< Exodus 20 >
1 And he spoke God all the words these saying.
Sai Allah ya faɗi waɗannan kalmomi ya ce,
2 (I *L(p)*) [am] Yahweh (God your *L(p)*) who I brought out you from [the] land of Egypt (from a house of *L(p)*) (slaves. *L(b+p)*)
“Ni ne Ubangiji Allahnka, wanda ya fitar da ku daga Masar, daga ƙasar bauta.
3 Not it will be[long] (to you gods other *L(p)*) on (face my. *L(p)*)
“Ba za ka yi wa kanka waɗansu alloli ba sai ni.
4 Not you must make (for yourself *L(p)*) an image - and any (form *L(p)*) (which *L(b+p)*) [is] in the heavens - (above *L(p)*) (and which *L(b+p)*) ([is] on the earth beneath and which [is] in the waters - from under to the earth. *L(p)*)
Ba za ka yi wa kanka waɗansu alloli a siffar wani abu a sama a bisa, ko a ƙarƙashin ƙasa, ko a ƙarƙashin ruwa ba.
5 Not (you must bow down to them *L(p)*) and not (you must be enticed to serve them *L(p)*) for I Yahweh God your [am] a God jealous visiting iniquity of fathers on children on a third generation and on a fourth generation (of [those who] hate me. *L(p)*)
Ba za ka durƙusa gare su, ko ka yi musu sujada ba. Gama ni, Ubangiji Allahnka mai kishi ne, nakan hukunta’ya’ya har tsara ta uku da ta huɗu na waɗanda suke ƙina,
6 (And doing covenant loyalty to thousands *L(p)*) to [those who] love me and to [those who] keep commandments my.
amma ina nuna ƙauna ga tsara dubbai na waɗanda suke ƙaunata, suke kuma kiyaye umarnaina.
7 Not you must take [the] name of Yahweh God your for emptiness for not he will leave unpunished Yahweh [the one] who he will take name his for emptiness.
Ba za ka yi amfani da sunan Ubangiji Allahnka a banza ba, gama Ubangiji zai hukunta duk wanda ya mai da sunansa banza.
8 (Remember *L(p)*) ([the] day of the sabbath to set apart as holy it. *L(p)*)
Ka tuna da ranar Asabbaci domin ka kiyaye ta da tsarki.
9 (Six days you will labor and you will do *L(p)*) all (work your. *L(p)*)
Kwana shida za ka yi dukan aikinka,
10 And [the] day (seventh [is] a sabbath - *L(p)*) to Yahweh (God your *L(p)*) not (you must do *L(p)*) any (work *L(p)*) you - and son your (and daughter your [male] servant your and female servant your and livestock your and sojourner your who [is] in gates your. *L(p)*)
amma rana ta bakwai Asabbaci ne ga Ubangiji, Allahnka. A ranar ba za ka yi wani aiki ba, ko kai, ko ɗanka, ko’yarka, ko bawa, ko baiwa, ko dabbarka, ko baƙon da yake zama tare da kai.
11 For six days he made Yahweh the heavens and the earth the sea and all that [is] in them and he rested on the day seventh there-fore he blessed Yahweh [the] day of the sabbath and he set apart as holy it.
Gama kwana shida Ubangiji ya halicci sama da ƙasa, da teku, da duk abin da yake cikinsu, amma ya huta a rana ta bakwai. Saboda haka Ubangiji ya albarkaci ranar Asabbaci, ya kuma mai da ita mai tsarki.
12 Honor father your and mother your so that they may be long! days your on the land which Yahweh God your [is] about to give to you.
Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka, domin ka yi tsawon rai a ƙasar da Ubangiji Allahnka yake ba ka.
13 (Not you must murder. *L(p)*)
Ba za ka yi kisankai ba.
14 (Not you must commit adultery. *L(p)*)
Ba za ka yi zina ba.
15 (Not you must steal. *L(p)*)
Ba za ka yi sata ba.
16 Not you must testify against neighbor your testimony of falsehood.
Ba za ka ba da shaidar ƙarya a kan maƙwabcinka ba.
17 Not you must covet [the] house of neighbor your not you must covet [the] wife of neighbor your and [male] servant his and female servant his and ox his and donkey his and all that [belongs] to neighbor your.
Ba za ka yi ƙyashin gidan maƙwabcinka ba. Ba za ka yi ƙyashin matar maƙwabcinka ba, ko bawansa, ko baiwarsa, ko sansa, ko jakinsa, ko duk abin da yake na maƙwabcinka ba.”
18 And all the people [were] seeing the thunder claps and the lightning and [the] sound of the ram's horn and the mountain smoking and it saw the people and they trembled and they stood from a distance.
Da mutane suka ga tsawa da walƙiya, suka ji karar ƙaho, suka kuma ga dutsen yana hayaƙi, sai suka yi rawar jiki don tsoro. Suka tsaya da nisa
19 And they said to Moses speak you with us so let us listen and may not he speak with us God lest we should die.
suka ce wa Musa, “Ka yi magana da mu da kanka, za mu kasa kunne. Amma kada Allah ya yi mana magana, don kada mu mutu.”
20 And he said Moses to the people may not you be afraid for in order to put to [the] test you he has come God and in order that may be fear his on faces your to not you will sin.
Musa ya ce wa mutane, “Kada ku ji tsoro, gama Allah ya zo don yă gwada ku, don ku riƙa girmama shi, don kuma kada ku yi zunubi.”
21 And it stood the people from a distance and Moses he drew near to the thick darkness where [was] there God.
Sa’ad da mutane suka tsattsaya da nesa, sai Musa ya matsa kusa da girgije mai duhu, inda Allah yake.
22 And he said Yahweh to Moses thus you will say to [the] people of Israel you you have seen that from the heavens I have spoken with you.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka faɗa wa Isra’ilawa wannan. ‘Kun gani da kanku cewa na yi magana da ku daga sama.
23 Not you must make! with me gods of silver and gods of gold not you must make for yourselves.
Kada ku yi waɗansu alloli in ban da ni, kada ku yi wa kanku allolin azurfa ko na zinariya.
24 An altar of earth you will make for me and you will sacrifice on it burnt offerings your and peace offerings your sheep your and cattle your in every place where I will cause to be remembered name my I will come to you and I will bless you.
“‘Ku yi mini bagaden ƙasa, ku kuma miƙa mini hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama, za ku hadayar da tumakinku da awakinku da shanu. Duk inda na sa a girmama sunana, zan zo wurinku, in sa muku albarka.
25 And if an altar of stones you will make for me not you must build them hewn [stone] for tool your you have wielded on it and you have profaned it.
In kuka yi mini bagade dutse, kada ku gina shi da sassaƙaƙƙun duwatsu, gama inda guduma ta taɓa duwatsun, sun haramtu ke nan.
26 And not you must go up on steps to altar my that not it will be uncovered nakedness your on it.
Kada ku gina wa bagadena matakala, domin kada yayinda wani yana hawa, mutane su ga tsiraicinsa.’