< Isaiah 58 >

1 Call out with a throat may not you refrain like trumpet raise voice your and declare to people my transgression their and to [the] house of Jacob sins their.
“Ku yi ihu da ƙarfi, ba ƙaƙƙautawa. Ku tā da muryarku kamar busar ƙaho. Ku furta wa mutanena tawayensu da kuma ga gidan Yaƙub zunubansu.
2 And me day day they seek! and [the] knowledge of ways my they desire! like a nation which righteousness it has done and [the] judgment of God its not it has forsaken they ask me judgments of righteousness [the] approach of God they desire!
Gama kowace rana suna nemana; suna marmarin sanin hanyoyina, sai ka ce al’ummar da take yin abin da yake daidai ba ta kuma yashe umarnan Allahnta ba. Sun nemi shawarwaran da suke daidai daga gare ni suna kuma marmari Allah ya zo kusa da su.
3 Why? have we fasted and not you have seen have we humbled? self our and not you know there! on [the] day of fasting your you find pleasure and all laborers your you drive hard.
Suna cewa, ‘Don me muka yi azumi, ba ka kuma gani ba? Me ya sa muka ƙasƙantar da kanmu, ba ka kuma lura da wannan ba?’ “Duk da haka a ranar azuminku, kuna yi yadda kuka ga dama kuna kuma zaluntar dukan ma’aikata.
4 There! for strife and contention you fast and to strike with a fist of wickedness not you fast like this day to make heard in the height[s] voice your.
Azuminku yakan ƙare a faɗa da kuma hargitsi, kuna ta naushin juna da mugayen naushe-naushe. Ba za ku iya azumi kamar yadda kuke yi a yau ku zaci za a ji muryarku can sama.
5 ¿ Like this is it [the] fast [which] I choose it a day to humble anyone self his ¿ to bend down like a bulrush head his and sackcloth and ash[es] he spreads as a bed ¿ this do you call a fast and a day of acceptance to Yahweh.
Irin azumin da na zaɓa ke nan, rana guda kawai don mutum ya ƙasƙantar da kansa? Sunkuyar da kanku kamar iwa kawai kuna kuma kwance a tsummoki da toka? Abin da kuke kira azumi ke nan rana yardajje ga Ubangiji?
6 ¿ Not [is] this [the] fast [which] I choose it to loosen [the] bonds of wickedness to unfasten [the] bindings of [the] yoke-bar and to let go crushed [people] free [people] and every yoke-bar you will tear apart.
“Irin azumin da na zaɓa shi ne, a kunce sarƙoƙin rashin adalci a kuma kunce igiyoyin karkiya, a’yantar da waɗanda ake zalunta a kuma kakkarye kowace karkiya?
7 ¿ Not [is it] to break for the hungry [person] bread your and poor [people] homeless people you will bring a house if you will see [the] naked and you will cover him and from own flesh your not you will hide yourself.
Ba shi ne ku rarraba abincinku da mayunwata ku kuma tanada wa matalauta masu yawo mahalli, sa’ad da kuka ga wanda yake tsirara, ku yi masa sutura, kada kuma ku ba wa namanku da jininku baya?
8 Then it will break forth like the dawn light your and healing your quickly it will spring up and it will go before you righteousness your [the] glory of Yahweh it will be rearguard your.
Sa’an nan haskenku zai keto kamar ketowar alfijir, warkarwarku kuma zai bayyana nan da nan; sa’an nan adalcinku zai tafi a gabanku, ɗaukakar Ubangiji kuma zai tsare ku daga baya.
9 Then you will call and Yahweh he will answer you will cry for help and he may say here [am] I if you will remove from among you [the] yoke-bar [the] stretching out of a finger and [the] speaking of wickedness.
Sa’an nan za ku yi kira, Ubangiji kuma zai amsa; za ku yi kuka don neman taimako, zai kuwa ce ga ni nan. “In kuka kawar da karkiyar zalunci, kuka daina nuna wa juna yatsa da kuma faɗar mugayen maganganu,
10 And you will offer to the hungry [person] self your and [the] appetite of [the] afflicted you will satisfy and it will rise in the darkness light your and gloom your [will be] like the noon.
in kuma kuka ɗauki lokaci kuka ƙosar da mayunwata kuka kuma biya bukatun waɗanda suke shan tsanani, sa’an nan ne haskenku zai haskaka cikin duhu darenku kuma zai zama kamar tsakar rana.
11 And he will lead you Yahweh continually and he will satisfy in arid regions appetite your and bones your he will strengthen and you will be like a garden watered and like a spring of waters which not they will fail waters its.
Ubangiji zai bishe ku kullum; zai biya muku bukatunku a ƙasa mai zafin rana ya kuma ƙarfafa ƙasusuwanku. Za ku zama kamar lambun da aka yi masa banruwa, kamar rafin da ruwansa ba ya ƙafewa.
12 And they will rebuild some of you [the] ruins of antiquity [the] foundations of a generation and a generation you will raise up and it will be called to you [one who] walls up a breach [one who] restores paths to dwell in.
Mutanenku za su sāke gina kufai na da su kuma daga tsofaffin harsashai; za a ce da ku Masu Gyaran Katangar da ta Rushe, Masu Farfaɗo da Tituna da kuma Wuraren zama.
13 If you will turn back from [the] sabbath foot your to do pleasures your on [the] day of holiness my and you will call the sabbath a delight [the] holy [day] of Yahweh honorable and you will honor it from doing own ways your from finding pleasure your and to speak a word.
“In kun kiyaye ƙafafunku daga take Asabbaci da kuma daga aikata abin da kuka gan dama a ranata mai tsarki, in kuka kira Asabbaci ranar murna rana mai tsarki ta Ubangiji kuma mai bangirma, in kuka girmama ta ta wurin ƙin yin abin da kuka gan dama da kuma yin al’amuranku ko yin mugayen maganganu,
14 Then you will take delight on Yahweh and I will make ride you on ([the] high places of *Q(k)*) [the] land and I will feed you [the] inheritance of Jacob ancestor your for [the] mouth of Yahweh it has spoken.
sa’an nan za ku yi farin ciki a cikin Ubangiji, zan kuma sa ku a kan maɗaukaka ƙasashe ku kuma yi biki a gādon mahaifinku Yaƙub.” Ni Ubangiji ne na faɗa.

< Isaiah 58 >