< Deuteronomy 3 >
1 And we turned and we went up [the] way of Bashan and he came forth Og [the] king of Bashan to meet us he and all people his for battle Edrei.
Biye da wannan muka juya muka haura ta hanyar wajen Bashan, inda Og, sarkin Bashan tare da dukan mayaƙansa suka fito don su sadu da mu a yaƙi, a Edireyi.
2 And he said Yahweh to me may not you fear him for in hand your I give him and all people his and land his and you will do to him just as you did to Sihon [the] king of the Amorite[s] who [was] dwelling in Heshbon.
Ubangiji ya ce mini, “Kada ka ji tsoronsa, gama na riga na miƙa shi da dukan mayaƙansa da kuma ƙasarsa gare ka. Yi masa abin da ka yi wa Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulkin Heshbon.”
3 And he gave Yahweh God our in hand our also Og [the] king of Bashan and all people his and we struck down him until not he had left to him a survivor.
Saboda haka Ubangiji Allahnmu ya ba da Og, sarkin Bashan da dukan mayaƙansa a hannuwanmu. Muka karkashe su, ba mu bar wani da rai ba.
4 And we captured all cities his at the time that not it was a town which not we took from with them sixty citi[es] all [the] region of Argob [the] kingdom of Og in Bashan.
A wannan lokaci muka kwashe dukan biranensa. Babu ɗaya daga birane sittin da ba mu ɗauke daga gare su ba, dukan yankin Argob, masarautar Og a Bashan.
5 All these [were] cities fortified wall high gates and bar[s] apart from [the] cities of the hamlet-dweller[s] many very.
Dukan biranen nan masu katanga da suke da tsayi masu ƙofofi da ƙyamare, akwai kuma manya ƙauyukan da ba su da katanga.
6 And we totally destroyed them just as we had done to Sihon [the] king of Heshbon we totally destroyed every city of men the women and the little one[s].
Muka hallaka su ƙaƙaf, kamar yadda muka yi wa Sihon sarkin Heshbon, muka hallaka kowace birni, maza, mata da yara.
7 And all the livestock and [the] booty of the cities we plundered for ourselves.
Amma dukan dabbobin da kuma ganimar daga biranensu muka kwaso wa kanmu.
8 And we took at the time that the land from [the] hand of [the] two [the] kings of the Amorite[s] who [were] on [the] other side of the Jordan from [the] wadi of Arnon to [the] mountain of Hermon.
A lokacin ne muka ƙwace wannan ƙasa daga hannun sarakunan nan biyu na Amoriyawa, wato, ƙasa wadda take a hayin Urdun, daga Kwarin Arnon zuwa Dutsen Hermon.
9 [the] Sidonians They call Hermon Sirion and the Amorite[s] they call it Senir.
(Hermon ne Sidoniyawa suke kira Siriyon, Amoriyawa kuwa suna kira shi Senir.)
10 All - [the] cities of the plain and all Gilead and all Bashan to Salecah and Edrei [the] cities of [the] kingdom of Og in Bashan.
Muka kama dukan biranen da suke kan tudu, da dukan Gileyad, da dukan Bashan, har zuwa Saleka da Edireyi, biranen masarautar Og a Bashan.
11 For only Og [the] king of Bashan he survived from [the] remnant of the Rephaites there! sarcophagus his [was] a sarcophagus of iron ¿ not [is] it in Rabbah of [the] people of Ammon [was] nine cubits length its and [was] four cubits breadth its by a cubit of a human.
(Og sarkin Bashan, ne kaɗai ya ragu cikin Refahiyawa. An yi gadonsa da ƙarfe, tsawon gadon ya fi ƙafa goma sha uku, fāɗinsa kuwa ƙafa shida ne. Yana nan a Rabba ta Ammonawa har yanzu.)
12 And the land this we took possession of at the time that from Aroer which [was] at [the] wadi of Arnon and [the] half of [the] hill country of Gilead and cities its I gave to the Reubenite[s] and to the Gadite[s].
Cikin ƙasar da muka kwasa a lokacin, na ba wa mutanen Ruben da mutanen Gad yankin arewa na Arower ta Kwarin Arnon, haɗe da rabin ƙasar tudu ta Gileyad, tare da biranenta.
13 And [the] remainder of Gilead and all Bashan [the] kingdom of Og I gave to [the] half of [the] tribe of Manasseh all [the] region of Argob to all Bashan it it was called [the] land of [the] Rephaites.
Sai kuma na ba wa rabin kabilar Manasse sauran rabin ƙasar tudu ta Gileyad da kuma dukan Bashan, masarautar Og (Wato, dukan yankin ƙasan nan na Argob a Bashan da dā ake kira ƙasar Refahiyawa.
14 Jair [the] son of Manasseh he took all [the] region of Argob to [the] border of the Geshurite[s] and the Maacathite[s] and he called them on own name his Bashan [the] villages of Jair until the day this.
