< Acts 7 >
1 Asked then the high priest; whether (therefore *k*) these things so are?
Sai babban firist ya tambaye shi ya ce, “Waɗannan zargen gaskiya ne?”
2 And he was speaking: Men brothers and fathers, do listen. The God of glory appeared to the father of us Abraham being in Mesopotamia before than dwelling of his in Haran,
Game da wannan ya amsa ya ce, “’Yan’uwa da ubanni, ku saurare ni! Allah mai ɗaukaka ya bayyana ga kakanmu Ibrahim yayinda yake a ƙasar Mesofotamiya tukuna, kafin ya yi zama a Haran.
3 and He said to him; do go out from the country of you and from the kindred of you and come into (the *no*) land which then to you I may show.’
Allah ya ce, ‘Ka bar ƙasarka da kuma mutanenka, ka tafi ƙasar da zan nuna maka.’
4 Then having gone out from [the] land of Chaldeans he dwelt in Haran; And from there And from there after dying the father of him He removed him into land this in which you yourselves now dwell,
“Saboda haka ya bar ƙasar Kaldiyawa ya kuma yi zama a Haran. Bayan mutuwar mahaifinsa, Allah ya aika da shi wannan ƙasar da yanzu kuke zama.
5 And not He did give to him an inheritance in it not even [give] [the] length of a foot but He promised to give to him for a possession it and to the descendants of him after him, not there being to him a child.
Bai ba shi gādo a nan ba, ko taki ɗaya na ƙasa. Amma Allah ya yi masa alkawari cewa shi da zuriyarsa masu zuwa bayansa za su mallaki ƙasar, ko da yake a lokacin Ibrahim ba shi da yaro.
6 Spoke however (thus *NK(O)*) God that will be the seed of him a sojourner in a land strange and they will enslave it and they will mistreat [it] years four hundred.
Allah ya yi magana da shi ta haka, ‘Shekara ɗari huɗu, zuriyarka za tă yi baƙunci a wata ƙasar da ba tasu ba, za su yi bauta su kuma sha wulaƙanci.
7 And the nation to which (then *NK(o)*) (they will be in bondage, *N(k)O*) will judge I myself, God said and after these things they will come forth and they will serve Me in place this.’
Amma zan hore ƙasar da suka bauta wa.’ Allah ya ce, ‘Kuma daga baya za su fita daga wannan ƙasa su kuma yi mini sujada a wannan wuri.’
8 And He gave to him [the] covenant of circumcision; and thus he begat Isaac and circumcised him on the day eighth, and (*k*) Isaac Jacob, and (*k*) Jacob the twelve patriarchs.
Sa’an nan ya yi wa Ibrahim alkawari game da kaciya. Ibrahim kuwa ya zama mahaifin Ishaku ya kuma yi masa kaciya kwana takwas bayan haihuwarsa. Daga baya Ishaku ya zama mahaifin Yaƙub, Yaƙub kuma ya zama mahaifin kakanninmu sha biyun nan.
9 And the patriarchs having envied Joseph sold [him] into Egypt; But was God with him
“Domin kakanninmu sun ji kishin Yusuf, sai suka sayar da shi bawa zuwa Masar. Amma Allah ya kasance tare da shi
10 and rescued him out of all the tribulations of him and gave to him favor and wisdom before Pharaoh king of Egypt and he appointed him ruler over Egypt and (over *n*) all the house of him.
ya kuma cece shi daga dukan wahalolinsa. Ya ba wa Yusuf hikima ya kuma sa ya sami farin jini a wurin Fir’auna, sarkin Masar; saboda haka ya mai da shi mai mulki a kan Masar da kuma dukan fadarsa.
11 Came then a famine upon all the (land *k*) (of Egypt *N(k)O*) and Canaan and affliction great and not were finding sustenance the fathers of us.
“Sai yunwa ta auko wa dukan Masar da Kan’ana, ta kawo wahala mai tsanani, kakanninmu ba su iya samun abinci ba.
12 Having heard now Jacob [there] is (grain in Egypt *N(k)O*) he sent forth the fathers of us first,
Sa’ad da Yaƙub ya ji cewa akwai hatsi a Masar, sai ya aiki kakanninmu ziyararsu ta farko.
13 and on the second time (was recognised by *NK(o)*) Joseph the to brothers of him, and known became to Pharaoh the family (of Joseph. *NK(O)*)
A ziyararsu ta biyu, Yusuf ya faɗa wa’yan’uwansa wane ne shi, Fir’auna kuwa ya sami sani game da iyalin Yusuf.
14 Having sent then Joseph he called for Jacob the father of him and all the kindred (of him *k*) in all souls seventy five.
Bayan wannan, Yusuf ya aika a zo da mahaifinsa Yaƙub da dukan iyalinsa, gaba ɗaya dai mutum saba’in da biyar ne.
