< Acts 24 >
1 After then five days came down the high priest Ananias with (of the *k*) elders (some *NO*) and an orator Tertullus certain, who made a representation to the governor against Paul.
Bayan kwana biyar sai Ananiyas babban firist ya tafi Kaisariya tare da waɗansu daga cikin dattawa da kuma wani lauya mai suna Tertullus, suka kawo ƙararsu game da Bulus a gaban gwamna.
2 When was invited then he began to accuse Tertullus saying; Great peace we are attaining through you and (excellent reforms *N(K)O*) are being done to the nation this [one] through your foresight
Sa’ad da aka shigo da Bulus, sai Tertullus ya shiga kai ƙararsa a gaban Felis yana cewa, “Mun daɗe muna zaman lafiya a ƙarƙashinka, hangen nesanka kuma ya kawo gyare-gyare a wannan ƙasa.
3 in every way both and everywhere we gladly accept [it], most excellent Felix, with all thankfulness.
Ko’ina da kuma a kowace hanya, ya mafifici Felis, mun amince da wannan da godiya marar iyaka.
4 In order that however not to any longer you I may be a hindrance, I implore to hear you us briefly in your kindness.
Amma don kada in ƙara gajiyar da kai, ina roƙonka ka yi haƙuri ka saurari ɗan taƙaitaccen jawabinmu.
5 Having found for man this a pest and stirring (insurrections *N(K)O*) among all the Jews in the world a leader then of the of the Nazarenes sect;
“Mun tarar da wannan mutum fitinanne ne, yana tā-da-na-zaune-tsaye a tsakanin Yahudawa ko’ina a duniya. Shi shugaban ɗarikar Nazarawa
6 who even the temple attempted to profane, whom also we seized (and according to our own law we wanted to judge. *K*)
har ma ya yi ƙoƙari ya ƙazantar da haikali; shi ya sa muka kama shi.
7 (having come up now Lysias the commander with great violence from the hands of us being carried away, *K*)
8 (having commanded the accusers of him to come upon you; *K*) From him you will be able yourself having examined [him] concerning all these things to know of which we ourselves accuse him.
Ta wurin bincika shi da kanka za ka gane gaskiyar game da dukan waɗannan zargin da muke kawo a kansa.”
9 (Agreed *N(k)O*) then also the Jews declaring these things so to be.
Yahudawa ma suka goyi bayan zargin, suna tabbatar cewa waɗannan abubuwa haka suke.
10 Answered (then *N(k)O*) Paul, when was signalling to him the governor to speak: For many years as being you judge to nation this knowing [these] encouraging things, concerning myself I present a defense;
Da gwamna ya yi masa alama yă yi magana, sai Bulus ya amsa ya ce, “Na san cewa ka yi shekaru da yawa kana mulki a wannan ƙasa; saboda haka ina farin ciki in kāre kaina.
11 Being able you (to know *N(k)O*) that not more there are to me days (than *k*) (twelve *N(k)O*) from which I went up to then worship (in *N(k)O*) Jerusalem;
Da sauƙi za ka iya tabbatar cewa, bai fi kwana goma sha biyu da suka wuce ne na tafi Urushalima, domin yin sujada ba.
12 And neither in the temple did they find me with anyone reasoning or (obstruction *N(k)O*) making of a crowd nor in the synagogues nor in the city;
Masu zargina ba su same ni ina gardama da kowa a haikali, ko kuma ina tā da hankalin jama’a a majami’u ko kuwa wani wuri dabam a cikin birni ba.
13 (nor *N(k)O*) to prove are they able (to you *N(K)O*) concerning [the things] of which (now *N(k)O*) they accuse me.
Ba kuwa za su iya tabbatar maka ƙarar da suke yi yanzu a kaina ba.
14 I confess however this to you that according to the Way which they name a sect so I serve the ancestral God believing in all [things] throughout the law and (that in *no*) the Prophets written,
Amma na yarda cewa ina bauta wa Allah na kakanninmu a matsayin mai bin Hanyar da suke kira ɗarika. Na gaskata dukan abin da ya amince da Doka da yake kuma a rubuce cikin Annabawa,
15 a hope having in God which also they themselves await, [that] a resurrection to ensue to then be (of [the] dead-*K*) of [the] just both and of [the] unjust;
ina kuma da irin bege ɗaya ga Allah yadda mutanen nan suke da shi, cewa akwai tashin matattu masu adalci da masu mugunta duka.
