< 2 Corinthians 6 >
1 Working together now also we exhort not in vain the grace of God to receive you;
A matsayinmu na abokan aikin Allah, muna roƙonku kada ku karɓi alherin Allah a banza.
2 He says for: In a time acceptable I listened to you and in a day of salvation I helped you; Behold now [is the] time of favor, behold now [is the] day of salvation;
Gama ya ce, “A lokacin samun alherina, na ji ka, a ranar samun ceto kuma, na taimake ka.” Ina gaya muku, yanzu ne lokacin samun alherin Allah, yanzu ne ranar samun ceto.
3 Nothing before no one placing an obstacle, so that not may be blemished the ministry,
Ba ma sa abin tuntuɓe wa kowa, domin kada hidimarmu ta zama abin zargi.
4 rather in everything we are commending ourselves as God’s servants in endurance great, in tribulations, in hardships, in distresses,
A maimakon haka, duk abin da muke yi, muna yin shi ne don mu nuna cewa mu masu hidimar Allah ne. Muna yin haka cikin jimrewa, da shan wahala, da shan wuya, har da shan masifu.
5 in beatings, in imprisonments, in riots, in labors, in watchings, in fastings,
Da shan dūka, da shan dauri, da yawan hargitsi, da yawan fama, da rashin barci, da kuma yunwa.
6 in purity, in knowledge, in patience, in kindness, in [the] Spirit Holy, in love genuine,
Da cikin tsarki, da fahimta, da haƙuri, da kirki, da cikin Ruhu Mai Tsarki, da cikin ƙauna mai gaskiya,
7 in [the] word of truth, in [the] power of God, with the weapons of righteousness for the right hand and for [the] left,
da cikin magana mai gaskiya, da kuma cikin ikon Allah. Muna riƙe da makaman adalci dama da hagu,
8 through glory and dishonor, through bad report and good report, as imposters and yet true,
ta wurin ɗaukaka da ƙasƙanci, da cikin ɓata suna, da kuma cikin yabo. Cikin faɗin gaskiya, an ɗauke mu masu ƙarya,
9 as being unknown and yet being well-known, as dying and yet behold we live, as being disciplined and yet not being killed,
mu sanannu ne, duk da haka an ɗauke mu kamar ba a san mu ba, muna mutuwa, duk da haka a raye muke, an ba mu horo, duk da haka ba a kashe mu ba,
10 as being sorrowful always yet rejoicing, as poor many yet enriching, as nothing having and yet all things possessing.
cikin baƙin ciki, duk da haka kullum cikin murna muke. Cikin matalauta, duk da haka muna azurtar da mutane da yawa. Ba mu da kome, alhali kuwa kome namu ne.
11 The mouth of us has been opened to you, Corinthians, the heart of us has been expanded;
Ya ku Korintiyawa, mun yi muku magana a sake, muka kuma saki zuciya da ku ƙwarai.
12 Not you are restrained by us, you are restrained however in the affections of you;
Ba mu ƙi nuna muku ƙaunarmu ba, sai dai ku kuka ƙi nuna mana.
13 Now [as] the same recompense, as to children I speak, do open [yourselves] also you.
A wannan zance kam, ina magana da ku kamar’ya’yana, ku ma ku saki zuciya da mu.
14 Not do become unequally yoked together with unbelievers; what for partnership [have] righteousness and lawlessness? (Or *N(k)O*) what fellowship light with darkness?
Kada ku haɗa kai da marasa bi. Gama me ya haɗa adalci da mugunta? Ko kuwa me ya haɗa haske da duhu?
15 What now harmony [has] (Christ *N(k)O*) with Belial? Or what part [has] a believer with an unbeliever?
Wace daidaituwa ce tsakanin Kiristi da Iblis? Me ya haɗa mai bi da marar bi?
16 What now agreement [the] temple of God with idols? (We ourselves *N(K)O*) for [the] temple of God (we are *N(K)O*) [the] living, even as has said God that I will dwell in them and will walk among [them], and I will be their God and they themselves will be (to Me *N(k)O*) a people.
Wane alkawari ne tsakanin haikalin Allah da na gumaka? Gama mu haikalin Allah mai rai ne. Kamar yadda Allah ya ce, “Zan zauna tare da su, in yi tafiya a cikinsu, zan zama Allahnsu, su kuma za su zama mutanena.”
17 Therefore do come out from [the] midst of them and do be separate, says [the] Lord, and unclean nothing do touch; and I myself and I myself will receive you,
Saboda haka, “Sai ku fito daga cikinsu, ku keɓe kanku, in ji Ubangiji. Kada ku taɓa wani abu marar tsabta, zan kuma karɓe ku.”
18 and I will be to you for a father and you yourselves will be to Me for sons and daughters, says [the] Lord Almighty.
Kuma, “Zan zama Uba a gare ku, ku kuma za ku zama’ya’yana, maza da mata, in ji Ubangiji Maɗaukaki.”