15 (And *no*) went down (now *ko*) Jacob into Egypt and died he himself and the fathers of us
Sai Yaƙub ya gangara zuwa Masar, inda shi da kuma kakanninmu suka mutu.
16 and they were carried over into Shechem and were placed in the tomb (which *N(k)O*) bought Abraham for a sum of silver from the sons of Hamor (in *N(k)O*) Shechem.
Aka dawo da gawawwakinsu Shekem aka binne su a kabarin da Ibrahim ya saya daga wurin’ya’yan Hamor da waɗansu kuɗi a Shekem.
17 Even as now was drawing near the time of the promise that (he agreed *N(K)O*) God to Abraham, increased the people and multiplied in Egypt
“Da lokaci ya yi kusa da Allah zai cika alkawarin da ya yi wa Ibrahim, sai yawan mutanenmu da suke a Masar ya ƙaru ƙwarai.
18 until that there arose king another (over Egypt *NO*) who not knew Joseph.
Sa’an nan wani sarki, wanda bai san kome game da Yusuf ba, ya zama mai mulkin Masar.
19 He having dealt treacherously with the race of us he mistreated the fathers of us making [them] the infants abandon of them unto the not to be given life.
Ya kuwa wulaƙanta mutanenmu sosai, ya kuma gwada wa kakanni-kakanninmu azaba ta wurin tilasta su su zubar da sababbin jariransu, don su mutu.
20 In that time was born Moses and he was beautiful to God; who was brought up months three in the house of the father (of him; *k*)
“A lokacin nan aka haifi Musa, shi kuwa ba kamar sauran jarirai ba ne. Wata uku aka yi renonsa a gidan mahaifinsa.
21 (When was being exposed *N(k)O*) then (he *N(k)O*) took up him the daughter of Pharaoh and brought up him for herself for a son.
Sa’ad da aka ajiye shi a waje, diyar Fir’auna ta ɗauke shi ta kuma rene shi kamar ɗanta.
22 And was instructed Moses (in *no*) all [the] wisdom of [the] Egyptians; he was now mighty in words and (in *k*) deeds (of him. *no*)
Musa ya sami ilimi cikin dukan hikimar Masarawa ya kuma zama mai iko cikin magana da ayyuka.
23 When then was fulfilled to him of forty years a period, it came into the mind of him to visit the brothers of him the sons of Israel.
“Da Musa ya cika shekara arba’in da haihuwa, sai ya yanke shawara yă ziyarci’yan’uwansa Isra’ilawa.
24 And having seen a certain one being wronged he defended [him] and he did vengeance for the [one] being oppressed having struck down the Egyptian.
Ya ga ɗayansu yana shan wulaƙanci a hannun wani mutumin Masar, sai ya je ya kāre shi, ya rama masa ta wurin kashe mutumin Masar ɗin.
25 He was supposing now to understand the brothers of him that God through [the] hand of him is giving salvation to them; but not they understood.
Musa ya yi tsammani mutanensa za su gane cewa, Allah yana amfani da shi don yă cece su, amma ba su gane ba.
26 On the and following day he appeared to those who were quarreling and (was reconciling *N(K)O*) them to peace having said: Men, brothers are (you yourselves; *k*) why why wrong one another?
Kashegari, Musa ya sadu da Isra’ilawa biyu suna faɗa. Ya yi ƙoƙari ya sasanta su, yana cewa, ‘Ku mutane, ku’yan’uwa ne, don me kuke so ku cutar da juna?’
27 The [one] however mistreating the neighbour pushed away him having said; Who you appointed ruler and judge over (us? *N(k)O*)
“Amma mutumin da yake wulaƙanta ɗayan, ya tura Musa a gefe ya ce, ‘Wa ya mai da kai mai mulki, da alƙali a kanmu?
28 Surely not to execute me you yourself desire [the] same way you executed yesterday the Egyptian?’
Kana so ka kashe ni kamar yadda ka kashe mutumin Masar nan na jiya?’
29 Fled then Moses at remark this and became exiled in [the] land of Midian, where he begat sons two.
Sa’ad da Musa ya ji haka, sai ya gudu zuwa ƙasar Midiyan, inda ya yi baƙunci, ya kuma haifi’ya’ya biyu maza.
30 And when were passing years forty appeared to him in the wilderness of the Mount Sinai an angel (of [the] Lord *K*) in a flame of fire of a bush.
“Bayan shekaru arba’in suka wuce, sai mala’ika ya bayyana ga Musa cikin harshen wuta a ɗan itace a hamada kusa da Dutsen Sinai.
