< Deuteronomy 24 >

1 If he will take a man a woman and he will marry her and it will be if not she will find favor in view his for he has found in her [the] nakedness of a thing and he will write for her a document of divorce and he will give [it] in hand her and he will send away her from house his.
Idan mutum ya auri mata, daga baya ba tă gamshe shi ba domin ya gano wani abu marar kyau game da ita, ya ba ta takardar saki, ya kuma kore ta daga gidansa,
2 And she will go out from house his and she will go and she will belong to a man another.
in bayan ta bar gidansa ta zama matar wani dabam,
3 And he will hate her the man latter and he will write for her a document of divorce and he will give [it] in hand her and he will send away her from house his or if he will die the man latter who he has taken her for himself to a wife.
sai mijinta na biyu ya ƙi ta, ya ba ta takardan saki, ya kore ta daga gidansa, ko kuwa ya mutu,
4 Not he will be able husband her former who he sent away her to return to take her to become of him wife after that she has been declared unclean for [is] an abomination that before Yahweh and not you will cause to sin the land which Yahweh God your [is] about to give to you an inheritance.
to, kada mijinta na farko, wanda ya sake ta yă sāke aurenta, tun da yake ta ƙazantu. Wannan zai zama abin ƙyama a gaban Ubangiji. Kada ku kawo zunubi a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo.
5 If he will take man a wife new not he will go out with the army and not it will pass on him to any thing free he will be to house his a year one and he will cause to rejoice wife his whom he has taken.
In mutum bai daɗe da aure ba, kada a sa yă je yaƙi, ko yă yi wani aiki. Gama zai huta shekara guda a gida, yă faranta wa matar da ya aura rai.
6 Not anyone will take as pledge a hand-mill and an upper millstone for a life that [is] taking as pledge.
Kada ku karɓi jinginar dutsen niƙa tare da ɗan dutsen niƙan, domin yin haka zai zama karɓar jinginar rai ne.
7 If he will be found anyone stealing a person any of countrymen his any of [the] people of Israel and he will treat as a slave him and he will sell him and he will die the thief that and you will remove the evil from midst your.
Idan aka kama wani yana satar ɗan’uwansa mutumin Isra’ila domin yă sa ya zama bawansa, ko yă sayar da shi, sai a kashe ɓarawon nan. Haka za ku kawar da mugunta daga cikinku.
8 Take heed to [the] plague of serious skin disease to take care exceedingly and to do according to all that they will instruct you the priests the Levites just as I commanded them you will take care to do.
Game da cututtukan kuturta, sai ku lura, ku yi yadda firistocin da suke Lawiyawa suka umarce ku. Dole ku lura ku bi abin da na umarce su.
9 Remember [that] which he did Yahweh God your to Miriam on the way when came out you from Egypt.
Ku tuna da abin da Ubangiji Allahnku ya yi wa Miriyam a hanya, bayan kun fito Masar.
10 If you will lend to neighbor your a loan of anything not you will go into house his to take as pledge pledge his.
Sa’ad da kuka ba da rance na kowane iri ga maƙwabcinku, kada ku shiga gidansa don karɓar wani abu a matsayin jingina.
11 On the outside you will stand and the person whom you [are] lending to him he will bring out to you the pledge the outside towards.
Ku tsaya a waje ku bar mutumin da yake karɓan rancen yă kawo muku abin da zai bayar a matsayin jingina.
12 And if [is] a person poor he not you will lie down in pledge his.
In matalauci ne, kada ku kwana da abin da zai bayar a matsayin jingina a wurinku.
13 Certainly you will return to him the pledge when goes the sun and he will lie down in garment his and he will bless you and to you it will belong righteousness before Yahweh God your.
Ku mayar da rigarsa a fāɗuwar rana saboda yă sami abin rufuwa. Yin haka zai sa yă gode muku, za a kuma ɗauka wannan a matsayin aikin adalci da kuka yi a gaban Ubangiji Allahnku.
14 Not you must oppress a hired laborer poor and needy one of countrymen your or one of sojourner[s] your who [is] in land your in gates your.
Kada ku zalunci ɗan ƙodago matalauci da mabukaci, ko da shi ɗan’uwanku ne mutumin Isra’ila, ko baƙon da yake zama a cikin garuruwanku.
15 On day its you will pay wage[s] his and not it will go on him the sun for [is] poor he and to it he [is] lifting up desire his and not he will call out on you to Yahweh and it will be on you sin.
Ku biya kuɗin aikinsa kowace rana kafin fāɗuwar rana, domin shi matalauci ne, yana kuma sa rai a kan wannan hakkin ne, don kada ya yi wa Ubangiji kuka a kanku, har yă zama laifi a gare ku.
16 Not they will be put to death parents on children and children not they will be put to death on parents (anyone *L(abh)*) for own sin his they will be put to death.
Ba za a kashe iyaye a maimakon’ya’yansu ba, ba kuwa za a kashe’ya’ya a maimakon iyayensu ba; kowa ya yi zunubi, shi za a kashe.
17 Not you will turn aside [the] justice of a sojourner a fatherless one and not you will take as pledge [the] garment of a widow.
Ba za ku danne hakkin baƙon da yake zama a cikinku ko na marayu ba, ba za ku ɗauki rigar matar da mijinta ya mutu a matsayin jingina ba.
18 And you will remember that a slave you were in Egypt and he redeemed you Yahweh God your from there there-fore I [am] commanding you to do the thing this.
Ku tuna dā ku bayi ne a Masar, Ubangiji Allahnku kuwa ya fisshe daga can. Shi ya sa na umarce ku ku yi wannan.
19 If you will harvest harvest your in field your and you will forget a sheaf in the field not you will return to fetch it to the sojourner to the fatherless one and to the widow it will belong so that he may bless you Yahweh God your in all [the] work of hands your.
Sa’ad da kuke girbi a gonarku, sai kuka manta da dami, kada ku koma don ku ɗauka. Ku bar shi don baƙo, maraya da kuma gwauruwa, saboda Ubangiji Allahnku yă albarkace ku a cikin dukan aikin hannuwanku.
20 If you will beat olive tree your not you will go over [the] boughs behind you to the sojourner to the fatherless one and to the widow it will belong.
Sa’ad da kuka kakkaɓe’ya’yan zaitun daga itatuwanku, kada ku yi kalan abin da ya rage. Ku bar shi don baƙo, maraya da kuma gwauruwa.
21 For you will gather grapes vineyard your not you will glean behind you to the sojourner to the fatherless one and to the widow it will belong.
Sa’ad da kuka yi girbin inabi a gonar inabinku, kada ku yi kalan abin da ya rage. Ku bar shi don baƙo, maraya da kuma gwauruwa.
22 And you will remember that a slave you were in [the] land of Egypt there-fore I [am] commanding you to do the thing this.
Ku tuna dā ku bayi ne Masar. Shi ya sa na umarce ku ku yi wannan.

< Deuteronomy 24 >