda suke ce muku, ‘Ba za ku bauta wa sarkin Babilon ba,’ gama annabcin ƙarya suke muku.
15 For not I sent them [the] utterance of Yahweh and they [are] prophesying in name my to falsehood so as to drive out I you and you will perish you and the prophets who are prophesying to you.
‘Ban aike su ba,’ in ji Ubangiji. ‘Suna annabcin ƙarya ne da sunana. Saboda haka, zan kore ku za ku kuwa hallaka, da ku da kuma annabawan da suke muku annabci.’”
16 And to the priests and to all the people this I spoke saying thus he says Yahweh may not you listen to [the] words of prophets your who are prophesying to you saying there! [the] articles of [the] house of Yahweh [are] about to be brought back from Babylon now quickly for falsehood they [are] prophesying to you.
Sai na ce wa firistoci da dukan waɗannan mutane, “Ga abin da Ubangiji yana cewa, kada ku saurari annabawan da suke cewa, ‘Ba daɗewa ba za a komo da kayan gidan Ubangiji daga Babilon.’ Suna muku annabcin ƙarya ne.
17 May not you listen to them serve [the] king of Babylon and live why? will it become the city this a ruin.
Kada ku saurare su. Ku bauta wa sarkin Babilon, za ku kuwa rayu. Don me wannan birni zai zama kufai?
18 And if [are] prophets they and if there [is] [the] word of Yahweh with them let them entreat please Yahweh of hosts to not go the articles - which remain in [the] house of Yahweh and [the] house of [the] king of Judah and in Jerusalem Babylon towards.
In su annabawa ne da gaske suna kuma da maganar Ubangiji, bari su roƙi Ubangiji Maɗaukaki ya sa kada a kwashe kayayyakin da suka ragu a gidan Ubangiji da kuma a cikin fadar sarkin Yahuda da kuma cikin Urushalima a kai Babilon.
19 For thus he says Yahweh of hosts concerning the pillars and on the sea and on the stands and on [the] remainder of the articles which remain in the city this.
Gama ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa game da ginshiƙai, kwatarniya, da dakalai, da sauran kayayyaki da aka bar su a birnin nan,
20 Which not he took them Nebuchadnezzar [the] king of Babylon when took into exile he (Jeconiah *Q(k)*) [the] son of Jehoiakim [the] king of Judah from Jerusalem Babylon towards and all [the] nobles of Judah and Jerusalem.
waɗanda Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kwashe sa’ad da ya kame Yekoniya ɗan Yehohiyakim sarkin Yahuda zuwa zaman bauta daga Urushalima zuwa Babilon tare da dukan manyan mutanen Yahuda da Urushalima,
21 For thus he says Yahweh of hosts [the] God of Israel on the articles which remain [the] house of Yahweh and [the] house of [the] king of Judah and Jerusalem.
I, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa game da abubuwan da aka bari a gidan Ubangiji da kuma a cikin fadar sarkin Yahuda da Urushalima,
22 Babylon towards they will be taken and there they will remain until [the] day give attention to I them [the] utterance of Yahweh and I will bring up them and I will bring back them to the place this.
‘Za a kwashe su zuwa Babilon a can kuwa za su kasance sai ranar da na neme su,’ in ji Ubangiji. ‘Sa’an nan zan komo da su in maido da su wannan wuri.’”