< 2 Kings 11 >

1 And Athaliah [the] mother of Ahaziah (she saw *Q(K)*) that he was dead son her and she arose and she destroyed all [the] offspring of royalty.
Da Ataliya mahaifiyar Ahaziya ta ga ɗanta ya mutu, sai ta shiga hallaka dukan iyalin gidan sarauta.
2 And she took Jehosheba [the] daughter of the king Joram [the] sister of Ahaziah Joash [the] son of Ahaziah and she stole him from among [the] sons of the king (who were about to be put to death *Q(K)*) him and suckling-nurse his in [the] chamber of the beds and they hid him from before Athaliah and not he was put to death.
Amma Yehosheba,’yar Sarki Yoram,’yar’uwar Ahaziya, ta ɗauki Yowash ɗan Ahaziya daga cikin’ya’yan sarkin da ake shiri a kashe, ta ɓoye. Ta ɓoye shi daga Ataliya a wurin mai lura da shi a ɗakin kwana; don kada a kashe shi.
3 And he was with her [the] house of Yahweh hiding himself six years and Athaliah [was] reigning over the land.
Ya kasance a ɓoye, shi da mai lura da shi, a haikalin Ubangiji shekara shida yayinda Ataliya take mulkin ƙasar.
4 And in the year seventh he sent Jehoiada and he took - [the] commanders of (the hundreds *Q(k)*) of the Carian[s] and of the runners and he brought them to himself [the] house of Yahweh and he made to them a covenant and he made to swear an oath with them in [the] house of Yahweh and he showed them [the] son of the king.
A shekara ta bakwai sai Yehohiyada ya aika a kira komandodin sojoji ɗari-ɗari, da Keretawa, da matsara, ya sa aka kawo masa su a haikalin Ubangiji. Ya ƙulla yarjejjeniya da rantsuwa da su a haikalin Ubangiji, sa’an nan ya nuna musu ɗan sarki.
5 And he commanded them saying this [is] the thing which you will do! the third [part] of you [who] come the sabbath and [who] keep [the] watch of [the] house of the king.
Ya umarce su cewa, “Ga abin da za ku yi sa’ad da kuka zo aiki a Asabbaci, ku raba kanku kashi uku. Kashi ɗaya za su yi gadin gidan sarki,
6 And the third [part] [will be] at [the] gate of Sur and the third [part] [will be] at the gate behind the runners and you will keep [the] watch of the house by turns.
kashi ɗaya za su yi gadin Ƙofar Sur, kashi ɗaya kuma za su yi gadin ƙofar da take bayan’yan gadin fada. Dukan waɗannan ƙungiyoyi uku za su yi gadin fadan,
7 And [the] two the hands in you all [those who] go out the sabbath and they will keep [the] watch of [the] house of Yahweh to the king.
ku kuma da kuke a sauran ƙungiyoyi biyu da kun saba hutu a Asabbaci, duk za ku yi gadin haikali don sarki.
8 And you will surround the king all around everyone and weapons his in hand his and the [one who] comes into the ranks he will be put to death and be with the king when goes out he and when comes he.
Ku tsaya kewaye da sarki, kowane mutum da makaminsa a hannu. Duk wanda ya kusace ku, ku kashe shi. Ku manne wa sarki duk inda ya tafi.”
9 And they did [the] commanders of (the hundreds *Q(k)*) according to all that he commanded Jehoiada the priest and they took each men his [those who] came the sabbath with [those who] went out the sabbath and they came to Jehoiada the priest.
Komandodin sojoji suka yi yadda Yehohiyada firist ya umarta. Kowa ya ɗauki mutanensa, waɗanda za su kama aiki Asabbaci da waɗanda za su kama hutun Asabbaci, suka zo wurin Yehohiyada firist.
10 And he gave the priest to [the] commanders of (the hundreds *Q(k)*) the spear and the shields which [had belonged] to the king David which [were] in [the] house of Yahweh.
Sai ya ba komandodin māsu da garkuwoyi da dā suke na Dawuda, waɗanda suke a cikin haikalin Ubangiji.
11 And they stood the runners everyone - and weapons his in hand his from [the] side of the house south to [the] side of the house north to the altar and to the house at the king all around.
