< Esther 1 >
1 And it was in [the] days of Ahasuerus that Ahasuerus who reigned from India and to Cush seven and twenty and one hundred province[s].
Ga abin da ya faru a zamanin Zerzes. Zerzes ya yi mulki bisan larduna 127 daga Indiya zuwa Kush.
2 In the days those when sat - the king Ahasuerus on [the] throne of royalty his which [was] in Susa the citadel.
A lokacin nan, Sarki Zerzes ya yi mulki daga gadon sarauta, cikin mazaunin masarautar Shusha.
3 In year three of reigning his he made a feast for all officials his and servants his [the] army of - Persia and Media the nobles and [the] officials of the provinces [were] before him.
A shekara ta uku ta mulkinsa, ya yi wa dukan hakimansa da ma’aikatansa liyafa. Shugabannin mayaƙan Farisa, da Mediya, da yerimai; da kuma hakimai na lardunan suka kasance.
4 When showed he [the] wealth of [the] splendor of kingdom his and [the] honor of [the] glory of greatness his days many eighty and one hundred day[s].
Kwanaki 180 cif, ya nuna yawan dukiyar masarautarsa, da ɗaukakarta da kuma darajar girmansa.
5 And when were completed - the days these he made the king for all the people who were found in Susa the citadel from great and unto insignificant a feast seven days in [the] court of [the] garden of [the] palace of the king.
Sa’ad da waɗannan kwanaki suka wuce, sai sarki ya yi liyafa a cikin lambun da aka shinge na fadar sarki wadda ta ɗauki kwana bakwai wa dukan mutane daga ƙarami har zuwa babba, waɗanda suke zama a masarautar Shusha.
6 White material - cotton and violet material [was] held with cords of fine linen and purple on rods of silver and pillars of marble couches of - gold and silver on a pavement of porphyry and marble and mother-of-pearl and paving stone.
Lambun yana da fararen labulen da aka rataye da shunayya na lallausan lilin, da aka ɗaura da igiyoyin fararen lilin, da yadin jan garura, haɗe da zoban azurfa a kan ginshiƙin farin ƙasa. A nan, akwai kujeru na zinariya da na azurfa a kan daɓe mai ado da aka yi da duwatsu masu daraja, da farin ƙasa, da fararen duwatsun wuya, da waɗansu duwatsu masu tsada.
7 And they gave to drink in vessels of gold and vessels from vessels [were] differing and wine of royalty [was] much according to [the] hand of the king.
Aka rarraba ruwan inabi cikin kwaf na zinariya, kowanne kuwa dabam yake da ɗayan. Ruwan inabin kuwa yana da yawa, bisa ga wadatar sarki.
8 And the drinking [was] according to the law there not [was one who] compelled for thus - he had appointed the king on every chief of house his to do according to [the] pleasure of man and man.
Bisa ga umarnin sarki, aka bar kowane baƙo yă sha yadda ya ga dama, gama sarki ya umarci dukan bayin da suke rarraba ruwan inabin su ba wa kowa abin da yake so.
9 Also Vashti the queen she made a feast of women [the] house of royalty which [belonged] to the king Ahasuerus.
Sarauniya Bashti ita ma ta yi liyafa saboda mata a fadar Sarki Zerzes.
10 On the day seventh when was good [the] heart of the king by the wine he said to Mehuman Biztha Harbona Bigtha and Abagtha Zethar and Carcas [the] seven the eunuchs who served with [the] face of the king Ahasuerus.
A rana ta bakwai, sa’ad da Sarki Zerzes, ya yi tilis da ruwan inabi, sai ya umarci bābānni bakwai waɗanda suke yin masa hidima, wato, Mehuman, Bizta, Harbona, Bigta, Abagta, Zetar da Karkas,
11 To bring Vashti the queen before the king with a crown of royalty to show the peoples and the officials beauty her for [was] good of appearance she.
su kawo Sarauniya Bashti a gabansa, sanye da rawanin sarautarta, don ta nuna kyanta wa mutane da kuma hakimai, gama ita kyakkyawa ce ƙwarai.
12 And she refused the queen Vashti to come at [the] word of the king which [was] by [the] hand of the eunuchs and he was angry the king exceedingly and rage his it burned in him.
