< Jeremiah 23 >
1 Woe to! [the] shepherds [who] are causing to stray and [who are] scattering [the] flock of pasture my [the] utterance of Yahweh.
“Kaiton makiyayan da suka hallakar suka kuma warwatsar da tumakin makiyayanta!” In ji Ubangiji.
2 Therefore thus he says Yahweh [the] God of Israel on the shepherds who are shepherding people my you you have scattered flock my and you have driven away them and not you have paid attention to them here I [am] about to visit on you [the] wickedness of deeds your [the] utterance of Yahweh.
Saboda haka ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana ce wa makiyayan da suke lura da mutanena, “Domin kun watsar da garkena kuka kuma kore su ba ku kuma lura da su ba, zan kawo hukunci a kanku saboda muguntar da kuka yi,” in ji Ubangiji.
3 And I I will gather together [the] remnant of flock my from all the lands where I have banished them there and I will bring back them to pasture their and they will be fruitful and they will increase.
“Ni kaina zan tattara raguwar garkena daga ƙasashen da na kore su zuwa zan kuma dawo da su ga makiyayansu, inda za su yi ta haihuwa su riɓaɓɓanya.
4 And I will raise up over them shepherds and they will shepherd them and not they will be afraid again and not they will be terrified and not they will be missing [the] utterance of Yahweh.
Zan sa makiyaya a kansu waɗanda za su lura da su, ba za su ƙara jin tsoro ko razana ba, ba kuwa waninsu da zai ɓace,” in ji Ubangiji.
5 Here! days [are] coming [the] utterance of Yahweh and I will raise up for David a branch righteous and he will reign a king and he will act prudently and he will do justice and righteousness in the land.
“Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan tā da wa Dawuda Reshen adalci, Sarki wanda zai yi mulki da hikima ya kuma yi abin da yake gaskiya da kuma daidai a ƙasar.
6 In days his it will be saved Judah and Israel it will dwell to security and this [will be] name his which anyone will call him Yahweh - [is] righteousness our.
A cikin zamaninsa za a ceci Yahuda Isra’ila kuma zai zauna lafiya. Sunan da za a kira shi ke nan, Ubangiji Adalcinmu.
7 Therefore here! days [are] coming [the] utterance of Yahweh and not people will say again [by] [the] life of Yahweh who he brought up [the] people of Israel from [the] land of Egypt.
“Saboda haka fa, kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da mutanen ba za su ƙara cewa, ‘Muddin Ubangiji yana raye, wanda ya fito da Isra’ila daga Masar ba,’
8 That except [by] [the] life of Yahweh who he brought up and who he brought [the] offspring of [the] house of Israel from a land north-ward and from all the lands where I banished them there and they will dwell on own land their.
amma za su ce, ‘Muddin Ubangiji yana raye, wanda ya fito da zuriyar Isra’ila daga ƙasar arewa da kuma daga dukan ƙasashen da ya yashe su.’ Sa’an nan za su zauna a ƙasarsu.”
9 Of the prophets it is broken heart my in inner being my they have become weak all bones my I have become like a person drunken and like a man [whom] it has passed over him wine because of Yahweh and because of [the] words of holiness his.
Game da annabawa kuwa, Zuciyata ta karai; dukan ƙasusuwana suna kaɗuwa. Na zama kamar wanda ya bugu, kamar mutumin da ruwan inabi ya sha kansa, saboda Ubangiji da kuma maganarsa mai tsarki.
10 For adulterers it is full the land for because of a curse it has dried up the land they have become dry [the] pastures of [the] wilderness and it has become course [of life] their evil and strength their [is] not right.
Ƙasar ta cika da mazinata; saboda la’ana ƙasar ta zama kango makiyaya a hamada ta bushe. Annabawa suna bin mugayen muradu suna kuma amfani da ƙarfinsu a hanyar marar kyau.
11 For both prophet as well as priest they are polluted also in house my I have found wickedness their [the] utterance of Yahweh.
“Annabi da firist dukansu biyu marasa sanin Allah ne; har ma a cikin haikalina na tarar da muguntarsu,” in ji Ubangiji.
12 Therefore it will become path their for them like slippery places in the darkness they will be pushed down and they will fall on it for I will bring on them calamity [the] year of punishment their [the] utterance of Yahweh.
“Saboda haka hanyarsu za tă yi santsi; za a jefar da su cikin duhu a can kuwa za su fāɗi. Zan kawo musu masifa a shekarar da za a hukunta su,” in ji Ubangiji.
13 And among [the] prophets of Samaria I saw offensiveness they prophesied by Baal and they caused to err people my Israel.
