< Isaiah 6 >
1 In [the] year of [the] death of the king Uzziah and I saw [the] Lord sitting on a throne high and lifted up and [the] skirts of robe his [were] filling the temple.
A shekarar da Sarki Uzziya ya mutu, na ga Ubangiji zaune a kan kujerar sarauta a sama cike da ɗaukaka, zatinsa ya cika haikali.
2 Seraphim [were] standing - from above him six wings six wings [belonged] to one with two [wings] - he covered face his and with two [wings] he covered feet his and with two [wings] he flew.
A bisansa akwai serafofi, kowanne yana da fikafikai shida. Fikafikai biyu sun rufe fuskokinsu, da biyu suka rufe ƙafafunsu, biyu kuma da su suke tashi.
3 And he called this to this and he said [is] holy - holy holy Yahweh of hosts [the] fullness of all the earth [is] glory his.
Suna kiran juna, “Mai Tsarki, Mai Tsarki, Mai Tsarki! Ubangiji Maɗaukaki ne; duniya ta cika da ɗaukakarsa.”
4 And they shook [the] foundations of the thresholds from [the] voice of the [one who] called and the house it was filled smoke.
Da jin ƙarar muryoyinsu madogarai da madogaran ƙofa suka girgiza, haikali kuma ya cika da hayaƙi.
5 And I said woe! to me for I am destroyed for [am] a man unclean of lips I and in among a people unclean of lips I [am] dwelling for the king Yahweh of hosts they have seen eyes my.
Sai na tā da murya na ce, “Kaitona! Na shiga uku! Gama ni mutum ne mai leɓuna marar tsarki, kuma ina raye a cikin mutane masu leɓuna marasa tsarki, idanuna kuma sun ga Sarki, Ubangiji Maɗaukaki.”
6 And he flew to me one of the seraphim and [was] in hand his a live coal [which] with tongs he had taken from on the altar.
Sai ɗaya daga cikin serafofin ya yi firiya zuwa wurina tare da garwashi mai wuta a hannunsa, wanda ya ɗiba da arautaki daga bagade.
7 And he made [it] touch mouth my and he said here! it has touched this lips your and it will be removed iniquity your and sin your it will be atoned for.
Da shi ne ya taɓa bakina ya ce, “Duba, wannan ya taɓa leɓunanka, yanzu fa an kawar da laifofinka, an kuma gafarta maka zunubanka.”
8 And I heard [the] voice of [the] Lord saying whom? will I send and who? will he go for us and I said here [am] I send me.
Sa’an nan na ji muryar Ubangiji tana cewa, “Wa zan aika? Wa zai tafi mana?” Sai na ce, “Ga ni! Ka aike ni!”
9 And he said go and you will say to the people this hear continually and may not you understand and see continually and may not you perceive.
Ya ce, “Je ka ka faɗa wa wannan mutane, “‘Kome yawan kasa kunne da za ku yi, ba za ku fahimta ba; Kome yawan dubar da za ku yi, ba za ku san abin da yake faruwa ba.’
10 Make fat [the] heart of the people this and ears its make heavy and eyes its seal over lest it should see with eyes its and with ears its it will hear and heart its it will understand and it will return and someone will heal it.
Ka sa zuciyar mutanen nan ta dushe; kunnuwansu su kurunce, idanunsu kuma su makance. In ba haka ba za su iya gani da idanunsu, su ji da kunnuwansu, su fahimta da zuciyarsu, su kuma juyo a kuma warkar da su.”
11 And I said until when? O Lord and he said until that they have lain desolate cities from not inhabitant and houses from not anyone and the ground it will be devastated a desolation.
Sa’an nan na ce, “Har yaushe, ya Ubangiji?” Ya kuma amsa, “Sai an lalatar da biranen ba kowa a ciki, sai an mai da gidaje kangwaye ƙasa kuma ta zama kango ba amfani,
12 And he will send far away Yahweh humankind and it will become great the abandoned [land] in [the] midst of the land.
sai lokacin da Ubangiji ya kori kowa aka kuma yashe ƙasar gaba ɗaya.
13 And still [will be] in it a tenth [part] and it will return and it will become burning like terebinth and like oak which in [the] felling a stump [is] in them [will be] offspring of holiness stump its.
Ko da yake kashi ɗaya bisa goma zai ragu a ƙasar, za tă sāke zama kango. Amma kamar yadda katambiri da itacen oak sukan bar kututturai sa’ad da aka yanke su, haka iri mai tsarkin nan zai zama kututture a ƙasar mai tsarki.”