< Exodus 16 >
1 And they set out from Elim and they came all [the] congregation of [the] people of Israel to [the] wilderness of Sin which [is] between Elim and between Sinai on [the] fif-teen day of the month second of going out their from [the] land of Egypt.
Dukan taron Isra’ila suka tashi daga Elim suka zo hamadar Sin, wadda take tsakanin Elim da Sinai, a rana ta goma sha biyar ga wata biyu, bayan sun fito daga Masar.
2 (And they grumbled *Q(K)*) all [the] congregation of [the] people of Israel on Moses and on Aaron in the wilderness.
A hamadan, dukan taro suka yi gunaguni a kan Musa da Haruna.
3 And they said to them [the] people of Israel who? will he give died we by [the] hand of Yahweh in [the] land of Egypt when sat we at [the] pot of the meat when ate we food to abundance for you have brought out us into the wilderness this to put to death all the assembly this by hunger.
Isra’ilawa suka ce musu, “Da ma a hannun Ubangiji ne muka mutu a Masar, inda muka zauna kewaye da tukwanen nama, muna cin duk abincin da muke so, amma kun kawo mu cikin wannan hamada don ku kashe dukan wannan taro da yunwa.”
4 And he said Yahweh to Moses here I [am] about to rain down for you bread from the heavens and it will go out the people and they will gather a matter of a day in day its so that I should put to [the] test it ¿ will it walk in law my or? not.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Zan zubo muku burodi kamar ruwa daga sama. Mutanen za su fita kowace rana su tattara abin da zai ishe su na ranan. Ta haka zan gwada su in ga ko za su bi umarnaina.
5 And it will be on the day sixth and they will prepare [that] which they will bring and it will be double to [that] which they will gather day - day.
A rana ta shida za su shirya abin da suka kwaso, wannan kuwa zai zama ninki biyu na abin da sukan tattara na sauran ranaku.”
6 And he said Moses and Aaron to all [the] people of Israel evening and you will know that Yahweh he brought out you from [the] land of Egypt.
Saboda haka Musa da Haruna suka ce wa dukan Isra’ila, “Da yamma za ku sani Ubangiji ne ya fitar da ku daga Masar.
7 And morning and you will see [the] glory of Yahweh because has heard he grumblings your on Yahweh and [are] we what? that (you will cause to grumble *Q(K)*) on us.
Da safe za ku ga ɗaukakar Ubangiji, saboda ya ji gunaguninku a kansa. Wane mu, da za ku yi gunaguni a kanmu?”
8 And he said Moses when gives Yahweh to you in the evening meat to eat and bread in the morning to be satisfied because has heard Yahweh grumblings your which you [are] grumbling on him and [are] we what? not [are] on us grumblings your for on Yahweh.
Musa ya kuma ce, “Za ku san cewa shi ne Ubangiji, sa’ad da ya ba ku nama ku ci da yamma, da kuma duk burodin da kuke so da safe, saboda ya ji gunagunin da kuka yi a kansa. Namu a wane? Ai, gunaguninku ba a kanmu ba, amma a kan Ubangiji ne.”
9 And he said Moses to Aaron say to all [the] congregation of [the] people of Israel draw near before Yahweh for he has heard grumblings your.
Sai Musa ya ce wa Haruna, “Ka faɗa wa dukan taron Isra’ila, ‘Ku zo gaban Ubangiji, gama ya ji gunaguninku.’”
10 And it was when spoke Aaron to all [the] congregation of [the] people of Israel and they turned to the wilderness and there! [the] glory of Yahweh it appeared in the cloud.
Yayinda Haruna yake magana da dukan taron Isra’ila, sai suka duba wajen hamada, sai ga ɗaukakar Ubangiji tana bayyana a girgije.
11 And he spoke Yahweh to Moses saying.
Ubangiji ya ce wa Musa,
12 I have heard [the] grumblings of [the] people of Israel speak to them saying between the two evenings you will eat meat and in the morning you will be satisfied bread and you will know that I [am] Yahweh God your.
“Na ji gunagunin Isra’ilawa. Ka faɗa musu, ‘A tsakanin fāɗuwar rana da almuru, za ku ci nama, da safe kuma za ku ƙoshi da burodi. Sa’an nan za ku sani ni ne Ubangiji Allahnku.’”
13 And it was in the evening and it came up the quail and it covered the camp and in the morning it was [the] layer of the dew around the camp.
Da yamman wannan rana, sai makware suka rufe dukan sansani, da safe kuma sai ga raɓa ta kewaye sansani.
14 And it went up [the] layer of dew and there! [was] on [the] surface of the wilderness thin [stuff] flake-like thin [stuff] like frost on the ground.
Lokacin da raɓar ta watse, sai ga wani abu kamar tsaki, falle-falle kuma da laushi, fari, kamar hazo, a ƙasa.
15 And they saw [the] people of Israel and they said each to brother his what? [is] it for not they knew what? [was] it and he said Moses to them it [is] the bread which he has given Yahweh to you to food.
Sa’ad da Isra’ilawa suka ga wannan, sai suka ce wa junansu, “Mene ne wannan?” Gama ba su san ko mene ne ba. Musa ya ce musu, “Wannan shi ne burodin da Ubangiji ya ba ku ku ci.
16 This [is] the word which he commands Yahweh gather some of it everyone to [the] mouth of food his an omer for the head [the] number of people your everyone for [those] who [are] in tent his you will take.
Wannan shi ne abin da Ubangiji ya umarta, ‘Kowane mutum zai tattara bisa ga bukatarsa. Ku tara rabin gallon don mutum guda da yake cikin tentinku.’”
