< Genesis 17 >

1 And he was Abram a son of ninety year[s] and nine years and he appeared Yahweh to Abram and he said to him I [am] God Almighty walk about before me and be blameless.
Sa’ad da Abram ya yi shekaru 99, sai Ubangiji ya bayyana a gare shi ya ce, ni “Ni ne Allah Maɗaukaki, ka yi tafiya a gabana ka kuma zama marar abin zargi.
2 So let me make covenant my between me and between you so I may increase you with muchness muchness.
Zan tabbatar da alkawarina tsakanina da kai, zan kuma ƙara zuriyarka ta yi yawa.”
3 And he fell Abram on face his and he spoke with him God saying.
Abram ya rusuna da fuskarsa har ƙasa, Allah kuma ya ce masa,
4 I here! covenant my [is] with you and you will become a father of a multitude of nations.
“Gare ni kam, wannan shi ne alkawarina da kai, za ka zama mahaifin al’ummai masu yawa.
5 And not it will be called again name your Abram and it will be name your Abraham for a father of a multitude of nations I have made you.
Ba za a ƙara kiranka Abram ba; sunanka zai zama Ibrahim, gama na mai da kai uban al’ummai masu yawa.
6 And I will make fruitful you with muchness muchness and I will make you into nations and kings from you they will come out.
Zan sa ka azurta sosai, zan yi al’ummai daga cikinka, sarakuna kuma za su fito daga cikinka,
7 And I will establish covenant my between me and between you and between offspring your after you for generations their to a covenant of perpetuity to become for you God and for offspring your after you.
zan kafa alkawarina kamar madawwamin alkawari tsakanina da kai da kuma zuriyarka bayanka har tsararraki masu zuwa, in zama Allahnka da kuma Allahn zuriyarka a bayanka.
8 And I will give to you and to offspring your after you - [the] land of sojournings your all [the] land of Canaan to a possession of perpetuity and I will become for them God.
Dukan ƙasar Kan’ana inda kake baƙo a yanzu, zan ba da ita a matsayin madawwamiyar mallaka gare ka da kuma zuriyarka a bayanka, zan kuma zama Allahnsu.”
9 And he said God to Abraham and you covenant my you will keep you and offspring your after you for generations their.
Sa’an nan Allah ya ce wa Ibrahim. “Kai fa, sai ka kiyaye alkawarina, kai da zuriyarka bayanka, har tsararraki masu zuwa.
10 This [is] covenant my which you will keep between me and between you and between offspring your after you they will be circumcised of you every male.
Wannan shi ne alkawarina da kai da kuma zuriyarka a bayanka, alkawarin da za ka kiyaye ke nan. Kowane namiji a cikinku kuwa za a yi masa kaciya.
11 And you will be circumcised [the] flesh of foreskin your and it will become a sign of [the] covenant between me and between you.
Za ku yi kaciya, za tă kuma zama alamar alkawari tsakanina da kai.
12 And a son of eight days he will be circumcised of you every male for generations your one born of [the] household and a purchase of silver from every son of foreignness who not [is] one of offspring your he.
Daga yanzu duk namijin da aka haifa a cikinku za a yi masa kaciya a rana ta takwas har dukan zamananku, ko haifaffen gida ne, ko sayayye da kuɗi daga kowane baƙo wanda ba na zuriyarku ba.
13 Definitely - he will be circumcised [the] one born of household your and [the] purchase of silver your and it will be covenant my in flesh your to a covenant of perpetuity.
Ko haifaffe a gidanka ko an sayo da kuɗi, dole a yi musu kaciya. Alkawarina cikin jikinku zai kasance madawwamin alkawari.
14 And an uncircumcised - male who not he will be circumcised [the] flesh of foreskin his and it will be cut off the person that from kinspeople its covenant my he has broken.
Kowane namijin da ba a yi masa kaciya a jiki ba, za a fid da shi daga cikin mutanensa; domin ya karya alkawarina.”
