< Deuteronomy 8 >

1 All the commandment which I [am] commanding you this day you will take care! to observe so that you may live! and you will increase and you will go and you will take possession of the land which he swore Yahweh to ancestors your.
Ku hankali, ku bi kowane umarnin da nake ba ku a yau, saboda ku rayu, ku ƙaru, ku kuma shiga, ku mallaki ƙasar da Ubangiji ya alkawarta da rantsuwa ga kakanninku.
2 And you will remember all the way which he led you Yahweh God your this forty year[s] in the wilderness so as to humble you to put to [the] test you to know [that] which [was] in heart your ¿ will you keep (commandments his *Q(K)*) or? not.
Ku tuna yadda Ubangiji Allahnku ya bishe ku a dukan hanya, a cikin hamada waɗannan shekaru arba’in, don yă ƙasƙantar da ku, yă kuma gwada ku don yă san abin da yake a zuciyarku, ko za ku kiyaye umarnansa, ko babu.
3 And he humbled you and he caused to hunger you and he caused to eat you (*L(abh)*) the manna which not you had known and not they had known! ancestors your so as to make know you that not on the bread by only it he lives humankind for on every utterance of [the] mouth of Yahweh he lives humankind.
Ya ƙasƙantar da ku, ya bar ku da yunwa, sa’an nan ya ciyar da ku da Manna, wadda ku, ko kakanninku, ba su sani ba, ta haka ne ya sa kuka sani cewa, ba da abinci kaɗai mutum zai rayu ba, amma ta wurin kowace kalmar da ta fito daga bakin Ubangiji.
4 Clothing your not it wore out from on you and foot your not it swelled this forty year[s].
Tufafinku ba su yayyage ba, ƙafafunku kuma ba su kumbura ba a waɗannan shekaru arba’in.
5 And you will know with heart your that just as he disciplines everyone child his Yahweh God your [is] disciplining you.
Sai ku sani fa a cikin zuciyarku cewa kamar yadda mutum kan horar da ɗansa, haka Ubangiji Allahnku ke horar da ku.
6 And you will keep [the] commandments of Yahweh God your by walking in ways his and by fearing him.
Ku kiyaye umarnan Ubangiji Allahnku, kuna tafiya cikin hanyoyinsa, kuna kuma girmama shi.
7 For Yahweh God your [will] bring you into a land good a land of torrents of water springs and deeps [which] go forth in the valley and on the mountain.
Gama Ubangiji Allahnku yana fitar da ku zuwa cikin ƙasa mai kyau, ƙasa mai rafuffuka da tafkunan ruwa, tare da maɓulɓulai masu gudu a kwari da tuddai;
8 A land of wheat and barley and vine and fig tree and pomegranate a land of olive tree of oil and honey.
ƙasa mai alkama da sha’ir, inabi da ɓaure, rumman, man zaitun da zuma;
9 A land which not in scarcity you will eat in it food not you will lack anything in it a land which stones its [are] iron and from hills its you will dig copper.
ƙasa inda abinci ba zai yi ƙaranci ba, ba kuma za ku rasa kome ba; ƙasa ce inda ƙarfe ne duwatsunta, ana kuma haƙar tagulla a tuddanta.
10 And you will eat and you will be satisfied and you will bless Yahweh God your on the land good which he has given to you.
Sa’ad da kuka ci, kuka ƙoshi, sai ku yabi Ubangiji Allahnku saboda ƙasa mai kyau da ya ba ku.
11 Take heed to yourself lest you should forget Yahweh God your to not to keep commandments his and judgments his and statutes his which I [am] commanding you this day.
Ku yi hankali cewa ba ku manta da Ubangiji Allahnku, har ku kāsa kiyaye umarnansa, dokokinsa da ƙa’idodinsa da nake ba ku a wannan rana ba.
12 Lest you should eat and you will be satisfied and houses good you will build and you will dwell.
To, sa’ad da kuka ci, kuka ƙoshi, sa’ad da kuka gina gidaje masu kyau, kuka zauna,
13 And herd your and flock your they will increase! and silver and gold it will increase of you and all that [belongs] to you it will increase.
sa’ad da kuma garkunanku na shanu da na tumaki suka ƙaru, azurfanku da zinariyarku kuma suka ƙaru, sa’an nan dukan abin da kuke da shi ya haɓaka,
14 And it will be lifted up heart your and you will forget Yahweh God your who brought out you from [the] land of Egypt from a house of slaves.
to, sai ku lura, kada ku ɗaukaka kanku, har ku manta da Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar, daga ƙasar bauta kuma.
15 Who led you in the wilderness - great and awesome snake - fiery and scorpion and thirsty ground where there not [was] water who brought forth for you water from [the] rock of flint.
Ya bishe ku cikin hamada mai fāɗi, mai bantsoro, wannan busasshiyar ƙasa wadda ba ta da ruwa, ga macizai masu dafi da kuma kunamai. Ya ba ku ruwa daga dutsen ƙanƙara.
16 Who caused to eat you manna in the wilderness which not they had known! ancestors your so as to humble you and so as to put to [the] test you to do good to you in end your.
Ya ba ku Manna don ku ci a cikin hamada, wani abin da kakanninku ba su taɓa sani ba, don yă ƙasƙantar yă kuma gwada ku, saboda yă yi muku alheri daga baya.
17 And you will say in heart your strength my and [the] might of hand my it has acquired for me the wealth this.
Wataƙila ku ce wa kanku, “Ikona da ƙarfin hannuwana ne suka ba ni da wannan arziki.”
18 And you will remember Yahweh God your that he [is] the [one who] gives to you strength to acquire wealth so as to carry out covenant his which he swore to ancestors your as the day this.
Amma ku tuna da Ubangiji Allahnku, gama shi ne wanda yake ba ku azanci na yin arziki, ta haka kuwa ya tabbatar da alkawarinsa, wanda ya rantse wa kakanninku, kamar yadda yake a yau.
19 And it will be certainly [if] you will forget Yahweh God your and you will walk after gods other and you will serve them and you will bow down to them I testify against you this day that certainly you will perish!
In kuka manta da Ubangiji Allahnku, kuka kuma bi waɗansu alloli, kuka yi musu sujada, kuka kuma rusuna musu, to, a yau ina gargaɗe ku cewa tabbatacce za a hallaka ku.
20 Like the nations which Yahweh [is] about to destroy from before you so you will perish! consequence not you will listen! to [the] voice of Yahweh God your.
Kamar al’ummai da Ubangiji ya hallakar kafin ku, haka zai hallaka ku, domin ba ku yi biyayya da muryar Ubangiji Allahnku ba.

< Deuteronomy 8 >