Amma da masu hidima suka ba da umarnin sarki, sai Sarauniya Bashti ta ƙi zuwa. Wannan ya ɓata wa sarki rai, ya kuma yi fushi ƙwarai.
13 And he said the king to wise men [who] knew the times for [was] thus [the] manner of the king before all [those who] knew law and judgment.
Da yake, al’ada ce sarki yă nemi shawara daga sanannu a batun doka da adalci, sai ya yi magana da masu hikima waɗanda suke fahimtar lokuta
14 And the [ones] close to him [were] Carshena Shethar Admatha Tarshish Meres Marsena Memucan [the] seven [the] officials of - Persia and Media [who] saw [the] face of the king who sat foremost in the kingdom.
suke kuma mafi kusa da sarki. Waɗannan masu hikima kuwa su ne, Karshena, Shetar, Admata, Tarshish, Meres, Marsena da kuma Memukan. Su hakimai bakwai ne na Farisa da Mediya waɗanda suke da dama ta musamman ta kaiwa ga sarki, suke kuma da matsayi mafi girma a masarautar.
15 According to [the] law what? [is] to do with the queen Vashti on - that not she did [the] command of the king Ahasuerus by [the] hand of the eunuchs.
Ya ce, “Bisa ga doka, me za a yi wa Sarauniya Bashti? Gama ta ƙi yin biyayya da umarnin sarki Zerzes da bābānni suka kai mata?”
16 And he said (Memucan *Q(k)*) before the king and the officials not on the king to only him she did wrong Vashti the queen for on all the officials and on all the peoples which [are] in all [the] provinces of the king Ahasuerus.
Sai Memukan ya amsa a gaban sarki da hakimai ya ce, “Sarauniya Bashti ta yi laifi, ba ga sarki kaɗai ba, amma ga dukan hakimai ma, da kuma mutanen dukan lardunan sarki Zerzes.
17 For it will go forth [the] matter of the queen to all the women to make despicable husbands their in view their because will say they the king Ahasuerus he said to bring Vashti the queen before him and not she came.
Domin halin Sarauniya zai zama sananne ga dukan mata, ta haka kuwa za su ƙasƙantar da mazansu su kuma ce, ‘Sarki Zerzes ya umarta a kawo Sarauniya Bashti a gabansa, amma ta ƙi zuwa.’
18 And the day this they will say - [the] noble ladies of Persia and Media who they have heard [the] matter of the queen to all [the] officials of the king and [will be] as enough of contempt and anger.
Wannan rana matan hakiman Farisa da na Mediya waɗanda suka ji game da halin sarauniya, za su yi haka wa dukan hakiman sarki. Zai zama babu ƙarshen rashin bangirma da kuma reni.
19 If [is] on the king good let it go forth a word of royalty from to before him and let it be written in [the] laws of Persia and Media and not it will pass away that not she will come Vashti before the king Ahasuerus and queenhood her let him give the king to fellow woman her good more than she.
“Saboda haka, in ya gamshi sarki, bari yă ba da hatimi na sarauta, bari kuma a rubuta shi cikin dokokin Farisa da Mediya, wanda ba za a iya sokewa ba, cewa Bashti ba za tă ƙara zuwa gaban sarkin Zerzes ba. Bari kuma sarki yă ba da matsayinta na sarauta ga wata, wadda ta fi ta.
20 And it will be heard [the] decree of the king which he will make in all kingdom his for [is] great it and all the women they will give honor to husbands their from great and unto insignificant.
Ta haka, sa’ad da aka yi shelar dokar sarki ko’ina a fāɗin masarautarsa, dukan mata za su ba wa mazansu girma, daga ƙarami har zuwa babba.”
21 And it was good the word in [the] eyes of the king and the officials and he did the king according to [the] word of Memucan.
Sarki da hakimansa suka gamsu da wannan shawara. Saboda haka sarki ya yi kamar yadda Memukan ya faɗa.
22 And he sent out documents to all [the] provinces of the king to province and province according to writing its and to people and people according to language its to be every man ruler in own household his and speaking according to [the] language of people his.
Ya aika da saƙo zuwa ga dukan ɓangarorin masarautar, zuwa ga kowane lardi a irin nasa rubutu, zuwa kuma ga kowane mutane a nasu harshe, ana shelar a kowane yare na mutane, cewa kowane mutum yă zama mai mulki bisa gidansa.