15 And he said God to Abraham Sarai wife your not you will call name her Sarai for [is] Sarah name her.
Allah ya kuma ce wa Ibrahim, “Game da Saira matarka kuwa, ba za ka ƙara kiranta Saira ba, sunanta zai zama Saratu.
16 And I will bless her and also I will give from her to you a son and I will bless her and she will become nations kings of peoples from her they will be.
Zan sa mata albarka, ban da haka ma, zan ba ka ɗa ta wurinta, zan sa mata albarka, za tă kuwa zama mahaifiyar al’ummai; sarakunan mutane za su fito daga gare ta.”
17 And he fell Abraham on face his and he laughed and he said in heart his ¿ to a son of one hundred year[s] will he be born and or? Sarah ¿ a daughter of ninety year[s] will she bear a child.
Ibrahim ya rusuna da fuskarsa har ƙasa, ya yi dariya, ya ce wa kansa, “Za a haifi ɗa wa mutum mai shekaru ɗari? Saratu za tă haifi ɗa tana da shekaru tasa’in?”
18 And he said Abraham to God if Ishmael he will live before you.
Ibrahim ya kuma ce wa Allah, “Me zai hana a dai bar Ishmayel kawai yă gāji alkawarin nan da ka yi mini.”
19 And he said God but Sarah wife your [is] about to bear to you a son and you will call name his Isaac and I will establish covenant my with him to a covenant of perpetuity for offspring his after him.
Sai Allah ya ce, “Duk da haka dai, matarka Saratu za tă haifi maka ɗa; za ka kuma kira shi Ishaku. A kansa zan tabbatar da madawwamin alkawarina, da kuma ga zuriyarsa da za su zo bayansa.
20 And to Ishmael I have heard you here! - I will bless him and I will make fruitful him and I will multiply him with muchness muchness two [plus] ten princes he will father and I will make him into a nation great.
Game da Ishmayel kuwa, na ji ka. Tabbatacce zan albarkace shi, zan sa yă azurta, zai kuma ƙaru ƙwarai. Zai zama mahaifin masu mulki goma sha biyu, zan kuma maishe shi babban al’umma!
21 And covenant my I will establish with Isaac whom she will bear to you Sarah to the time this in the year following.
Amma dai zan kafa alkawarina da Ishaku wanda Saratu za tă haifa maka war haka shekara mai zuwa.”
22 And he finished to speak with him and he went up God from with Abraham.
Da ya gama magana da Ibrahim, sai Allah ya tashi daga gare shi.
23 And he took Abraham Ishmael son his and all those born of household his and all [the] purchase of silver his every male among [the] men of [the] household of Abraham and he circumcised [the] flesh of foreskin their on [the] substance of the day this just as he had spoken with him God.
A wannan rana, Ibrahim ya ɗauki ɗansa Ishmayel da dukan waɗanda aka haifa cikin gidansa, da waɗanda aka sayo da kuɗinsa, ya kuwa yi wa kowane namiji a cikin gidansa kaciya kamar yadda Allah ya faɗa masa.
24 And Abraham [was] a son of ninety and nine year[s] when was circumcised he [the] flesh of foreskin his.
Ibrahim yana da shekara tasa’in da tara sa’ad da aka yi masa kaciya,
25 And Ishmael son his [was] a son of thir-teen year[s] when was circumcised he [the] flesh of foreskin his.
Ishmayel ɗansa kuma yana da shekara goma sha uku.
26 On [the] substance of the day this he was circumcised Abraham and Ishmael son his.
Aka yi wa Ibrahim da ɗansa Ishmayel kaciya a rana ɗaya.
27 And all [the] men of household his one born of [the] household and a purchase of silver from with a son of foreignness they were circumcised with him.
Aka yi wa kowane namiji a gidan Ibrahim kaciya, da waɗanda aka haifa a gidansa, da waɗanda aka sayo da kuɗi daga baƙo.

< Genesis 17 >