31 And Moses having seen [it] was marvelling at the vision; When is approaching then he to behold [it], there was [the] voice of [the] Lord (to him: *K*)
Sa’ad da ya ga haka, ya yi mamakin abin da ya gani. Da ya yi kusa domin ya duba sosai, sai ya ji muryar Ubangiji ta ce,
32 I myself [am] the God of the Fathers of you, the God of Abraham and (the God *k*) of Isaac and (the God *k*) of Jacob.’ Terrified then having become Moses not he was daring to look.
‘Ni ne Allahn kakanninka, Allah na Ibrahim, Ishaku, da kuma Yaƙub.’ Sai Musa ya yi rawan jiki don tsoro, bai kuwa yi karambanin dubawa ba.
33 Said then to him the Lord; do take off the sandal of the feet of you; for the place (on *N(k)O*) which you have stood ground holy is.
“Sa’an nan Ubangiji ya ce masa, ‘Ka cire takalmanka; wurin da kake tsayen nan mai tsarki ne.
34 Having seen I saw the oppression of the people of Mine in Egypt and the groans (of them *NK(o)*) I have heard; and I have come down to deliver them; and now come (I may send *N(k)O*) you to Egypt.’
Tabbatacce na ga wulaƙancin da ake yi wa mutanena a Masar. Na ji nishinsu na kuma sauka domin in’yantar da su. Yanzu ka zo, zan aike ka ka koma Masar.’
35 This Moses whom they rejected having said; Who you appointed ruler and judge?’ — him [whom] God [as] (and *no*) ruler and redeemer (has sent by *N(k)O*) [the] hand of [the] angel who having appeared to him in the bush.
“Wannan Musa ɗin da suka ƙi suna cewa, ‘Wa ya mai da kai mai mulki da kuma alƙali?’ Allah da kansa ya aike shi, ta wurin mala’ikan da ya bayyana a gare shi a ɗan itace, yă zama mai mulkinsu, da kuma mai cetonsu.
36 this one led out them having done wonders and signs in ([the] land of *NK(o)*) (Egypt *N(k)O*) and in [the] Red Sea and in the wilderness years forty.
Ya fitar da su daga Masar ya kuma yi ayyukan da abubuwan banmamaki a Masar, a Jan Teku, da kuma cikin hamada har shekara arba’in.
37 This is the Moses having said to the sons of Israel; A prophet for you will raise up ([the] Lord *K*) God (of you *K(O)*) out from the brothers of you like me myself (of him you will listen to. *K*)
“Wannan Musa ne ya ce Isra’ilawa, ‘Allah zai aika muku wani annabi kamar ni daga cikin mutanenku.’
38 This is the [one] having been in the congregation in the wilderness with the angel who is speaking to him in the Mount Sinai and of the fathers of us who received (oracles *NK(O)*) living to give (to us; *NK(O)*)
Ya kasance a cikin taron nan a hamada, tare da mala’ikan da ya yi magana da shi a Dutsen Sinai, da kuma tare da kakanninmu; ya kuma karɓi kalmomi masu rai don yă miƙa mana.
39 to whom not wanted obedient to be the fathers of us, but they thrust away and they turned back (in *no*) (the hearts *NK(o)*) of them to Egypt,
“Amma kakanninmu suka ƙi yin masa biyayya. A maimakon haka, sai suka ƙi shi a cikin zuciyarsu kuwa suka koma Masar.
40 having said to Aaron; do make us gods who will go before us; As for Moses this who brought out us from [the] land of Egypt, not we know what (happened *N(k)O*) to him.’
Suka ce wa Haruna, ‘Ka yi mana allolin da za su yi mana jagora. Game da wannan Musa ɗin wanda ya fitar da mu daga Masar, ba mu san abin da ya faru da shi ba!’
41 And they made a calf in the days those and offered a sacrifice to the idol and they were rejoicing in the works of the hands of them.
A lokacin ne suka ƙera gunki mai siffar ɗan maraƙi. Suka kawo masa hadayu suka kuma yi bikin girmama abin da suka ƙera da hannuwansu.
42 Turned away however God and delivered them to worship the host of heaven, even as it has been written in [the] book of the prophets: Not slain beasts and sacrifices did you offer to Me years forty in the wilderness, O house of Israel?
Sai Amma Allah ya juya musu baya ya kuma ba da su ga bautar abubuwan da suke a sararin sama. Wannan ya yi daidai da abin da yake a rubuce a cikin littafin annabawa cewa, “‘Kun kawo mini hadayu da sadakoki shekaru arba’in cikin, hamada, ya gidan Isra’ila?
43 And You took up the tabernacle of Moloch and the star of the god of you Rephan, the images that you made to worship them; and I will remove you beyond Babylon.’
Kun ɗaukaka gidan tsafin Molek, da tauraron allahnku Refan, gumakan da kuka ƙera don ku yi musu sujada. Saboda haka zan aike ku zuwa bauta’ gaba da Babilon.
