< Isaiah 59 >
1 Here! not it is [too] short [the] hand of Yahweh for saving and not it is [too] heavy ear his for hearing.
Tabbatacce hannun Ubangiji bai kāsa yin ceto ba, kunnensa kuma bai kurmance da zai kāsa ji ba.
2 For except iniquities your they have been separating between you and between God your and sins your they have hidden face from you from hearing.
Amma laifofinku sun raba ku da Allahnku; zunubanku sun ɓoye fuskarsa daga gare ku, saboda kada yă ji.
3 For hands your they are defiled with blood and fingers your with iniquity lips your they have spoken falsehood tongue your injustice it mutters.
Gama hannuwanku sun ƙazantu da jini, yatsotsinku kuma da alhaki. Leɓunanku suna faɗin ƙarairayi, harshenku kuma yana raɗar mugayen abubuwa.
4 There not [is one who] calls in righteousness and there not [is one who] enters into judgment in truth [they are] trusting on emptiness and they speak worthlessness they conceive mischief and they bring forth wickedness.
Babu wani mai ce a yi adalci; babu wani mai nema a dubi al’amarinsa da mutunci. Sun dogara a gardandamin banza suna ƙarairayi; suna ɗaukar cikin ɓarna, su haifi mugunta.
5 Eggs of a viper they have hatched and webs of a spider they weave the [one who] eats any of eggs their he will die and the pressed [egg] it is hatched a snake.
Suna ƙyanƙyashe ƙwan kāsā su kuma saƙa yanar gizo-gizo. Duk wanda ya ci ƙwansu zai mutu, kuma sa’ad da ƙwan ya fashe, zai ƙyanƙyashe kububuwa.
6 Webs their not they will become clothing and not people will cover themselves with products their products their [are] products of wickedness and deed[s] of violence [is] in hands their.
Yanar gizo-gizonsu ba amfani don tufa; ba za su iya rufuwa da abin da suka yi ba. Ayyukansu mugaye ne, ayyukan tā da hargitsi kuma suna a hannuwansu.
7 Feet their to evil they run and they may hasten to shed blood innocent thoughts their [are] thoughts of wickedness devastation and destruction [are] on highways their.
Ƙafafunsu sukan gaggauta zuwa aikata zunubi; suna da saurin zub da jini. Tunaninsu mugaye ne; lalaci da hallaka sun shata hanyoyinsu.
8 A way of peace not they know and there not [is] justice on tracks their paths their they have made crooked themselves any [one who] treads on it not he knows peace.
Ba su san hanyar salama ba; babu adalci a hanyoyinsu. Sun mai da su karkatattun hanyoyi; babu wanda zai yi tafiya a kansu ya sami salama.
9 There-fore it is far justice from us and not it reaches us righteousness we wait eagerly for the light and there! darkness for gleams of light in gloom we walk.
Saboda haka gaskiya ta yi nisa da mu, adalci kuma ba ya kaiwa gare mu. Muna neman haske, sai ga duhu; muna neman haske, sai muka yi ta tafiya cikin baƙin inuwa.
10 We grope for like blind [people] a wall and like there not [are] eyes we grope we have stumbled at noon like the twilight among the fat people like dead [people].
Kamar makafi, sai lallubar bango muke yi, muna lallubawar hanyarmu kamar marasa idanu. Da tsakar rana muna tuntuɓe sai ka ce wuri ya fara duhu; cikin ƙarfafa, mun zama kamar matattu.
11 We growl like bears all of us and like doves certainly we moan we wait eagerly for justice and there not for deliverance it is far from us.
Muna gurnani kamar beyar; muna ta ƙugi kamar kurciyoyi. Muna ta neman adalci amma ina; mun nemi fansa, amma yana can da nisa.
12 For they are many transgressions our before you and sins our it has testified against us that transgressions our [are] with us and iniquities our we know them.
Gama laifofinmu suna da yawa a gabanka, zunubanmu kuma suna ba da shaida gāba da mu. Laifofinmu kullum suna a gabanmu, muna kuma sane da laifofinmu,
13 We have transgressed and we have denied Yahweh and we have turned back from after God our we have spoken oppression and rebellion we have conceived and we have uttered from [the] heart words of falsehood.
tawaye da mūsun Ubangiji, mun juye bayanmu ga Allahnmu, zugawa a yi zalunci da tayarwa, faɗin ƙarairayi da zukatanmu suka shirya.
14 And it has been driven back backwards justice and righteousness from a distance it stands for it has stumbled in the open place truth and honesty not it is able to enter.
Saboda haka aka kau da yin gaskiya adalci kuma ya tsaya can da nesa; gaskiya ta yi tuntuɓe a tituna, sahihanci ba zai shiga ba.
15 And it was truth lacking and [one who] turned aside from evil [was] plundered and he saw Yahweh and it was displeasing in view his that there not [was] justice.
Gaskiya ta ɓace gaba ɗaya, kuma duk wanda ya guji mugunta zai zama ganima. Ubangiji ya duba bai kuwa ji daɗi cewa babu adalci ba.
16 And he saw that there not [was] anyone and he was appalled that there not [was one who] interposed and it gave victory to him own arm his and own righteousness his it it sustained him.
Ya ga cewa babu wani, ya yi mamaki cewa babu wanda zai shiga tsakani; saboda haka hannunsa ya aikata masa ceto, adalcinsa kuma ya raya shi.
17 And he put on righteousness like body armor and a helmet of salvation on head his and he put on garments of vengeance clothing and he wrapped himself like robe zeal.
Ya yafa sulke a matsayin rigar ƙirji, da hulan kwanon ceto a kansa; ya sa rigunan ɗaukar fansa ya kuma nannaɗe kansa da kishi kamar a cikin alkyabba.
18 As on deeds as on he will repay rage to opponents his recompense to enemies his to the islands recompense he will repay.
Bisa ga abin da suka yi, haka za a sāka fushi a kan abokan gābansa ramuwa kuma a kan maƙiyansa; zai sāka wa tsibirai abin da ya dace da su.
19 And they may fear from [the] setting place [the] name of Yahweh and from [the] rising of [the] sun glory his for he will come like river narrow [which] [the] wind of Yahweh it will drive it.
Daga yamma, mutane za su ji tsoron Ubangiji, daga mafitar rana kuma, za su girmama ɗaukakarsa. Gama zai zo kamar rigyawa mai tsananin gudu cewa numfashin Ubangiji zai tafi tare da shi.
20 And he will come to Zion a redeemer and to [those who] repent of transgression in Jacob [the] utterance of Yahweh.
“Mai fansa zai zo Sihiyona, zuwa waɗanda suke cikin Yaƙub da suka tuba daga zunubansu,” in ji Ubangiji.
21 And I this [is] covenant my with them he says Yahweh spirit my which [is] on you and words my which I have put in mouth your not they will depart from mouth your and from [the] mouth of offspring your and from [the] mouth of [the] offspring of offspring your he says Yahweh from now and until perpetuity.
“Game da ni dai, ga alkawarina da su,” in ji Ubangiji. “Ruhuna, wanda yake a kanka, da kuma maganata da na sa a bakinka ba za tă rabu da bakinka ba, ko daga bakunan’ya’yanka ba, ko kuwa daga bakunan zuriyarsu ba daga wannan lokaci zuwa gaba da kuma har abada,” in ji Ubangiji.