< Haggai 2 >
1 In the seventh [month] on [day] twenty and one of the month it came [the] word of Yahweh by [the] hand of Haggai the prophet saying.
a ranar ashirin da ɗaya ga watan bakwai, maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai cewa,
2 Say please to Zerubbabel [the] son of Shealtiel [the] governor of Judah and to Joshua [the] son of Jehozadak the priest great and to [the] remnant of the people saying.
“Ka yi magana da Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel wanda yake gwamna a Yahuda, da Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist, da kuma dukan raguwar mutane. Ka tambaye su ka ce,
3 Who? among you [is] the [one who] remains who he saw the house this in splendor its former and what? [are] you seeing it now ¿ not [is] as it as nothing in view your.
‘Wane ne a cikinku ya ragu da ya ga wannan gida a darajarsa ta dā? Yaya yake a gare ku a yanzu? Bai yi kamar a bakin kome ba, ko ba haka ba?
4 And now be strong O Zerubbabel - [the] utterance of Yahweh and be strong O Joshua [the] son of Jehozadak the priest great and be strong O all [the] people of the land [the] utterance of Yahweh and work that I [am] with you [the] utterance of Yahweh of hosts.
Amma yanzu ka ƙarfafa, ya Zerubbabel,’ in ji Ubangiji. ‘Ka ƙarfafa, ya Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist. Ku ƙarfafa, dukanku mutanen ƙasar,’ in ji Ubangiji, ‘ku yi aiki. Gama ina tare da ku,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
5 The word which I cut with you when came out you from Egypt and spirit my [is] standing in midst of you may not you be afraid.
‘Wannan shi ne alkawarin da na yi da ku a lokacin da kuka fito daga Masar. Ruhuna kuwa yana tare da ku. Kada ku ji tsoro.’
6 For thus he says Yahweh of hosts yet one [time] [is] a little it and I [am] about to shake the heavens and the earth and the sea and the dry ground.
“Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ba da jimawa ba zan sāke girgiza sammai da kuma ƙasa, teku da busasshiyar ƙasa.
7 And I will shake all the nations and they will come [the] precious thing of all the nations and I will fill the house this splendor he says Yahweh of hosts.
Zan girgiza dukan al’ummai, marmarin kowace al’umma kuma zai taso, sa’an nan zan cika gidan nan da ɗaukaka,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
8 [belongs] to Me the silver and [belongs] to me the gold [the] utterance of Yahweh of hosts.
‘Da zinariya da azurfa duka nawa ne,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
9 Great it will be [the] splendor of the house this latter more than the former he says Yahweh of hosts and in the place this I will give peace [the] utterance of Yahweh of hosts.
‘Ɗaukakar gidan nan na yanzu za tă fi ɗaukakar gidan nan na dā,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki. ‘A wannan wuri kuma zan ba da salama,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.”
10 On [day] twenty and four of the ninth [month] in year two of Darius it came [the] word of Yahweh to Haggai the prophet saying.
A ranar ashirin da huɗu ga watan tara, a shekara ta biyu ta mulkin Dariyus, maganar Ubangiji ta zo wa annabi Haggai cewa,
11 Thus he says Yahweh of hosts ask please the priests instruction saying.
“Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ku tambayi firist abin da doka ta ce.
12 There! - he will carry someone flesh of holiness in [the] skirt of garment his and he will touch with skirt his bread and cooked food and wine and oil and every food ¿ will it become holy and they answered the priests and they said no.
Idan mutum yana riƙe da naman da aka keɓe a rigarsa, sa’an nan kuma wannan rigar ta taɓa burodi, ko dafaffen abinci, ko ruwan inabi, ko mai, ko kowane irin abinci, wannan zai sa abin yă zama tsarkake?’” Firistoci suka amsa, suka ce, “A’a.”
13 And he said Haggai if he will touch a [person] unclean of a corpse all these [things] ¿ will it become unclean and they answered the priests and they said it will become unclean.