44 The tabernacle of the testimony was (among *K*) the fathers of us in the wilderness, even as had commanded the [One] speaking to Moses to make it according to the pattern that he had seen;
“Kakanni-kakanninmu suna da tabanakul na Shaida tare da su a hamada. An yi shi bisa ga yadda Allah ya umarci Musa, bisa ga zānen da ya gani.
45 which also brought [it] having received by succession the fathers of us with Joshua in the taking possession of the nations whom drove out God from [the] face of the fathers of us until the days of David;
Bayan sun gāji tabanakul nan, kakanninmu a ƙarƙashin jagorancin Yoshuwa suka kawo shi tare da su, lokacin da suka ƙwace ƙasar daga al’umman da Allah ya kora a idanunsu. Tabanakul ɗin ya kasance a ƙasar har zamanin Dawuda,
46 who found favor before God and asked to find a dwelling place for the (house *N(K)O*) of Jacob.
wanda ya sami tagomashi daga Allah, ya kuma nemi yă yi wa Allah na Yaƙub wurin zama.
47 Solomon however built for Him [the] house.
Amma Solomon ne ya gina masa gida.
48 Yet not the Most High in hand-made (temples *K*) dwells, Even as the prophet says:
“Duk da haka, Mafi Ɗaukaka ba ya zama a gidajen da mutane suka gina. Kamar yadda annabi ya faɗi cewa,
49 Heaven [is] to Me a throne, (and *NK(o)*) the earth a footstool of the feet of Mine; What kind of house will you build Me? says [the] Lord, or what [is] [the] place of the rest of Mine?
“‘Sama ne kursiyina, duniya kuma wurin ajiye tafin ƙafata. Wane irin gida za ka gina mini? Ko kuwa ina wurin hutuna zai kasance? In ji Ubangiji.
50 Surely the hand of Mine has made these things all?’
Ba hannuna ne ya yi dukan waɗannan abubuwa ba?’
51 Stiff-necked and uncircumcised (in the *k(o)*) (hearts *N(k)O*) (of you *o*) and in ears, you yourselves always the Spirit Holy resist, as the fathers of you also you;
“Ku mutane masu taurinkai, da zukata da kuma kunnuwa marasa kaciya! Kuna kama da kakanninku. Kullum kuna tsayayya da Ruhu Mai Tsarki!
52 Which of the prophets not did persecute the fathers of you? And they killed those having foretold about the coming of the Righteous One, of whom now you yourselves betrayers and murderers (have become; *N(k)O*)
An yi wani annabin da kakanninku ba su tsananta wa ba? Sun ma kashe waɗanda suka yi maganar zuwan Mai Adalcin nan. Yanzu kuwa kun bashe shi kuka kuma kashe shi
53 who received the law by [the] ordination of angels and not kept [it].
ku da kuka karɓi dokar da aka sa a aiki ta wurin mala’iku amma ba ku yi biyayya da ita ba.”
54 Hearing now these things they felt cut up in the hearts of them and were gnashing the teeth at him.
Da membobin Sanhedrin suka ji haka, sai suka yi fushi suka ciji haƙoransu.
55 He being however full of [the] Spirit Holy, having looked intently into heaven saw [the] glory of God and Jesus already standing at [the] right hand of God
Amma Istifanus, cike da Ruhu Mai Tsarki, ya dubi sama ya kuma ga ɗaukakar Allah, da Yesu kuma tsaye a hannun dama na Allah.
56 and he said; Behold I see the heavens (opened up *N(k)O*) and the Son of Man at [the] right [hand] already standing of God.
Ya ce, “Ga shi, na ga sama a buɗe da kuma Ɗan Mutum tsaye a hannun dama na Allah.”
57 Having cried out then in a voice loud they held the ears of them and rushed with one accord upon him;
Da jin haka sai suka tattoshe kunnuwansu, suka kuma yi ihu da ƙarfi sosai, suka aukar masa gaba ɗaya.
58 and having cast [him] out of the city they were stoning [him]. And the witnesses laid aside the garments of them at the feet of a young man named Saul
Suka ja shi zuwa bayan birnin suka kuma yi ta jifansa da duwatsu. Ana cikin haka, shaidun suka ajiye tufafinsu a wurin wani saurayi mai suna Shawulu.
59 And [as] they were stoning Stephen he was calling out and saying; Lord Jesus, do receive the spirit of mine.
Yayinda suke cikin jifansa, sai Istifanus ya yi addu’a ya ce, “Ubangiji Yesu, ka karɓi ruhuna.”
60 Having fallen then on [his] knees he cried in a voice loud; Lord, not may place to them this sin. And this having said he fell asleep.
Sa’an nan ya durƙusa ya ɗaga murya ya ce, “Ubangiji, kada ka riƙe wannan zunubi a kansu.” Da ya faɗi haka, sai ya yi barci.