< Deuteronomy 21 >
1 If it will be found [one] slain in the land which Yahweh God your [is] about to give to you to take possession of it lying in the open country not it is known who? did he strike him.
In aka sami an kashe mutum kwance a fili, a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku ku mallaka, ba a kuma san wanda ya kashe shi ba,
2 And they will go out elders your and judges your and they will measure to the cities which [are] around the [one] slain.
sai dattawanku da alƙalanku su je su gwada nisan wurin da gawar take zuwa garuruwan da suke maƙwabtaka.
3 And it will be the city near to the [one] slain and they will take [the] elders of the city that a heifer of [the] herd which not it has been worked by it which not it has dragged by a yoke.
Sai dattawan garin da suke kurkusa da gawar su ɗauki karsanar da ba a taɓa yin aiki da ita ba, ba a kuma taɓa sa mata karkiya ba,
4 And they will bring down [the] elders of the city that the heifer to a wadi ever-flowing which not it is tilled in it and not it is sown and they will break [the] neck of there the heifer in the wadi.
a gangara da ita kwarin da ba a taɓa nome, ko shuki a ciki ba, inda kuma akwai rafi mai gudu, a can cikin kwarin za su karye wuyanta.
5 And they will draw near the priests [the] sons of Levi for them he has chosen Yahweh God your to serve him and to bless in [the] name of Yahweh and on mouth their it will be every dispute and every wound.
Firistoci,’ya’yan Lawi maza, za su fito, gama Ubangiji Allahnku ya zaɓe su su yi masa hidima, su kuma furta albarku a cikin sunan Ubangiji, za su kuma daidaita duk rigimar cin mutunci.
6 And all [the] elders of the city that near to the [one] slain they will wash hands their over the heifer broken necked in the wadi.
Sa’an nan dukan dattawan garin da yake kurkusa da gawar za su wanke hannuwansu a bisa karsanan da aka karye wuyar a kwarin,
7 And they will answer and they will say hands our not (they shed *Q(K)*) the blood this and eyes our not they saw.
za su kuma furta, “Hannuwanmu ba su zub da wannan jini ba, idanunmu kuma ba su ga an yi haka ba.
8 Make atonement for people your Israel which you ransomed O Yahweh and may not you put blood innocent in [the] midst of people your Israel and it will be atoned for for them the blood.
Karɓi wannan kafara saboda mutanenka Isra’ila, wanda ka fansar, ya Ubangiji, kada kuma ka ɗaura wa mutanenka alhakin jinin mutumin nan marar laifi.” Za a kuwa yi kafarar zub da jinin da aka yi.
9 And you you will remove the blood innocent from midst your for you will do the right in [the] eyes of Yahweh.
Ta haka za ku fid da laifin zub da jinin marar laifi daga cikinku, da yake kun yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji.
10 If you will go out to war on enemies your and he will give him Yahweh God your in hand your and you will take captive captive[s] his.
Sa’ad da kuka tafi yaƙi da abokan gābanku, sai Ubangiji Allahnku ya bashe su a hannuwanku kuka kuma kama su a matsayin bayi,
11 And you will see among the [female] captive[s] a woman beautiful of appearance and you will love her and you will take [her] for yourself to a wife.
in ka ga wata kyakkyawar mace wadda ta ɗauki hankalinka a cikin bayin, za ka iya aure ta tă zama matarka.
12 And you will bring her into [the] middle of house your and she will shave head her and she will attend to finger-nails her.
Ka kawo ta gidanka ka sa tă aske kanta, tă yanka kumbanta
13 And she will remove [the] clothing of captivity her from on her and she will dwell in house your and she will weep for father her and mother her a month of days and after thus you will go into her and you will be husband her and she will become of you a wife.
tă kuma tuɓe tufafin da ta sa sa’ad da aka kama ta. Bayan ta zauna a gidanka ta kuma yi makokin mahaifinta da mahaifiyarta wata ɗaya cif, sai ka shiga wurinta ka zama mijinta, za tă kuwa zama matarka.
14 And it will be if not you delight in her and you will let go her for self her and certainly not you will sell her for money not you will treat as a slave her because that you have humiliated her.
In ba ka jin daɗinta, ka bar tă tafi inda take so. Ba za ka sayar da ita ko ka yi da ita kamar baiwa ba, da yake ka ƙasƙantar da ita.
15 If they will belong to a man two wives the one [is] loved and the one [is] hated and they will bear to him sons the loved [one] and the hated [one] and he will belong the son the firstborn to the hated [wife].
In mutum yana da mata biyu, yana kuwa ƙaunar ɗaya, ba ya kuma ƙaunar ɗayan, su biyun kuwa suka haifi masa’ya’ya maza, sai ya zamana cewa ɗan farin ya kasance na wadda ba ya ƙauna,
16 And it will be on [the] day causes to inherit he sons his [that] which it will belong to him not he will be able to treat as firstborn [the] son the loved [one] on [the] face of [the] son of the hated [one] the firstborn.
to, a ranar da zai yi faɗa wane ne a cikin’ya’yansa zai riƙe gādon da zai bar musu, kada yă sa ɗan matar da yake ƙauna yă zama kamar shi ne ɗan fari, a maimakon ɗan matar da ba ya ƙauna, wanda shi ne ɗan farin.
17 That the firstborn [the] son of the hated [one] he will acknowledge by giving to him a mouth of two in all that it will be found to him for he [is] [the] beginning of manly vigor his [belongs] to him [the] claim of the birthright.
Dole yă yarda cewa ɗan matar da ba ya ƙaunar ne ɗan fari, ta wurin ba shi rabo kashi biyu na dukan abin da yake da shi, gama shi ne mafarin ƙarfinsa, yana da hakkin ɗan fari.
18 If he will belong to anyone a son stubborn and rebellious not he [is] listening to [the] voice of father his and to [the] voice of mother his (and they will discipline *L(abh)*) him and not he will listen to them.
In mutum yana da gagararren ɗa mai tawaye, wanda ba ya biyayya ga mahaifinsa da mahaifiyarsa, ba ya kuma jin su sa’ad da suke horonsa,
19 And they will seize him father his and mother his and they will bring out him to [the] elders of city his and to [the] gate of place his.
mahaifinsa da mahaifiyarsa za su kama shi su kawo shi ga dattawa a ƙofar garinsu.
20 And they will say to [the] elders of city his son our this [is] stubborn and rebellious not he [is] listening to voice our a glutton and a drunkard.
Za su ce wa dattawan, “Wannan ɗanmu gagararre ne, mai tawaye. Ba ya mana biyayya. Mai zari ne, kuma mashayi.”
21 And they will stone him all [the] men of city his with stones and he will die and you will remove the evil from midst your and all Israel they will hear and they may fear.
Sa’an nan dukan mazan garinsa za su jajjefe shi har yă mutu. Dole ku fid da mugu daga cikinku. Dukan Isra’ila kuwa za su ji wannan su kuma ji tsoro.
22 And if it will be in anyone a sin of a sentence of death and he will be put to death and you will hang him on a tree.
In mutum ya yi laifin da ya isa kisa, aka kuwa rataye shi a itace,
23 Not it will remain overnight corpse his on the tree for certainly you will bury him on the day that for [is] a curse of God [one who] is hanged and not you will make unclean land your which Yahweh God your [is] about to give to you an inheritance.
kada ku bar jikinsa a kan itacen yă kwana. Ku tabbata kun binne shi a ranar, domin duk wanda aka rataye a kan itace la’ananne ne ga Allah. Kada ku ƙazantar da ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo.