< Ezekiel 11 >
1 And it lifted up me a spirit and it brought me to [the] gate of [the] house of Yahweh eastern which faces east-ward and there! [were] at [the] entrance of the gate twenty and five man and I saw in midst of them Jaazaniah [the] son of Azzur and Pelatiah [the] son of Benaiah [the] leaders of the people.
Sa’an nan Ruhu ya ɗaga ni sama ya kawo ni ƙofar gidan Ubangiji wadda take fuskantar gabas. Can a mashigi zuwa ƙofar akwai mutum ashirin da biyar, na kuma ga a cikinsu akwai Ya’azaniya ɗan Azzur da Felatiya ɗan Benahiya, shugabannin jama’a.
2 And he said to me O son of humankind these [are] the people who plan wickedness and who counsel counsel of evil in the city this.
Ubangiji ya ce mini, “Ɗan mutum, waɗannan su ne mutanen da suke ƙulla mugunta suna kuma ba da muguwa shawara a cikin wannan birni.
3 Who say not [is] in [the] near [future] to build houses it [is] the pot and we [are] the meat.
Suna cewa, ‘Lokaci bai yi kusa da za a gina gidaje ba? Wannan birni yana tukunyar dahuwa, mu ne kuwa naman.’
4 Therefore prophesy on them prophesy O son of humankind.
Saboda haka yi annabci a kansu; yi annabci, ɗan mutum.”
5 And it fell on me [the] spirit of Yahweh and he said to me say thus he says Yahweh thus you have said O house of Israel and [the] thoughts of spirit your I I know it.
Sai Ruhun Ubangiji ya sauko a kaina, ya kuma faɗa mini in ce, “Ga abin da Ubangiji yana cewa, haka kuke cewa, ya gidan Isra’ila, amma na san abin da yake a zuciyarku.
6 You have multiplied slain [ones] your in the city this and you have filled streets its [the] slain.
Kun kashe mutane da yawa a wannan birni kuka kuma cika titunanta da gawawwaki.
7 Therefore thus he says [the] Lord Yahweh slain [ones] your which you have put in [the] midst of it they [are] the meat and it [is] the pot and you he will bring out from [the] midst of it.
“Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa gawawwakin da kuka zubar a can su ne naman, wannan birni kuwa ita ce tukunya, amma zan kore ku daga cikinta.
8 A sword you have feared and a sword I will bring on you [the] utterance of [the] Lord Yahweh.
Kuna jin tsoron takobi, kuma takobi ne zan kawo muku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
9 And I will bring out you from [the] midst of it and I will give you in [the] hand of strangers and I will bring about on you judgments.
Zan kore ku daga birnin in miƙa ku a hannuwan baƙi in kuma azabtar da ku.
10 By the sword you will fall on [the] territory of Israel I will judge you and you will know that I [am] Yahweh.
Za ku mutu ta wurin takobi, zan kuma hukunta ku a iyakokin Isra’ila. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
11 It not it will become for you a pot and you you will become in [the] midst of it meat to [the] border of Israel I will judge you.
Wannan birni ba za tă zama muku tukunya ba, ba kuwa za ku zama nama a cikinta ba; zan hukunta ku a iyakokin Isra’ila.
12 And you will know that I [am] Yahweh whom in statutes my not you have walked and judgments my not you have done and according to [the] judgments of the nations which [are] around you you have done.
Za ku kuwa san cewa ni ne Ubangiji, gama ba ku bi ƙa’idodina ba balle ku kiyaye dokokina, amma kuka bi hanyoyin al’ummai kewaye da ku.”
13 And it was when prophesied I and Pelatiah [the] son of Benaiah he died and I fell on face my and I cried out a voice great and I said alas! O Lord Yahweh complete destruction [are] you? making with [the] remnant of Israel.
Yanzu yayinda nake yin annabci, sai Felatiya ɗan Benahiya ya mutu. Sai na fāɗi rubda ciki na kuma yi kuka da babbar murya na ce, “Kash, Ubangiji Mai Iko Duka! Za ka hallaka raguwar Isra’ila ƙaƙaf ne?”
14 And it came [the] word of Yahweh to me saying.
Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
15 O son of humankind brothers your brothers your [the] people of redemption your and all [the] house of Israel all of it whom they said to them [the] inhabitants of Jerusalem be distant from with Yahweh to us it it has been given the land to a possession.
“Ɗan mutum,’yan’uwanka,’yan’uwanka waɗanda suke danginka na cikinka da kuma dukan gidan Isra’ila su ne waɗanda mutanen Urushalima suka ce, ‘Su ne da nisa daga Ubangiji; an ba mu wannan ƙasa ta zama mallakarmu.’
16 Therefore say thus he says [the] Lord Yahweh that I have removed far away them among the nations and that I have scattered them among the lands and I have become for them a sanctuary a little in the lands where they have gone there.
“Saboda haka ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ko da yake na kore su zuwa cikin al’ummai na kuma warwatsa su cikin ƙasashe, duk da haka na zama wuri mai tsarki a gare su a ƙasashen da suka tafi.’
17 Therefore say thus he says [the] Lord Yahweh and I will gather you from the peoples and I will gather you from the lands which you have been scattered among them and I will give to you [the] land of Israel.
“Saboda haka, ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan tattaro ku daga al’ummai in kuma dawo da ku daga ƙasashen da aka warwatsa ku, zan kuwa sāke mayar muku da ƙasar Isra’ila.’
18 And they will come there towards and they will remove all detestable things its and all abominations its from it.
“Za su dawo gare ta su kawar da dukan mugayen siffofi da gumaka masu banƙyama.
19 And I will give to them a heart one and a spirit new I will put in inner being your and I will remove [the] heart of stone from flesh their and I will give to them a heart of flesh.
Zan ba su zuciya ɗaya in kuma sa sabon ruhu a cikinsu; zan fid da zuciyar dutse daga gare su in kuma ba su zuciya ta nama.
20 So that in statutes my they may walk and judgments my they may keep and they will do them and they will become for me a people and I I will become for them God.
Sa’an nan za su bi ƙa’idodina su kuma yi hankali ga kiyaye dokokina. Za su zama mutanena, ni kuwa zan zama Allahnsu.
21 And to [the] heart of detestable things their and abominations their heart their [is] going conduct their on own head their I will requite [the] utterance of [the] Lord Yahweh.
Amma game da waɗanda zukatansu suka karkata ga bin mugayen siffofi da gumakan banƙyama, zan sāka musu gwargwadon ayyukansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
22 And they lifted up the cherubim wings their and the wheels [were] close by them and [the] glory of [the] God of Israel [was] above them from to above.
Sa’an nan kerubobi, tare da da’irori kusa da su, suka buɗe fikafikansu, ɗaukakar Allah kuwa tana a bisansu.
23 And it went up [the] glory of Yahweh from over [the] middle of the city and it stood still over the mountain which [was] from [the] east of the city.
Ɗaukakar Ubangiji ta haura daga cikin birnin ta sauka a bisa dutse gabas da shi.
24 And a spirit it lifted up me and it brought me Chaldea towards to the exile[s] in the vision by [the] spirit of God and it went up from on me the vision which I had seen.
Ruhu ya ɗaga ni sama ya kuma kawo ni ga masu zaman bauta a ƙasar Babilon cikin wahayin da Ruhun Allah ya bayar. Sa’an nan wahayin da na gani ya rabu da ni,
25 And I spoke to the exile[s] all [the] words of Yahweh which he had shown me.
na kuwa faɗa wa masu zaman bautan dukan abin da Ubangiji ya nuna mini.