< Daniel 10 >
1 In year three of Cyrus [the] king of Persia a word it was revealed to Daniel whom it had been called name his Belteshazzar and [was] truth the word and a war great and he understood the word and understanding [belonged] to him by the vision.
A shekara ta uku ta Sairus sarkin Farisa, sai aka ba wa Daniyel (wanda ake kira Belteshazar) wahayi. Saƙon kuwa gaskiya ce wadda take tattare da babban yaƙi. Fahimtar saƙon ya zo masa a cikin wahayi.
2 In the days those I Daniel I was mourning three sevens days.
A wannan lokaci ni Daniyel na yi makoki har na sati uku.
3 Food of desirableness not I ate and meat and wine not it came into mouth my and indeed not I anointed myself until were completed three sevens days.
Ban ci abinci mai kyau ba; ba nama ko ruwa inabin da ya shiga bakina; kuma ba na amfani da man shafawa gaba ɗaya har sai da sati nan uku suka wuce.
4 And on day twenty and four of the month first and I I was on [the] side of the river great that [is] [the] Tigris.
A rana ta ashirin da huɗu ga watan farko, a sa’ad da nake tsaye a bakin babban kogi, Tigris,
5 And I lifted up eyes my and I saw and there! a man one clothed linen and loins his [were] girded with [the] gold of Uphaz.
na ɗaga kaina na duba sai ga wani mutum tsaye sanye da rigar lilin, ya yi ɗamara da zinariya zalla daga Ufaz kewaye da ƙugunsa.
6 And body his [was] like topaz and face his [was] like [the] appearance of lightning and eyes his [were] like torches of fire and arms his and feet his [were] like [the] appearance of bronze burnished and [the] sound of words his [was] like [the] sound of a multitude.
Jikinsa kamar lu’ulu’u yake, fuskarsa kuma kamar walƙiya, idanunsa kamar harshen wuta, hannuwansa da ƙafafunsa kamar gogaggiyar tagulla, muryarsa kuma kamar amon babban taron jama’a.
7 And I saw I Daniel to alone me the vision and the men who they were with me not they saw the vision but terror great it fell on them and they fled in hiding themselves.
Ni, Daniyel, kaɗai ne na ga wahayin; mutanen da suke tare da ni ba su gani ba, amma wata irin babbar razana ta auko musu har suka gudu suka ɓuya.
8 And I I was left behind to alone me and I saw the vision great this and not it remained in me strength and vigor my it was changed on me into destruction and not I retained strength.
Sai aka bar ni ni kaɗai, ina juyayi wannan babban wahayi, ba ni da sauran ƙarfi, fuskata ta yamutse kuma ba ni da sauran ƙarfi.
9 And I heard [the] sound of words his and just as heard I [the] sound of words his and I I was dazed on face my and face my [was] ground towards.
Sai na ji yana magana, da ina sauraronsa, sai na shiga barci mai nauyi, na kuwa fāɗi rubda ciki.
10 And there! a hand it touched me and it shook me on knees my and [the] palms of hands my.
Sai hannu ya taɓa ni ya sa makyarkyata a hannuna da ƙafafuna.
11 And he said to me O Daniel man of preciousness understand the words which I [am] about to speak to you and stand on standing place your for now I have been sent to you and when spoke he with me the word this I stood up trembling.
Sai ya ce, “Daniyel, kai ne wanda ake ƙauna sosai, ka yi lura da kyau game da kalmomin da zan yi maka magana a kansu, ka tashi yanzu, gama an aiko ni a gare ka.” Sa’ad da ya faɗa mini haka, sai na tashi a tsaye ina rawan jiki.
12 And he said to me may not you fear O Daniel for - from the day first which you gave heart your to understand and to humble yourself before God your they were heard words your and I I have come on words your.
Sai ya ci gaba da cewa, “Kada ka ji tsoro, Daniyel. Gama tun daga ran da ka fara sa zuciya ga neman ganewa, ka kuma ƙasƙantar da kanka a gaban Allahnka, an ji addu’arka, amsar addu’arka ce ta kawo ni.
13 And [the] prince of - [the] kingdom of Persia [was] standing to before me twenty and one day[s] and there! Michael one of the princes chief he came to help me and I I remained behind there beside [the] kings of Persia.
Amma mai mulkin masarautar Farisa ya tsare ni har kwana ashirin da ɗaya. Sai da Mika’ilu, ɗaya daga cikin manya shugabanni, ya zo ya taimake ni, saboda an tsare ni a can tare da sarkin Farisa.
14 And I have come to make understand you [that] which it will happen to people your at [the] end of the days for still [the] vision [is] for the days.
Yanzu na zo domin in bayyana maka abin da zai faru da mutanenka nan gaba, gama wahayin ya shafi lokacin da bai riga ya zo ba ne.”
15 And when spoke he with me according to the words these I put face my [the] ground towards and I was dumb.
Yayinda yake faɗin mini haka, sai na sunkuyar da kaina ƙasa shiru, ba magana.
16 And there! like [the] likeness of [the] sons of humankind [was] touching lips my and I opened mouth my and I spoke! and I said! to the [one] standing to before me O lord my on the vision they have turned pangs my on me and not I have retained strength.
Sai wani wanda ya yi kama da mutum ya taɓa leɓunana, na kuma buɗe bakina sai na fara magana. Na ce wa wannan da yake tsaye a gabana, “Na cika da azaba saboda wannan wahayi, ranka yă daɗe, ina kuma neman taimako.
17 And how? is he able [the] servant of lord my this to speak with lord my this and I from now not it remains in me strength and breath not it is left in me.
Yaya ni bawanka zan iya magana da kai, ranka yă daɗe? Ƙarfina ya ƙare kuma ina numfashi da ƙyar.”
18 And he repeated and he touched me like [the] appearance of humankind and he strengthened me.
Har yanzu wannan wanda yana kama da mutum ya taɓa ni ya kuma ba ni ƙarfi.
19 And he said may not you fear O man of preciousness peace [be] to you be strong and be strong (and when spoke he *L(abh)*) with me I strengthened myself and I said let him speak lord my for you have strengthened me.
Ya kuma ce, “Kada ka ji tsoro, ya kai mutumin da ake fahariya, salama a gare ka! Ka ƙarfafa yanzu; ka yi ƙarfin hali.” Sa’ad da ya yi magana da ni, sai na samu ƙarfi na ce, “Ka yi magana ranka yă daɗe, tun da yake ka sa na sami ƙarfi.”
20 And he said ¿ do you know why? have I come to you and now I will return to engage in battle with [the] prince of Persia and I [am] about to go forth and there! [the] prince of Greece he will come.
Sai ya ce mini, “Ka san abin da ya kawo ni gare ka? Ba da jimawa ba zan koma in yi yaƙi da mai mulkin Farisa, kuma idan na tafi, mai mulkin Hellenawa zai taso;
21 But I will tell to you the [thing] inscribed in writing of truth and there not [is] one [who] shows himself strong with me on these that except Michael prince your.
amma da farko zan faɗa maka abin da aka rubuta a cikin Littafin Gaskiya (Babu wanda ya taimake ni yaƙi da waɗannan sai dai Mika’ilu, sarkinku.