< 2 Kings 5 >

1 And Naaman [the] commander of [the] army of [the] king of Aram he was a man great before master his and lifted up of face for by him he had given Yahweh victory to Aram and the man he was a mighty [man] of strength having a skin disease.
Na’aman babban hafsan hafsoshin rundunar sarkin Aram ne, kuma ƙasaitaccen mutum ne mai martaba a idon maigidansa, domin ta wurinsa Ubangiji ya ba Aram nasara. Na’aman jarumi ne ƙwarai, amma yana da kuturta.
2 And Aram they had gone out marauding bands and they had taken captive from [the] land of Israel a girl young and she was before [the] wife of Naaman.
To, daga cikin hare haren da mutanen Aram suke kaiwa, sai suka kama wata yarinya daga ƙasar Isra’ila, aka sa ta zama mai yi wa matar Na’aman aiki.
3 And she said to mistress her would that! master my [was] before the prophet who [is] in Samaria then he will deliver him from skin disease his.
Sai ta ce wa uwargijiyarta, “Da dai shugabana zai ga annabin da yake Samariya, da annabin zai warkar da shi daga kuturtarsa.”
4 And he went and he told to master his saying like this and like this she spoke the girl who [is] from [the] land of Israel.
Sai Na’aman ya je wurin maigidansa ya faɗa masa abin da yarinyan nan daga Isra’ila ta faɗa.
5 And he said [the] king of Aram come go so let me send a letter to [the] king of Israel and he went and he took in hand his ten talents of silver and six thousand gold and ten changes of garments.
Sarkin Aram ya ce, “Ko ta ƙaƙa, ka tafi, zan aika da wasiƙa ga sarkin Isra’ila.” Sai Na’aman ya tashi, ɗauke da talenti goma na azurfa, shekel dubu shida na zinariya, da tufafi kashi goma.
6 And he brought the letter to [the] king of Israel saying and now when comes the letter this to you here! I have sent to you Naaman servant my and you will deliver him from skin disease his.
Wasiƙar da ya kai wa sarkin Isra’ila ta ce, “Da wannan wasiƙa ina aika Na’aman gare ka don ka warkar da kuturtarsa.”
7 And it was when read aloud [the] king of Israel the letter and he tore clothes his and he said ¿ God [am] I to kill and to restore to life that this [man] [is] sending to me to deliver a man from skin disease his that only consider please and see that [is] seeking an opportunity he to me.
Da sarkin Isra’ila ya karanta wasiƙar, sai ya yayyage tufafinsa, ya ce, “Ni Allah ne? Zan iya ɗauke rai ko in mai da shi? Me ya sa wannan mutum ya turo mini wannan mutum in warkar da kuturtarsa? Dubi fa yadda yake nemana da faɗa!”
8 And it was when heard - Elisha [the] man of God that he had torn [the] king of Israel clothes his and he sent to the king saying why? did you tear clothes your let him come please to me so he may know that there [is] a prophet in Israel.
Da Elisha mutumin Allah ya ji cewa sarkin Isra’ila ya yayyage tufafinsa, sai ya aika masa da wannan saƙo, “Don me za ka yayyage tufafinka? Ka sa mutumin yă zo wurina, zai kuwa san cewa akwai annabi a Isra’ila.”
9 And he came Naaman (with horses his *Q(K)*) and with chariot[s] his and he stood [the] entrance of the house of Elisha.
Saboda haka Na’aman ya tafi da dawakansa da keken yaƙinsa, ya tsaya a ƙofar gidan Elisha.
10 And he sent to him Elisha a messenger saying go and you will wash seven times in the Jordan and it may return flesh your to you and be clean.
Sai Elisha ya aika’yan saƙo su ce masa, “Je, ka nutse sau bakwai a Urdun, fatar jikinka za tă koma daidai, ka kuma tsarkaka.”
11 And he was angry Naaman and he went and he said here! I said to myself - he will come out continuously and he will stand and he will call on [the] name of Yahweh God his and he will wave hand his to the place and he will deliver the [one] having a skin disease.
Amma Na’aman ya tashi daga can da fushi yana cewa, “Na yi tsammani zai fito ne wurina yă tsaya, yă yi kira bisa ga sunan Ubangiji Allahnsa, yă kaɗa hannunsa inda kuturtar take, yă warkar da ni.
12 ¿ Not good ([are] Amana *Q(K)*) and Pharpar [the] rivers of Damascus more than all [the] waters of Israel ¿ not will I wash in them and I will be clean and he turned and he went in a rage.
Ashe, Amana da Farfa, kogunan da suke Damaskus, ba su fi dukan ruwan da suke Isra’ila ba? Me zai sa ba zan nutse cikinsu in tsarkaka ba?” Sai ya juya ya yi tafiyarsa da fushi.
13 And they drew near servants his and they spoke to him and they said would that a thing great the prophet he spoke to you ¿ not will you do [it] and indeed? if he has said to you wash and be clean.
Sai bayin Na’aman suka je kusa da shi suka ce, “Baba, da a ce annabin ya ce ka yi wani abu mai wuya, da ba za ka yi ba? Balle fa cewa kawai ya yi, ‘Ka yi wanka ka kuma tsarkaka’!”
14 And he went down and he dipped in the Jordan seven times according to [the] word of [the] man of God and it returned flesh his like [the] flesh of a lad young and he was clean.
Saboda haka Na’aman ya je ya nutse sau bakwai a Urdun, yadda mutumin Allah ya ce masa, sai fatarsa ta koma kamar ta ɗan yaro.