17 And they did so [the] people of Israel and they gathered [it] the [one who] made much and the [one who] made little.
Isra’ilawa suka yi kamar yadda aka faɗa musu, waɗansu suka tattara da yawa, waɗansu kuma kaɗan.
18 And they measured [it] by the omer and not he had a surplus the [one who] made much and the [one who] made little not he had a lack everyone to [the] mouth of food his they had gathered.
Da suka gwada a mudu, wanda ya tattara da yawa bai sami mafi yawa ba, wanda kuma ya tattara kaɗan bai sami ƙanƙani ba. Kowane mutum ya tattara daidai bukatarsa.
19 And he said Moses to them everyone may not him leave over any of it until morning.
Sa’an nan Musa ya ce musu, “Kada wani yă bar saura har safe.”
20 And not they listened to Moses and they left over people some of it until morning and it became rotten worms and it stank and he was angry towards them Moses.
Duk da haka waɗansu ba su kula da umarnin Musa ba, suka bar saura har safe, kashegari kuwa ta yi tsutsotsi, ta ruɓe, sai Musa ya yi fushi da su.
21 And they gathered it in the morning in the morning everyone according to [the] mouth of food his and it was warm the sun and it melted.
Kowace safiya, kowanne mutum yakan tattara daidai bukatarsa, lokacin da rana ta yi zafi, sai ta narke.
22 And it was - on the day sixth they gathered bread of double two omer[s] for the one and they came all [the] leaders of the congregation and they told to Moses.
A rana ta shida, suka tattara ninki biyu, mudu biyu ga mutum guda, sai shugabannin taron suka zo suka kawo ƙara wurin Musa.
23 And he said to them it [is that] which he said Yahweh a sabbath observance a sabbath of holiness to Yahweh [is] tomorrow [that] which you will bake bake and [that] which you will boil boil and all the surplus leave for yourselves for keeping until the morning.
Shi kuma ya ce musu, “Wannan shi ne umarnin Ubangiji, ‘Gobe za tă zama ranar hutu, Asabbaci mai tsarki ga Ubangiji. Domin haka sai ku toya abin da kuke so ku toya, ku kuma dafa abin da kuke so ku dafa. Abin da ya rage ku ajiye har safe.’”
24 And they left it until the morning just as he had commanded Moses and not it stank and a maggot not it was in it.
Sai suka bar saura har safe, kamar yadda Musa ya umarta, bai kuwa yi wari ko yă yi tsutsa ba.
25 And he said Moses eat it this day for [is] a sabbath this day to Yahweh this day not you will find it in the field.
Musa ya ce, “Ku ci shi yau, saboda yau Asabbaci ne na Ubangiji. Ba za ku same shi a ƙasa a yau ba.
26 Six days you will gather it and on the day seventh a sabbath not it will be in it.
Kwana shida za ku tattara shi, amma a rana ta bakwai, Asabbaci, ba za a same shi ba.”
27 And it was on the day seventh they went out some of the people to gather [it] and not they found [it].
Duk da haka waɗansu mutane suka fita a ranar Asabbaci don su tattara, amma ba su sami kome ba.
28 And he said Yahweh to Moses until when? have you refused to keep commandments my and laws my.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Har yaushe za ku ƙi bin dokokina da umarnaina?
29 Consider that Yahweh he has given to you the sabbath there-fore he [is] giving to you on the day sixth bread of two days remain - everyone in place his may not him go out anyone from place his on the day seventh.
Ku lura fa, ai, Ubangiji ne ya ba ku Asabbaci; shi ya sa a kan ba ku burodi na kwana biyu, a rana ta shida. Kowa ya kamata yă kasance inda yake a rana ta bakwai; kada kowa yă fita.”
30 And they rested the people on the day seventh.
Sai mutanen suka huta a rana ta bakwai.
31 And they called [the] household of Israel name its manna and it [was] like [the] seed of coriander white and taste its [was] like a wafer with honey.
Mutanen Isra’ila suka kira burodin Manna. Manna yana nan fari kamar farin riɗi, ɗanɗanonsa kuma yana kama da masa da aka yi da zuma.
32 And he said Moses this [is] the word which he commands Yahweh [the] fullness of the omer of it [will be] for keeping to generations your so that - they may see the bread which I caused to eat you in the wilderness when brought out I you from [the] land of Egypt.
Musa ya ce, “Wannan shi ne abin da Ubangiji ya umarta, ‘Ku auna mudu guda na Manna, a adana ta dukan zamananku, domin kowane zamani yă ga irin abincin da na ba ku ku ci a hamada, yayinda na fitar da ku daga Masar.’”
33 And he said Moses to Aaron take a jar one and put there [the] fullness of the omer manna and deposit it before Yahweh for keeping to generations your.
Saboda haka Musa ya ce wa Haruna, “Ka ɗauki tulu, ka sa mudu guda na Manna a ciki. Sa’an nan ka sa shi a gaban Ubangiji, don a adana don tsararraki masu zuwa.”
34 Just as he had commanded Yahweh to Moses and he deposited it Aaron before the testimony for keeping.
Sai Haruna ya ajiye Mannar a gaban Akwatin Alkawari, don a adana ta kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa.
35 And [the] people of Israel they ate the manna forty year[s] until came they into a land inhabited the manna they ate until came they to [the] border of [the] land of Canaan.
Isra’ilawa suka yi shekaru arba’in suna cin Manna, har sai da suka shiga cikin ƙasar da take da mutane, suka ci Manna har zuwa kan iyakar ƙasar Kan’ana.
36 And the omer [is] [the] tenth [part] of the ephah it.
(Omer guda, daidai ne da kashi ɗaya bisa goma na Efa.)