“A cikin annabawan Samariya na ga wannan abin banƙyama. Suna annabci ta wurin Ba’al suna ɓad da mutanena Isra’ila.
14 And among [the] prophets of Jerusalem I have seen a horrible [thing] they have committed adultery and they have walked in falsehood and they have strengthened [the] hands of evil-doers to not they have turned away anyone from evil his they have become to me all of them like Sodom and inhabitants its like Gomorrah.
A cikin annabawan Urushalima kuma na ga wani abin bantsoro. Suna zina suna kuma rayuwar ƙarya. Sun ƙarfafa hannuwa masu aikata mugunta, domin kada wani ya juya daga muguntarsa. Dukansu sun yi kama da Sodom a gare ni; mutanen Urushalima sun yi kama da Gomorra.”
15 Therefore thus he says Yahweh of hosts on the prophets here I [am] about to make eat them wormwood and I will make drink them water of poison for from with [the] prophets of Jerusalem it has gone out wicked behavior to all the land.
Saboda haka, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa game da annabawa, “Zan sa su ci abinci mai ɗaci su kuma sha ruwa mai dafi, domin daga annabawan Urushalima rashin sani Allah ya bazu ko’ina a ƙasar.”
16 Thus he says Yahweh of hosts may not you listen to [the] words of the prophets who are prophesying to you [are] deluding they you [the] vision of own heart their they speak not from [the] mouth of Yahweh.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Kada ku saurari abin da annabawan suke muku annabci; suna cika ku da sa zuciyar ƙarya. Suna maganar wahayi daga tunaninsu, ba daga bakin Ubangiji ba.
17 [they are] saying Continually to [those who] despise me he says Yahweh peace it will belong to you and every [one who] walks in [the] stubbornness of own heart his they have said not it will come on you calamity.
Suna cin gaba da ce wa waɗanda suka rena ni, ‘Ubangiji ya ce za ku zauna lafiya.’ Ga duka waɗanda suke bin taurin zukatansu kuwa sukan ce, ‘Babu lahanin da zai same ku.’
18 For who? has he stood in [the] council of Yahweh so he may see and he may hear word his who? has he paid attention to (word his *Q(K)*) and has he listened?
Amma wane ne a cikinsu ya taɓa tsaya a majalisar Ubangiji yă ga ko ya ji maganarsa? Wa ya saurari ya kuma ji maganarsa?
19 There! - [the] storm of Yahweh rage it has gone out and a storm whirling on [the] head of wicked [people] it will whirl about.
Ga shi, hadarin Ubangiji zai taso cikin hasala guguwa tana kaɗawa a kan kawunan mugaye.
20 Not it will turn back [the] anger of Yahweh until has brought about he and until has carried out he [the] purposes of heart his at [the] end of the days you will understand it understanding.
Fushin Ubangiji ba zai kau ba sai ya aikata nufin zuciyarsa. A kwanakin masu zuwa za ku gane sarai.
21 Not I sent the prophets and they they ran not I spoke to them and they they prophesied.
Ban aiki waɗannan annabawa ba, duk da haka sun tafi da saƙonsu; ban yi musu magana ba, duk da haka sun yi annabci.
22 And if they had stood in council my so they may cause to hear words my people my and they will turn back them from way their wicked and from [the] wickedness of deeds their.
Amma da a ce sun tsaya a majalisata, da sun yi shelar maganata ga mutanena sun kuma juyar da su daga mugayen hanyoyinsu da kuma daga mugayen ayyukansu.
23 ¿ A God from near [am] I [the] utterance of Yahweh and not a God from a distance.
“Ni ɗin Allah na kusa ne kawai,” in ji Ubangiji, “ba Allah na nesa ba?
24 Or? will he hide himself anyone in hiding places and I not I will see him [the] utterance of Yahweh ¿ not the heavens and the earth [am] I filling [the] utterance of Yahweh.
Akwai wanda zai iya ɓuya a lungu har da ba zan iya ganinsa ba?” In ji Ubangiji “Ban cika sama da ƙasa ba?” In ji Ubangiji.
25 I have heard [that] which they have said the prophets who prophesy in name my falsehood saying I have dreamed I have dreamed.
“Na ji abin da annabawa suna cewa su da suke annabcin ƙarya a sunana. Suna cewa, ‘Na yi mafarki! Na yi mafarki!’
26 Until when? ¿ [is] there in [the] heart of the prophets [who] prophesy falsehood and [the] prophets of [the] deceitfulness of own heart their.
Har yaushe wannan zai ci gaba a cikin zukata annabawa masu ƙarya, waɗanda suke annabcin ruɗun tunaninsu?
27 Who plan to make forget people my name my by dreams their which they recount each to neighbor his just as they forgot ancestors their name my for Baal.