15 And he went back to [the] man of God he and all camp his and he came and he stood before him and he said here! please I know that there not [is] a God in all the earth that except in Israel and now accept please a blessing from with servant your.
Sai Na’aman da dukan masu hidimarsa suka koma wurin mutumin Allah. Na’aman ya tsaya a gaban mutumin Allah ya ce, “Yanzu na san cewa babu wani Allah a duk duniya sai a Isra’ila. Ina roƙonka ka karɓi kyauta daga hannun bawanka.”
16 And he said [by] [the] life of Yahweh whom I stand before him if I will accept and he urged him to accept and he refused.
Annabin ya amsa ya ce, “Muddin Ubangiji wanda nake bauta masa yana a raye, ba zan karɓi kome ba.” Ko da yake Na’aman ya yi ta roƙonsa, amma ya ƙi.
17 And he said Naaman and not let it be given please to servant your [the] load of a pair of mules earth for not he will offer again servant your burnt offering and sacrifice to gods other that except to Yahweh.
Sai Na’aman ya ce, “In ba za ka karɓa ba, ina roƙonka, bari a ba wa bawanka ƙasa gwargwadon abin da jakuna biyu za su iya ɗauka, gama bawanka ba zai sāke yin hadaya ta ƙonawa, ko wata hadaya ga wani allah ba, sai ga Ubangiji.
18 To the matter this may he forgive Yahweh servant your when goes master my [the] house of Rimmon to bow down there and he - [is] supporting himself on hand my and I will bow down [the] house of Rimmon when bow down I [the] house of Rimmon may he forgive (*Q(K)*) Yahweh servant your in the matter this.
Amma ina fata Ubangiji zai gafarta wa bawanka saboda abu guda. Bari yă gafarta mini sa’ad da na raka sarkina zuwa haikalin Rimmon domin yă yi sujada, bari Ubangiji yă yi wa bawanka gafara saboda wannan.”
19 And he said to him go to peace and he went from with him a distance of land.
Sai Elisha ya ce, “Ka sauka lafiya.” Bayan Na’aman ya yi ɗan nisa,
20 And he said Gehazi [the] servant of Elisha [the] man of God here! - he has restrained master my Naaman the Aramean this from accepting from hand his [that] which he brought [by] [the] life of Yahweh that except I run after him and I will accept from with him anything.
sai Gehazi, bawan Elisha mutumin Allah, ya yi tunani a ransa ya ce, “Maigidana ya yi wa Na’aman mutumin Aram nan ƙaramci da bai karɓi duk abin da ya kawo ba. Muddin Ubangiji yana a raye, zan bi shi a guje in karɓi wani abu daga gare shi.”
21 And he pursued Gehazi after Naaman and he saw Naaman [one who] ran after him and he fell from on the chariot to meet him and he said ¿ peace.
Saboda haka Gehazi ya bi Na’aman a guje. Da Na’aman ya hango shi yana zuwa a guje, sai ya sauka daga keken yaƙinsa ya tarye shi ya ce, “Lafiya?”
22 And he said - peace master my he has sent me saying here! now this they have come to me two young men from [the] hill country of Ephraim of [the] sons of the prophets give! please to them a talent of silver and two changes of garments.
Gehazi ya amsa ya ce, “Lafiya ƙalau. Maigidana ne ya aiko ni cewa, ‘Samari biyu daga ƙungiyar annabawa sun ziyarce ni daga ƙasa mai duwatsu na yankin Efraim. Ina roƙonka ka ba su talenti na azurfa da tufafi kashi biyu.’”
23 And he said Naaman be willing accept two talents and he urged him and he secured two talents silver in two bags and two changes of garments and he gave [them] to two of servants his and they carried [them] before him.
Na’aman ya ce, “Ba damuwa, karɓi talenti biyu.” Ya roƙi Gehazi yă karɓa, sa’an nan ya ƙunsa masa talentin biyu na azurfa ya sa masa a kan jakankuna biyu, ya haɗa da tufafi kashi biyu, ya ba bayinsa biyu suka ɗauka, ya ce su sha gaban Gehazi.
24 And he came to the hill and he took [them] from hand their and he deposited [them] in the house and he sent away the men and they went.
Da Gehazi ya isa wani tudu, sai ya karɓi kayan daga wurin bayin ya shiga da su a ɓoye a cikin gida. Sa’an nan ya sallami mutanen suka tafi.
25 And he he went and he stood to master his and he said to him Elisha (from whence? *Q(K)*) O Gehazi and he said not he has gone servant your where? and where?
Sa’an nan ya shiga ya tsaya a gaban maigidansa Elisha. Sai Elisha ya tambaye shi ya ce, “Ina ka je, Gehazi?” Sai Gehazi ya amsa ya ce, “Bawanka bai je ko’ina ba.”
26 And he said to him not heart my did it go? just when he turned a man from on chariot his to meet you ¿ a time to accept silver and to accept clothes and olive trees and vineyards and sheep and cattle and male servants and maidservants.
Amma Elisha ya ce masa, “Ashe, ba ina tare da kai a ruhu ba sa’ad da mutumin ya sauko daga keken yaƙinsa ya tarye ka. Kana gani wannan lokaci ne da za a karɓi kuɗi, da riguna, da gonar inabi, da tumaki, da bijimai, da bayi maza da mata?
27 And [the] skin disease of Naaman it will cling to you and to offspring your for ever and he went out from to before him having a skin disease like snow.
Kuturtar Na’aman zai manne maka da zuriyarka har abada.” Sai Gehazi ya fita daga gaban Elisha a kuturce, fari fat kamar dusar ƙanƙara.

< 2 Kings 5 >