< Isaiah 49 >

1 Listen O islands to me and pay attention O peoples from a distance Yahweh from [the] womb he called me from [the] inward parts of mother my he has brought to remembrance name my.
Ku kasa kunne gare ni, ku tsibirai; ku ji wannan, ku al’ummai masu nesa. Kafin a haife Ni Ubangiji ya kira ni; tun daga haihuwata ya ambaci sunana.
2 And he made mouth my like a sword sharp in [the] shadow of hand his he hid me and he made me an arrow polished in quiver his he concealed me.
Ya yi bakina kamar takobi mai kaifi, cikin inuwar hannunsa ya ɓoye ni; ya sa na zama kamar kibiya mai tsini ya kuma ɓoye ni cikin kwarinsa.
3 And he said to me [are] servant my you Israel whom by you I will get glory for myself.
Ya ce mini, “Kai bawana ne, Isra’ila, a cikinka zan bayyana darajata.”
4 And I I said to emptiness I have labored to nothingness and futility strength my I have caused to fail nevertheless justice my [is] with Yahweh and recompense my [is] with God my.
Amma na ce, “Na yi aiki a banza; na kashe duk ƙarfina a banza da wofi. Duk da haka abin da yake nawa yana a hannun Ubangiji, ladana kuma tana a wurin Allahna.”
5 And now - he says Yahweh [who] formed me from [the] womb a servant of him to bring back Jacob to him and Israel (to him *Q(K)*) it will be gathered and I may be honored in [the] eyes of Yahweh and God my he has been strength my.
Yanzu fa Ubangiji ya ce ya siffanta ni a cikin mahaifa don in zama bawansa don in dawo da Yaƙub gare shi in kuma tattara Isra’ila gare shi, gama an girmama ni a gaban Ubangiji Allahna kuma ne ƙarfina
6 And he said it is [too] trifling for being you of me servant to raise up [the] tribes of Jacob (and [the] preserved [ones] of *Q(K)*) Israel to bring back and I will make you a light of [the] nations to be salvation my to [the] end of the earth.
ya ce, “Ɗan ƙaramin abu ne ka zama bawana don ka maido da kabilar Yaƙub ka kuma dawo da waɗannan na Isra’ilawan da na kiyaye. Zan kuma mai da kai haske ga Al’ummai, don ka kawo cetona zuwa iyakokin duniya.”
7 Thus he says Yahweh [the] redeemer of Israel holy [one] its to despise life to [one who] abhors a nation to a servant of rulers kings they will see and they will stand up princes so they may bow down on account of Yahweh who [is] faithful [the] holy [one] of Israel and he has chosen you.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Fansa da kuma Mai Tsarkin nan na Isra’ila gare shi wanda al’ummai suka rena suka kuma ki, ga bawan masu mulki. “Sarakuna za su gan ka su kuma miƙe tsaye, sarakuna za su gani su kuma rusuna, saboda Ubangiji, wanda yake mai aminci, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, wanda ya zaɓe ka.”
8 Thus - he says Yahweh in a time of favor I will answer you and on a day of salvation I will help you and I will watch over you and I will make you a covenant of [the] people to raise up [the] land to give as inheritance inheritances desolate.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “A lokacin tagomashina zan amsa muku, kuma a ranar ceto zan taimake ku; zan kiyaye ku zan kuma sa ku zama alkawari ga mutane, don ku maido da ƙasa ku kuma sāke raba gādon kufai,
9 To say to [the] prisoners come out to [those] who [are] in darkness reveal yourselves on roads they will graze and [will be] on all bare heights pasture their.
don ku ce wa waɗanda suke cikin kurkuku, ‘Ku fito,’ ga waɗanda suke cikin duhu kuma, ‘Ku’yantu!’ “Za su yi kiwo kusa da hanyoyi su kuma sami wurin kiwo a kowane tudu.
10 Not they will be hungry and not they will be thirsty and not it will strike them burning heat and sun for [one who] has compassion on them he will guide them and to springs of water he will lead them.
Ba za su taɓa jin yunwa ko ƙishi ba, ba kuwa zafin hamada ko rana ta buge su ba. Shi da ya yi musu jinƙai zai jagorance su ya kuma bishe su kusa da maɓulɓulan ruwa.
11 And I will make all mountains my into road and highways my they will be lifted up!
Zan mayar da dukan duwatsu su zama hanyoyi, a kuma gyara manyan hanyoyina.
12 Here! these from a distance they will come and here! these from [the] north and from [the] west and these from [the] land of Sinim.
Duba, za su zo daga nesa waɗansu daga arewa, waɗansu daga yamma, waɗansu daga yankin Aswan.”
13 Shout for joy O heaven and be glad O earth (and break forth *Q(K)*) O mountains a shout of joy for he has comforted Yahweh people his and afflicted [people] his he has compassion on.
Ku yi sowa don farin ciki, ya ku sammai; ki yi farin ciki, ya ke duniya; ku ɓarke da waƙa, ya ku duwatsu! Gama Ubangiji ya ta’azantar da mutanensa zai kuma ji tausayin mutanensa da suke shan wahala.