Suna tsammanin mafarkan da suke faɗa wa juna za su sa mutane su manta da sunana, kamar yadda kakanninsu suka manta da sunana ta wurin yin wa Ba’al sujada.
28 The prophet whom [is] with him a dream let him recount [the] dream and whom word my [is] with him let him speak word my faithfulness what? [belongs] to the straw with the grain [the] utterance of Yahweh.
Bari annabin da ya yi mafarki ya faɗa mafarkinsa, amma bari wanda yake da maganata ya yi ta da aminci. Gama me ya haɗa ciyawa da alkama?” In ji Ubangiji.
29 ¿ Not thus [is] word my like fire [the] utterance of Yahweh and like a hammer [which] it shatters rock.
“Maganata ba wuta ba ce,” in ji Ubangiji, “kuma kamar gudumar da kan ragargaza dutse?
30 Therefore here I [am] on the prophets [the] utterance of Yahweh [who] steal words my each from with neighbor his.
“Saboda haka,” in ji Ubangiji, “Ina gāba da annabawan da suke satar maganganuna daga juna.
31 Here I [am] on the prophets [the] utterance of Yahweh who take tongue their and they have uttered an utterance.
I,” in ji Ubangiji, “Ina gāba da annabawan da suke kaɗa harsunansu sa’an nan su ce, ‘Ubangiji ne ya furta.’
32 Here I [am] on [those who] prophesy dreams of falsehood [the] utterance of Yahweh and they have recounted them and they caused to err people my by falsehoods their and by recklessness their and I not I sent them and not I appointed them and certainly not they benefit the people this [the] utterance of Yahweh.
Tabbatacce, ina gāba da waɗannan da suke annabci mafarkan karya,” in ji Ubangiji. “Suna faɗarsu suna ɓad da mutanena da ƙarairayinsu na rashin hankali, duk da haka ban aike su ba, ban kuwa umarce su ba. Ba su amfani wannan mutane ba ko kaɗan,” in ji Ubangiji.
33 And if it will ask you the people this or the prophet or a priest saying what? [is] [the] burden of Yahweh and you will say to them what? burden and I will abandon you [the] utterance of Yahweh.
“Sa’ad da waɗannan mutane, ko annabi ko firist, ya tambaye ka, ‘Mece ce maganarUbangiji?’ Ka ce musu, ‘Wace magana? Zan yashe ku, in ji Ubangiji.’
34 And the prophet and the priest and the people who he will say [the] burden of Yahweh and I will visit [judgment] on the person that and on house his.
In annabi ko firist ko da wani dabam ya ce, ‘Wannan ne abin da Ubangiji yake cewa,’ zan hukunta wannan mutum da kuma gidansa.
35 Thus you will say each to neighbor his and each to brother his what? did he answer Yahweh and what? did he say Yahweh.
Ga abin da kowannenku yana cin gaba da ce wa abokinsa ko danginsa, ‘Mece ce amsar Ubangiji?’ Ko kuwa ‘mene ne Ubangiji ya faɗa?’
36 And [the] burden of Yahweh not you will remember again for the burden it is for a person own word his and you change [the] words of God living Yahweh of hosts God our.
Amma kada ku ƙara ambatar ‘maganar Ubangiji’ domin kowace maganar mutum kan zama maganarsa. Ta haka kukan lalace maganar Allah mai rai, Ubangiji Maɗaukaki, Allahnmu.
37 Thus you will say to the prophet what? did he answer you Yahweh and what? did he say Yahweh.
Ga abin da za ku ci gaba da faɗa wa annabi, ‘Mece ce amsar Ubangiji gare ka?’ Ko kuwa ‘mene ne Ubangiji ya faɗa?’
38 And if [the] burden of Yahweh you will say therefore thus he says Yahweh because have spoken you the word this [the] burden of Yahweh and I sent to you saying not you must say [the] burden of Yahweh.
Ko da yake kuna cewa, ‘Wannan ce maganar Ubangiji,’ ga abin da Ubangiji yana cewa kuna amfani da kalmomi, ‘Wannan ce maganar Ubangiji,’ ko da yake na ce muku kada ku ce, ‘Wannan ce maganar Ubangiji.’
39 Therefore here [am] I and I will surely you lift up and I will abandon you and the city which I gave to you and to ancestors your from on face my.
Saboda haka, tabbatacce zan manta da ku in kuma jefar da ku daga gabana tare da birnin da na ba ku da kuma kakanninku.
40 And I will put on you a reproach of perpetuity and shame of perpetuity which not it will be forgotten.
Zan kawo muku madawwamiyar kunya, kunya ta har abada wadda ba za a taɓa manta ba.”