Matsaran kuma kowa da makaminsa a hannu, suka tsaya kewaye da sarki, kusa da bagade da kuma haikali, daga gefen kudu zuwa gefen arewa na haikalin.
12 And he brought out [the] son of the king and he put on him the crown and the testimony and they made king him and they anointed him and they struck a palm and they said may he live the king.
Sai Yehohiyada ya fito da ɗan sarki ya sa masa rawani a kā; ya ba shi shafin alkawari, ya kuma furta shi sarki. Suka shafe shi da mai, mutane kuma suka yi ta tafi suka ihu, suna cewa, “Ran sarki yă daɗe.”
13 And she heard Athaliah [the] sound of the runners the people and she went to the people [the] house of Yahweh.
Sa’ad da Ataliya ta ji surutun matsara da na mutane, sai ta tafi wurin mutanen a haikalin Ubangiji.
14 And she saw and there! the king [was] standing at the pillar according to the custom and the commanders and the trumpets [were] with the king and all [the] people of the land [was] joyful and [was] giving a blast on trumpets and she tore Athaliah clothes her and she called out treason treason.
Da ta duba sai ga sarki, tsaye kusa da ginshiƙi, bisa ga al’ada. Hafsoshi da masu busa suna tsaye kusa da sarki, dukan mutanen ƙasar kuma suna farin ciki suna busa ƙahoni. Sai Ataliya ta keta tufafinta ta tā da murya tana cewa, “Kai! Wannan cin amana ne! Ai, wannan cin amana ne!”
15 And he commanded Jehoiada the priest [the] commanders of (the hundreds *Q(k)*) [the] officers of the army and he said to them bring out her to from between to the ranks and the [one who] comes behind her put to death with the sword for he had said the priest may not she be put to death [the] house of Yahweh.
Yehohiyada ya umarci komandodin sojoji waɗanda suke lura da mayaƙa, ya ce, “Ku fitar da ita daga cikinku, ku kuma kashe duk wanda ya bi ta.” Gama firist ɗin ya ce, “Kada a kashe ta a cikin haikalin Ubangiji.”
16 And they put to her hands and she went [the] way of [the] entrance of the horses [the] house of the king and she was put to death there.
Saboda haka suka kama ta yayinda ta kai inda dawakai sukan shiga filin fada, a can kuwa aka kashe ta.
17 And he made Jehoiada the covenant between Yahweh and between the king and between the people to become a people of Yahweh and between the king and between the people.
Sa’an nan Yehohiyada ya yi alkawari tsakanin Ubangiji da sarki da kuma mutane cewa za su zama mutanen Ubangiji. Ya kuma yi alkawari tsakanin sarki da mutane.
18 And they went all [the] people of the land [the] house of Baal and they pulled down it (altars its *Q(K)*) and images its they broke thoroughly and Mattan [the] priest of Baal they killed before the altars and he appointed the priest overseers over [the] house of Yahweh.
Sai dukan mutanen ƙasar suka tafi haikalin Ba’al suka rushe shi. Suka farfasa bagadai da kuma gumaka, suka kuma kashe Mattan wanda yake firist na Ba’al a gaban bagade. Sa’an nan Yehohiyada firist ya sa matsara a haikalin Ubangiji.
19 And he took [the] commanders of the hundreds and the Carian[s] and the runners and - all [the] people of the land and they took down the king from [the] house of Yahweh and they came [the] way of [the] gate of the runners [the] house of the king and he sat on [the] throne of the kings.
Ya tafi tare da komandodin sojoji, Keretawa, matsara da kuma dukan mutanen ƙasar, tare kuwa suka kawo sarki daga haikalin Ubangiji zuwa cikin fada, ta ƙofar matsara. Sarki kuwa ya ɗauki mazauninsa a bisa kursiyin sarauta,
20 And it rejoiced all [the] people of the land and the city it was at peace and Athaliah they had put to death with the sword [the] house of (the king. *Q(K)*)
dukan mutanen ƙasar suka yi murna. Birnin ya sami salama don an kashe Ataliya da takobi a fada.
21 [was] a son of Seven years Jehoash when became king he.
Yowash yana da shekara bakwai sa’ad da ya fara mulki.

< 2 Kings 11 >