Yayir na zuriyar Manasse ya karɓi dukan yankin ƙasar Argob a Bashan har zuwa iyakar Geshurawa da Ma’akatiyawa. Sai ya kira ƙauyukan wurin da sunansa, Hawwot Yayir.)
15 And to Makir I gave Gilead.
Na kuma ba da Gileyad ga Makir.
16 And to the Reubenite[s] and to the Gadite[s] I gave from Gilead and to [the] wadi of Arnon [the] middle of the wadi and a border and to Jabbok the wadi [is] [the] border of [the] people of Ammon.
Amma ga mutanen Ruben da mutanen Gad, na ba da yankin da ya tashi daga Gileyad, ya gangara zuwa Kwarin Arnon (tsakiyar kwarin kuwa shi ne iyaka) ya fita zuwa Kogin Yabbok, wanda yake shi ne iyakar Ammonawa.
17 And the Arabah and the Jordan and a border from Kinnereth and to [the] sea of the Arabah [the] Sea of Salt under [the] slopes of Pisgah east-ward.
Iyakarsa daga yamma kuwa shi ne Urdun a Araba, daga Kinneret zuwa Tekun Araba (wato, Tekun Gishiri) a gangaren gindin Dutsen Fisga wajen gabas.
18 And I commanded you at the time that saying Yahweh God your he has given to you the land this to take possession of it equipped you will pass over before countrymen your [the] people of Israel O all [the] sons of strength.
Na umarce ku a lokacin na ce, “Ubangiji Allahnku ya ba ku wannan ƙasa ku mallake ta. Dukan mayaƙanku za su haye da shirin yaƙi a gaban’yan’uwanku, Isra’ilawa.
19 Only wives your and little one[s] your and livestock your I know that livestock much [belongs] to you they will remain in cities your which I have given to you.
Amma matanku, yaranku da dabbobinku (na sani kuna da dabbobi masu yawa), su ne za ku bari a garuruwan da na ba ku,
20 Until that he will give rest Yahweh - to countrymen your like you and they will take possession of also they the land which Yahweh God your [is] about to give to them on [the] other side of the Jordan and you will return everyone to possession his which I have given to you.
sai Ubangiji ya ba da hutu ga sauran’yan’uwanku, yadda ya yi da ku, su ma suka sami ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba su, a ƙetaren Urdun, sa’an nan kowannenku zai komo ga mallakar da na ba ku.”
21 And Joshua I commanded at the time that saying eyes your [are] the [ones which] have seen all that he did Yahweh God your to [the] two the kings these thus he will do Yahweh to all the kingdoms where you [are] about to pass over there.
A lokacin nan na umarci Yoshuwa na ce, “Da idanunka ka ga dukan abin da Ubangiji Allahnku ya yi da waɗannan sarakuna biyu. Haka Ubangiji zai yi da dukan masarautai a can, inda za ku.
22 Not you must fear them for Yahweh God your he [is] the [one who] will fight for you.
Kada ku ji tsoronsu, gama Ubangiji Allahnku zai yi yaƙi dominku.”
23 And I sought favor to Yahweh at the time that saying.
A lokacin, na roƙi Ubangiji na ce,
24 O Lord Yahweh you you have begun to show servant your greatness your and hand your strong that who? [is] God in the heavens and on the earth who he will do like works your and like mighty deeds your.
“Ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka fara nuna wa bawanka ɗaukakarka da ikonka. Akwai wani allah a sama ko a duniya, wanda zai aikata waɗannan manyan ayyukan kamar ka?
25 Let me pass over please so I may see the land good which [is] on [the] other side of the Jordan the hill country good this and Lebanon.
Ina roƙonka, bari in ƙetare in ga ƙasa mai kyau ɗin nan a ƙetaren Urdun, wannan ƙasar mai kyau ta tuddai, da kuma Lebanon.”
26 And he was furious Yahweh with me on account of you and not he listened to me and he said Yahweh to me enough for you may not you repeat to speak to me again in the matter this.
Amma saboda ku, Ubangiji ya yi fushi da ni, bai kuwa saurare ni ba. Sai Ubangiji ya ce, “Ya isa haka, kada ka ƙara yin magana da ni game da wannan batu.
27 Go up - [the] top of Pisgah and lift up eyes your west-ward and north-ward and south-ward and east-ward and see with own eyes your that not you will pass over the Jordan this.
Haura zuwa ƙwanƙolin Fisga, ka dubi ƙasar da idanunka daga kowane gefe, yamma, da arewa, da kudu, da kuma gabas, gama ba za ka ƙetare wannan Urdun ba.
28 And commission Joshua and encourage him and strengthen him for he he will pass over before the people this and he he will give as an inheritance them the land which you will see.
Amma ka umarci Yoshuwa, ka ƙarfafa shi, ka kuma ba shi ƙarfin gwiwa, gama shi ne zai jagoranci wannan mutane su haye, yă kuma ba su gādon ƙasar da za ka gani.”
29 And we remained in the valley opposite to Beth Peor.
Sai muka zauna a kwari kusa da Bet-Feyor.