16 In this (also *N(k)O*) I myself strive without offense a conscience (to have *NK(o)*) toward God and men (through *N(K)O*) (all [times]. *N(k)O*)
Saboda haka, ina ƙoƙari kullum in kasance da lamiri mai tsabta a gaban Allah da mutane.
17 After years now many alms to then bring to the nation of mine I came and offerings,
“Bayan’yan shekaru da dama da ba na nan, sai na dawo Urushalima don in kawo wa mutanena kyautai saboda matalauta in kuma yi sadaka.
18 during (which *N(k)O*) they found me purified in the temple not with a crowd nor in tumult, Some however [are] from Asia Jews
Ni tsarkake ne sa’ad da suka same ni cikin filin haikalin ina yin haka. Babu taro tare da ni, ba kuwa ina tā da hankali ba.
19 who (it was necessary *N(k)O*) before you to appear and to make accusation, if anything they would have against me myself.
Amma akwai waɗansu Yahudawa daga lardin Asiya, waɗanda ya kamata suna a nan a gabanka su kawo ƙara in suna da wani a kaina.
20 Otherwise themselves it they should say (if *k*) any they found (in me myself *ko*) unrighteousness when was standing I before the Council,
Ko kuwa waɗannan da suke a nan su faɗi laifin da suka same ni da shi sa’ad da na tsaya a gaban Majalisa,
21 [other] than concerning one this voice which I cried out among them standing that Concerning [the] resurrection of [the] dead I myself am judged this day (by *N(k)O*) you.
sai ko wannan abu ɗaya kaɗai da na ɗaga murya na faɗi yayinda nake tsaye a gabansu cewa, ‘A game da tashin matattu ake mini shari’a a gabanku yau.’”
22 (having heard these things *K*) deferred then them Felix more precisely knowing the [things] concerning the Way having said; When Lysias the commander may have come down, I will examine the [things] as to you.
Sai Felis, wanda yake da cikakken sani game da Hanyar, ya ɗaga sauraron ƙarar. Ya ce, “In Lisiyas shugaban ƙungiyar soja ya iso, zan yanke muku shari’a.”
23 having commanded (also *k*) to the centurion to keep (*k*) (him, *N(K)O*) to [let him] have then ease and not to forbid the private [friends] of him to minister (or to come near *K*) to him.
Ya yi wa jarumin umarni yă tsare Bulus amma yă ba shi’yanci yă kuma bar abokansa su lura da bukatunsa.
24 After then days some having arrived Felix with Drusilla the (own *N(k)O*) wife being a Jewess he sent for Paul and heard him concerning the in Christ (Jesus *NO*) faith.
Bayan’yan kwanaki da dama sai Felis ya zo da matarsa Durusilla, mutuniyar Yahuda. Sai ya aika a zo da Bulus ya kuma saurare shi da yake magana game da bangaskiya cikin Kiristi Yesu.
25 When reasoning then he concerning righteousness and self-control and the judgment which is coming (to be [in the future] *K*) frightened having become Felix answered; For the present being do go away; opportunity then having found I will call for you;
Da Bulus ya ci gaba jawabi a kan adalci, kamunkai da kuma hukunci mai zuwa, sai Felis ya tsorata ya ce, “Yanzu kam, ya isa haka! Kana iya tafi. In na sami zarafi, zan kira ka.”
26 At the same time (now *k*) also he is hoping that riches will be given to him by Paul (so that may release him *K*) Therefore also often him sending for he was talking with him.
A wani fanni yana sa rai cewa Bulus zai ba shi toshiyar baki, saboda haka ya yi ta aika a kira masa Bulus yă yi magana da shi.
27 When two years however having been completed he received [as] successor Felix Porcius Festus, wishing then (favor *N(k)O*) to acquire for himself with the Jews Felix left Paul imprisoned.
Da shekaru biyu suka wuce, sai Forsiyus Festus, ya gāji Felis, amma domin Felis ya so yă biya wa Yahudawa bukata, sai ya bar Bulus a kurkuku.