< Hosea 8 >

1 To mouth your a horn like eagle over [the] house of Yahweh because they have transgressed covenant my and on law my they have rebelled.
“Ka sa kakaki a leɓunanka! Gaggafa tana a bisan gidan Ubangiji domin mutane sun tā da alkawarina suka kuma tayar wa dokata.
2 To me they cry out O God my we know you Israel.
Isra’ila ta yi mini kuka, ‘Ya Allahnmu, mun yarda da kai!’
3 It has rejected Israel good an enemy he will pursue him.
Amma Isra’ila sun ƙi abin da yake mai kyau; abokin gāba zai fafare su.
4 They they have made kings and not from me they have installed leaders and not I knew silver their and gold their they have made for themselves idols so that it may be cut off.
Suna naɗa sarakuna, ba da izinina ba; sun zaɓa shugabanni ba da yardanta ba. Da azurfa da zinariya sun ƙera gumaka wa kansu wanda zai kai zuwa ga hallakarsu.
5 He has rejected calf your O Samaria it has burned anger my on them until when? not will they be able innocence.
Ku zubar da gunkin maraƙinku, ya Samariya! Fushina yana ƙuna a kansu. Sai yaushe za su rabu da gumaka?
6 For [are] from Israel and it a craftsman he made it and not [is] God it for fragments it will become [the] calf of Samaria.
Su daga Isra’ila ne! Wannan maraƙi, mai aikin hannu ne ya yi shi; gunki ne ba Allah ba. Za a farfashe shi kucu-kucu, waccan maraƙin Samariya.
7 For a wind they sow and a storm-wind they will reap standing grain not [belongs] to it growth not it will produce flour perhaps it will produce strangers they will swallow it.
“Gama sun shuka iska don haka za su girbe guguwa. Hatsin da yake tsaye ba shi da kai, ba zai yi tsaba ba. Ko da ya yi tsaba ma, baƙi ne za su ci.
8 It will be swallowed Israel now they are among the nations like a vessel [which] there not [is] pleasure in it.
An haɗiye Isra’ila; yanzu tana cikin al’ummai kamar abin da ba shi da amfani.
9 For they they have gone up Assyria a wild donkey isolated to itself Ephraim they have hired (lovers *L(abh)*)
Gama sun haura zuwa Assuriya kamar jakin jejin da yake yawo shi kaɗai. Efraim ya sayar da kansa ga maza.
10 also for they will hire among the nations now I will gather them and they have begun a few from [the] burden of a king princes.
Ko da yake sun sayar da kansu a cikin al’ummai, yanzu zan tattara su wuri ɗaya. Za su fara lalacewa a ƙarƙashi danniyar babban sarki.
11 For he has multiplied Ephraim altars for sinning they have become to him altars for sinning.
“Ko da yake Efraim ya gina bagadai masu yawa don hadayun zunubi, waɗannan sun zama bagade don yin zunubi.
12 (I wrote *Q(k)*) for him ([the] numerous things of *Q(K)*) law my like a strange [thing] they are regarded.
Na rubuta musu abubuwa masu yawa na dokata, amma suka ɗauke su tamƙar wani baƙon abu ne.
13 [the] sacrifices of Gifts my they sacrifice flesh and they ate [it] Yahweh not he is pleased with them now he will remember iniquity their so he may punish sins their they Egypt they will return.
Suna miƙa hadayun da aka ba ni su kuma ci nama, amma Ubangiji ba ya jin daɗinsu. Yanzu zai tuna da muguntarsu yă kuma hukunta zunubansu. Za su koma Masar.
14 And he has forgotten Israel maker his and he has built palaces and Judah he has multiplied cities fortified and I will send fire on cities his and it will consume fortresses his.
Isra’ila ya manta da Mahaliccinsa ya kuma gina fadodi; Yahuda ya gina katanga a yawancin garuruwansa. Amma zan aiko da wuta a bisa biranensu da zai cinye kagaransu.”

< Hosea 8 >