Sa’an nan Haggai ya ce, “In mutumin da ya ƙazantar da kansa ta wurin taɓa gawa, ya taɓa wani daga cikin waɗannan abubuwa, za su ƙazantu?” Firistoci suka amsa, suka ce, “I, zai ƙazantu.”
14 And he answered Haggai and he said [is] thus the people this and [is] thus the nation this before me [the] utterance of Yahweh and [is] thus all [the] work of hands their and [that] which they will bring near there [is] unclean it.
Sai annabi Haggai ya ce, “‘Haka yake da wannan mutane da kuma wannan al’umma a gabana,’ in ji Ubangiji. ‘Duk abin da suke yi da kuma dukan abin da suke miƙawa ƙazantattu ne.
15 And therefore set please heart your from the day this and up-wards from before put a stone to a stone in [the] temple of Yahweh.
“‘Yanzu kuwa sai ku yi la’akari da wannan daga wannan rana zuwa gaba, ku tuna yadda al’amura suke kafin a ɗora wani dutse bisa wani a haikalin Ubangiji.
16 From when were they someone came to a heap of twenty [measures] and it was ten someone came to the wine vat to draw fifty [measures] a winepress and it was twenty.
A lokacin, idan wani ya tafi wurin tsibin da zai auna mudu ashirin, sai yă iske mudu goma kawai. Idan kuma wani ya tafi wurin matse ruwan inabi don yă ɗebo lita hamsin, sai yă tarar da lita ashirin kawai.
17 I struck you with blight and with mildew and with hail all [the] work of hands your and not you to me [the] utterance of Yahweh.
Na mai da aikin da kuka sha wahala kuka yi ya zama banza ta wurin saukar da burtuntuna, da fumfuna, da ƙanƙara, duk da haka ba ku juyo gare ni ba,’ in ji Ubangiji.
18 Set please heart your from the day this and up-wards from day twenty and four of the ninth [month] from the day when it was founded [the] temple of Yahweh set heart your.
‘Daga wannan rana zuwa gaba, wato, rana ta ashirin da huɗu ga watan tara, ku lura da ranar da aka kafa harsashin haikalin Ubangiji. Ku lura da kyau.
19 ¿ Still [is] the seed in the granary and to the vine and the fig tree and the pomegranate and [the] tree of the olive not it has borne [fruit] from the day this I will bless.
Akwai sauran irin da ya rage a rumbu? Har yanzu, kuringar inabi da itacen ɓaure, rumman da itacen zaitun ba su ba da’ya’ya ba tukuna. “‘Amma daga wannan rana zuwa gaba zan sa muku albarka.’”
20 And it came [the] word of Yahweh - a second [time] to Haggai on [day] twenty and four of the month saying.
Maganar Ubangiji ta zo wa annabi Haggai sau na biyu a rana ta ashirin da huɗu ga wata cewa,
21 Say to Zerubbabel [the] governor of Judah saying I [am] about to shake the heavens and the earth.
“Ka faɗa wa Zerubbabel gwamnan Yahuda cewa zan girgiza sammai da ƙasa.
22 And I will overthrow [the] throne of kingdoms and I will destroy [the] strength of [the] kingdoms of the nations and I will overthrow chariotry and riders its and they will go down horses and riders their each by [the] sword of brother his.
Zan hamɓarar da gadajen mulki in kuma ragargaza ƙarfin ƙasashen al’ummai. Zan tumɓuke kekunan yaƙi da mahayansu; dawakai da mahayansu za su mutu, kowane ta wurin takobin ɗan’uwansu.
23 On the day that [the] utterance of Yahweh of hosts I will take you O Zerubbabel [the] son of Shealtiel servant my [the] utterance of Yahweh and I will make you like signet-ring for you I have chosen [the] utterance of Yahweh of hosts.
“‘A wannan rana,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki, ‘Zan ɗauke ka, bawana Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel,’ in ji Ubangiji, ‘in kuma maishe ka kamar zoben hatimi, gama na zaɓe ka,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.”