< Isaiah 62 >
1 For [the] sake of Zion not I will be silent and for [the] sake of Jerusalem not I will remain quiet until it will go forth like brightness righteousness its and salvation its like a torch [which] it burns.
Saboda Sihiyona ba zan yi shiru ba, saboda Urushalima ba zan huta ba, sai adalcinta ya haskaka kamar hasken safiya, cetonta kuma ya haskaka kamar fitila mai haske.
2 And they will see nations righteousness your and all kings glory your and it will be called to you a name new which [the] mouth of Yahweh it will designate it.
Al’ummai za su ga adalcinki, sarakuna kuma za su ga ɗaukakarki; za a kira ki da sabon suna sunan da bakin Ubangiji zai ambata.
3 And you will be a crown of beauty in [the] hand of Yahweh (and a headdress of *Q(K)*) royalty in [the] palm of God your.
Za ki zama rawanin daraja a hannun Ubangiji, rawanin sarauta a hannun Allahnki.
4 Not it will be said of you again abandoned and of land your not it will be said again desolation that to you it will be called Hephzi-bah and to land your married for he delights Yahweh in you and land your it will be married.
Ba za a ƙara ce da ke Yasasshiya ba, ko a kira ƙasarki Kango. Amma za a ce da ke Hefziba ƙasarki kuma Bewula; gama Ubangiji zai ji daɗinki, ƙasarki kuma za tă yi aure.
5 For he marries a young man a young woman they will marry you sons your and [the] joy of a bridegroom on a bride he will rejoice on you God your.
Kamar yadda saurayi kan auri yarinya, haka’ya’yanki maza za su aure ki; kamar kuma yadda ango yakan yi farin ciki da amaryarsa, haka Allahnki zai yi farin ciki da ke.
6 On walls your O Jerusalem I have appointed watchmen all the day and all the night continually not they will be silent O those [who] cause to remember Yahweh [let] not rest [belong] to you.
Na sa matsara a kan katangarki, ya Urushalima; ba za su taɓa yin shiru ba, dare da rana. Ku da kuke kira bisa sunan Ubangiji, kada ku ba kanku hutu,
7 And may not you give rest to him until he will establish and until he will make Jerusalem praise on the earth.
kuma kada ku ba shi hutu sai ya kafa Urushalima ya kuma mai da ita yabon duniya.
8 He swears an oath Yahweh by right [hand] his and by [the] arm of strength his if I will give grain your again food to enemies your and if they will drink sons of foreignness new wine your which you have labored for it.
Ubangiji ya rantse da hannunsa na dama ta hannunsa kuma mai iko cewa, “Ba zan ƙara ba da hatsinki ya zama abinci ga abokan gābanki ba, baƙi kuma ba za su ƙara shan ruwan inabin wanda kika sha wahala samu ba;
9 For [those who] gather it they will eat it and they will praise Yahweh and [those who] gather it they will drink it in [the] courts of holiness my.
amma waɗanda suka girbe shi za su ci shi su kuma yabi Ubangiji, waɗanda kuma suka tattara’ya’yan inabi za su sha shi a filayen wurina mai tsarki.”
10 Pass pass in the gates make clear [the] way of the people build up build up the highway clear [it] from stone[s] raise a standard over the peoples.
Ku wuce, ku wuce ƙofofi! Ku shirya hanya saboda mutane. Ku gina, ku gina babbar hanya! Ku kawar da duwatsu. Ku ɗaga tuta saboda al’ummai.
11 There! Yahweh he has proclaimed to [the] end of the earth say to [the] daughter of Zion there! salvation your [is] about to come there! reward his [is] with him and recompense his [is] before him.
Ubangiji ya yi shela ga iyakokin duniya cewa, “Faɗa wa Diyar Sihiyona, ‘Ga Mai Cetonki yana zuwa! Ga ladarsa tana tare da shi, sakamakonsa yana raka shi.’”
12 And people will call them [the] people of holiness [the] redeemed of Yahweh and to you it will be called [one] sought out a city [which] not it has been forsaken.
Za a ce da shi Tsattsarkar Mutane, Fansassu na Ubangiji; za a kuma ce da ke Wadda Aka Nema Birnin da Ba Za a Ƙara Yashe ta ba.