< Isaiah 38 >
1 In the days those he became sick Hezekiah to die and he went to him Isaiah [the] son of Amoz the prophet and he said to him thus he says Yahweh command to household your for [are] about to die you and not you will live.
A kwanakin nan sai Hezekiya ya kamu da ciwo ya kuma kusa ya mutu. Annabi Ishaya ɗan Amoz ya tafi wurinsa ya kuma ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce ka shirya gidanka, domin za ka mutu; ba za ka warke ba.”
2 And he turned Hezekiah face his to the wall and he prayed to Yahweh.
Hezekiya ya juye fuskarsa wajen bango ya kuma yi addu’a ga Ubangiji,
3 And he said I beg you O Yahweh remember please this: I have walked about before you in faithfulness and with a heart complete and the good in view your I have done and he wept Hezekiah weeping great.
“Ka tuna, ya Ubangiji, yadda na yi tafiya a gabanka da aminci da dukan zuciya na kuma yi abin da yake nagari a idanunka.” Sai Hezekiya ya yi kuka mai zafi.
4 And it came [the] word of Yahweh to Isaiah saying.
Sai maganar Ubangiji ta zo wa Ishaya cewa,
5 Go and you will say to Hezekiah thus he says Yahweh [the] God of David ancestor your I have heard prayer your I have seen tear[s] your here I he will add to days your fif-teen year[s].
“Ka tafi ka faɗa wa Hezekiya, ‘Ga abin da Ubangiji Allah na kakanka Dawuda, ya ce na ji addu’arka na kuma ga hawayenka; zan ƙara maka shekaru goma sha biyar ga rayuwarka.
6 And from [the] hand of [the] king of Assyria I will deliver you and the city this and I will defend the city this.
Zan kuwa cece ka da wannan birni daga hannun sarkin Assuriya. Zan kiyaye wannan birni.
7 And this for you [will be] the sign from with Yahweh that he will do Yahweh the thing this which he has spoken.
“‘Ga alamar Ubangiji gare ka cewa Ubangiji zai aikata kamar yadda ya yi alkawari.
8 Here I [am] about to turn back [the] shadow of the steps which it had gone down on [the] steps of Ahaz with the sun backwards ten steps and it went back the sun ten steps on the steps which it had gone down.
Zan sa inuwar da rana ta yi a kan matakalar Ahaz ta koma baya da taki goma.’” Saboda haka inuwar ta koma da baya daga fuskar rana har taki goma.
9 A writing of Hezekiah [the] king of Judah when was sick he and he lived from sickness his.
Rubutun Hezekiya sarkin Yahuda bayan ciwonsa da kuma warkarwarsa.
10 I I said in [the] half of days my let me go in [the] gates of Sheol I have been caused to miss [the] remainder of years my. (Sheol )
Na ce, “Cikin tsakiyar rayuwata dole in bi ta ƙofofin mutuwa a kuma raba ni da sauran shekaruna?” (Sheol )
11 I said not I will see Yahweh Yahweh in [the] land of the living not I will look at humankind again with [the] inhabitants of cessation.
Na ce, “Ba zan ƙara ganin Ubangiji ba, Ubangiji a ƙasa ta masu rai; ba zan ƙara ga wani mutum, ko in kasance tare da waɗanda suke zama a wannan duniya ba.
12 Dwelling-place my it has been pulled up and it has been removed from me like [the] tent of shepherd my I have rolled up like weaver life my from [the] loom he cuts off me from day unto night you make an end of me.
Kamar tentin makiyayi an rushe gidana aka kuma ƙwace ta daga gare ni. Kamar mai saƙa, na nannaɗe rayuwata, ya kuma yanke ni daga sandar saƙa; dare da rana ka kawo ni ga ƙarshe.
13 I have lain down until morning like lion so he breaks all bones my from day unto night you make an end of me.
Na yi jira da haƙuri har safiya, amma kamar zaki ya kakkarya ƙasusuwana duka; dare da rana ka kawo ni ga ƙarshe.
14 Like a swallow a crane so I chirp I moan like dove they are cast down eyes my to the height[s] O Lord oppression [belongs] to me stand surety for me.
Na yi kuka kamar mashirare ko zalɓe, na yi kuka kamar kurciya mai makoki. Idanuna suka rasa ƙarfi yayinda na duba sammai. Na damu; Ya Ubangiji, ka taimake ni!”
15 What? will I say and he has spoken to me and he he has acted I will walk deliberately all years my on [the] bitterness of self my.
Amma me zan ce? Ya riga ya yi mini magana, shi kansa ne kuma ya aikata. Zan yi tafiya da tawali’u dukan kwanakina saboda wahalar raina.
16 O Lord on them people live and to all in them [the] life of spirit my and may you restore to health me and preserve alive me.
Ubangiji, ta waɗannan abubuwa ne mutane suke rayuwa; ruhuna kuma yana samun rai a cikinsu shi ma. Ka maido mini da lafiya ka kuma sa na rayu.
17 Here! for welfare it was bitter to me bitterly and you you loved life my from [the] pit of destruction for you threw away behind back your all sins my.
Tabbatacce wannan kuwa saboda ribata ne cewa in sha irin wahalan nan. Cikin ƙaunarka ka kiyaye ni daga ramin hallaka; ka sa dukan zunubaina a bayanka.
18 For not Sheol it gives thanks to you death it praises you not they hope [those who] go down of [the] pit to faithfulness your. (Sheol )
Gama kabari ba zai yabe ka ba, matattu ba za su rera yabonka ba; waɗanda suka gangara zuwa rami ba za su sa zuciya ga amincinka ba. (Sheol )
19 [the] living [the] living He he gives thanks to you as I this day a father to children he makes known concerning faithfulness your.
Masu rai, masu rai, su suke yabonka, kamar yadda nake yi a yau; iyaye za su faɗa wa’ya’yansu game da amincinka.
20 Yahweh [is] to save me and songs my we will play all [the] days of lives our at [the] house of Yahweh.
Ubangiji zai cece ni, za mu kuma rera da kayan kiɗi masu tsirkiya dukan kwanakinmu a cikin haikalin Ubangiji.
21 And he said Isaiah let them take a cake of figs and let them rub [it] on the boil so he may live.
Ishaya ya riga ya ce, “Ku shirya curin da aka yi da’ya’yan ɓaure ku kuma shafa a marurun, zai kuwa warke.”
22 And he said Hezekiah what? [will be the] sign that I will go up [the] house of Yahweh.
Hezekiya ya riga ya yi tambaya ya ce, “Me zai zama alama ta cewa zan haura zuwa haikalin Ubangiji?”