14 And it said Zion he has forsaken me Yahweh and [the] Lord he has forgotten me.
Amma Sihiyona ta ce, “Ubangiji ya yashe ni, Ubangiji ya manta da ni.”
15 ¿ Will she forget a woman sucking child her from having compassion on [the] child of womb her also these they will forget and I not I will forget you.
“Yana yiwuwa mahaifiya ta manta da jariri a ƙirjinta ta kuma kāsa nuna tausayi ga yaron da ta haifa? Mai yiwuwa ta manta, amma ba zan taɓa manta da ke ba!
16 Here! on palms of hands I have inscribed you walls your [are] before me continually.
Duba, na zāna ki a tafin hannuwana; katangarki kullum suna a gabana.
17 They have made haste children your [those who] tear down you and [those who] make desolate you from you they will go out.
’Ya’yanki maza su komo da gaggawa, waɗanda suka lalatar da ke kuwa za su bar ki.
18 Lift up all around eyes your and see all of them they have gathered together they have come to you [by] [the] life of me [the] utterance of Yahweh that all of them like ornament[s] you will put on and you will tie on them like bride.
Ki ɗaga idanunki ki duba kewaye; dukan’ya’yanki sun taru suka kuma dawo gare ki. Muddin ina raye,” in ji Ubangiji, “Za ki yafa su duka kamar kayan ado; za ki yi ado da su, kamar amarya.
19 For waste places your and desolate [places] your and [the] land of destruction your for now you will be [too] cramped for [the] inhabitant[s] and they will be far away [those who] swallowed up you.
“Ko da yake an lalatar da ke aka kuma mai da ke kufai ƙasarki kuma ta zama kango, yanzu za ki kāsa sosai saboda yawan mutanenki, kuma waɗanda suka cinye ki za su kasance can da nisa.
20 Yet they will say in ears your [the] children of bereavement your it is cramped for me the place draw near! for me so let me dwell.
’Ya’yan da aka haifa a lokacin baƙin cikinki za su ce a kunnenki, ‘Wannan wuri ya yi mana kaɗan ƙwarai; ki ƙara mana wurin zama.’
21 And you will say in heart your who? did he father for me these [children] and I [was] bereaved and barren gone into exile - and thrust away and these [children] who? did he bring up here! I I remained to alone me these [children] where? [are] they.
Sa’an nan za ki ce a zuciyarki, ‘Wa ya haifa waɗannan? Na yi baƙin ciki na kuma zama wadda ba ta haihuwa; an yi mini daurin talala aka kuma ƙi ni. Wane ne ya yi renon waɗannan? An bar ni ni kaɗai, amma waɗannan, ina suka fito?’”
22 Thus he says [the] Lord Yahweh here! I will lift up to [the] nations hand my and to peoples I will raise standard my and they will bring sons your in a bosom and daughters your on a shoulder they will be carried.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Duba, zan yi alama wa Al’ummai, zan ɗaga tutana wa mutane; za su kawo’ya’yanki maza a hannuwansu su riƙe’ya’yanki mata a kafaɗunsu.
23 And they will be kings foster-fathers your and princesses their suckling-nurses your faces ground they will bow down to you and [the] dust of feet your they will lick up and you will know that I [am] Yahweh whom not they will be ashamed [those who] wait for me.
Sarakuna za su zama kamar iyayen reno, sarauniyoyinsu kuma za su yi renonku kamar uwaye. Za su rusuna a gabanki da fuskokinsu har ƙasa; za su lashe ƙura a ƙafafunki. Sa’an nan za ki san cewa ni ne Ubangiji; waɗanda suke sa zuciya gare ni ba za su sha kunya ba.”
24 ¿ Will it be taken from a warrior booty and or? [the] captive[s] of [the] righteous will it escape.
Za a iya ƙwace ganima daga jarumawa, ko a kuɓutar da kamammu daga hannun marasa tsoro?
25 For thus - he says Yahweh also a captive of a warrior he will be taken and [the] booty of a ruthless [person] it will be delivered and opponent your I I will oppose and children your I I will save.
Amma ga abin da Ubangiji yana cewa, “I, za a ƙwace kamammu daga jarumawa, a kuma karɓe ganima daga hannun marasa tsoro; zan gwabza da waɗanda suke gwabzawa da ke, zan kuwa ceci’ya’yanki.
26 And I will cause to eat [those who] maltreat you own flesh their and like sweet wine own blood their they will become drunk! and they will know all flesh that I [am] Yahweh deliverer your and redeemer your [the] mighty one of Jacob.
Zan sa masu zaluntarki su ci naman jikinsu; za su bugu da jininsu, sai ka ce sun sha ruwan inabi. Sa’an nan dukan mutane za su sani cewa ni, Ubangiji, ni ne Mai Cetonki, Mai Fansarki, Maɗaukakin nan na Yaƙub.”

< Isaiah 49 >