< 1 Samuel 20 >

1 And he fled David (from Naioth *Q(k)*) in Ramah and he went and he said - before Jonathan what? have I done what? [is] iniquity my and what? [is] sin my before father your that [is] seeking life my.
Sai Dawuda ya gudu daga Nayiwot a Rama ya je wurin Yonatan ya ce, “Me na yi? Wane laifi ne na yi? Ta wace hanya ce na yi wa mahaifinka laifi har da yake neman yă kashe ni?”
2 And he said to him far be it not you will die here! (not he does *Q(K)*) father my anything great or anything small and not he uncovers ear my and why? will he hide father my from me the thing this there not [is] this.
Yonatan ya ce, “Faufau, ba za ka mutu ba! Ka ji nan, mahaifina ba ya yin kome ba tare da ya shawarce da ni ba. Me ya sa ya ɓoye mini wannan? Ba zai yiwu ba.”
3 And he swore an oath again David and he said certainly he knows father your that I have found favor in view your and he has said may not he know this Jonathan lest he should be grieved and but [by] [the] life of Yahweh and [by] [the] life of self your for about a step between me and between death.
Sai Dawuda ya rantse ya ce, “Mahaifinka ya san cewa, na sami tagomashi a gare ka, domin haka ba zai sanar maka da wannan ba, don kada yă baƙanta maka rai. Na rantse da Ubangiji, da kai kuma, taki ɗaya kaɗai ya rage tsakanina da mutuwa.”
4 And he said Jonathan to David whatever it will say self your so I may do for you.
Sai Yonatan ya ce, “Duk abin da kake so in yi maka zan yi.”
5 And he said David to Jonathan here! a new moon [will be] tomorrow and I certainly I will sit with the king to eat and you will let go me and I will hide myself in the field until the evening third.
Dawuda ya ce, “Gobe fa shi ne Bikin Sabon Wata, ya kamata in ci tare da sarki amma bari in tafi fili in ɓuya har jibi da yamma.
6 Certainly [if] he will miss me father your and you will say certainly he asked for himself from me David to run Beth-lehem city his for [the] sacrifice of the days [is] there for all the clan.
In mahaifinka bai gan ni ba, ka gaya masa cewa, ‘Dawuda ya nemi izinina domin yă hanzarta yă tafi garinsa a Betlehem saboda ana hadaya ta shekara-shekara don dukan zuriyarsa.’
7 If thus he will say good safety [belongs] to servant your and if certainly it will burn to him know that it has been determined harm from with him.
In ya yi na’am, to, bawanka ya tsira. Amma in ka ga ya damu, to, ka tabbata ya yi niyya yă kashe ni.
8 And you will do covenant loyalty towards servant your for in [the] covenant of Yahweh you have brought servant your with you and if there in me [is] iniquity put to death me you and to father your why? this will you bring me.
Kai kuma, ka nuna alheri ga bawanka, gama ka riga ka yi yarjejjeniya da ni a gaban Ubangiji, in kuwa na yi laifi ne sai ka kashe ni da kanka. Don me za ka bashe ni ga mahaifinka?”
9 And he said Jonathan far be it to you that - if ever I will know that it has been determined harm from with father my to come on you and not it will I tell to you.
Yonatan ya ce, “Labudda! In na ji ƙishin-ƙishin, cewa mahaifina yana neman yă kashe ka ashe, ba zan gaya maka ba?”
10 And he said David to Jonathan who? will he tell to me or what? will he answer you father your hard.
Dawuda ya ce, “Wa zai gaya mini idan mahaifinka ya amsa maka da amsa marar daɗi?”
11 And he said Jonathan to David come! so we may go out the field and they went out [the] two of them the field.
Yonatan ya ce, “Zo mu fita zuwa fili.” Sai suka tafi tare.
12 And he said Jonathan to David Yahweh [the] God of Israel that I will sound out father my about this time - tomorrow the third and there! good [is] to David and not? then will I send to you and I will uncover ear your.
Sai Yonatan ya ce wa Dawuda, “Na yi rantse da Ubangiji, Allah na Isra’ila cewa war haka jibi, zan yi ƙoƙari in ji daga mahaifina, idan ya yi magana mai kyau game da kai, zan gaya maka.
13 Thus may he do Yahweh to Jonathan and thus may he add if it will make good to father my harm on you and I will uncover ear your and I will send away you and you will go to peace and may he be Yahweh with you just as he has been with father my.
Amma in mahaifina ya sa zuciya yă cuce ka, Ubangiji yă hukunta ni da hukunci mai tsanani in ban gaya maka ba, in kuma sa ka ka tafi lafiya. Ubangiji yă kasance tare da kai kamar yadda ya kasance da mahaifina.
14 And not if still I [am] alive and not you will do with me [the] covenant loyalty of Yahweh and not I will die.
Amma ka nuna mini alheri marar ƙarewa iri ta Ubangiji dukan rayuwata don kada a kashe ni.
15 And not you must cut off covenant loyalty your from with house my until perpetuity and not when cuts off Yahweh [the] enemies of David everyone from on [the] surface of the earth.
Kada kuma ka yanke alherinka ga iyalina ko da Ubangiji ya hallaka dukan maƙiyin Dawuda a duniya.”
16 And he made Jonathan with [the] house of David and he will require Yahweh from [the] hand of [the] enemies of David.
Saboda haka Yonatan ya yi yarjejjeniya da gidan Dawuda cewa Ubangiji yă kawo dukan maƙiyin Dawuda ga mutuwa.
17 And he repeated Jonathan to make swear an oath David in love his him for [the] love of own self his he loved him.
Yonatan kuwa ya sa Dawuda ya sāke tabbatar masa rantsuwansa game da abokantakarsa da shi, gama yana ƙaunar Dawuda kamar ransa.
18 And he said to him Jonathan [will be] tomorrow a new moon and you will be missed if it will be empty seat your.
Sai Yonatan ya gaya wa Dawuda cewa, “Gobe ne Bikin Sabon Wata, za a rasa ka, da yake kujerarka za tă kasance ba kowa a kai.
19 And you will do three times you will come down exceedingly and you will come to the place where you hid yourself there on [the] day of the deed and you will stay beside the stone Ezel.
Jibi wajajen yamma, ka tafi wurin da ka ɓuya lokacin da wannan matsala ta fara, ka tsaya kusa da dutsen Etsel.
20 And I [the] three the arrows [its] side I will shoot to send [them] for myself to a target.
Zan harbi kibiya uku ta wajen, sai ka ce dai ina harbin baka.
21 And there! I will send the lad go find the arrows certainly [if] I will say to the lad there! the arrows - [are] from you and hither fetch it - and come! for safety [belongs] to you and there not [is] anything [by] [the] life of Yahweh.
Sa’an nan zan aiki yaro in ce masa, ‘Je ka nemo kibiyoyin.’ In na ce masa, ‘Duba, kibiyoyin suna wannan gefen da kake, kawo su,’ sai ka fito, wato, tabbatacce muddin Ubangiji yana raye, ka tsira, ba wani hatsari.
22 And if thus I will say to the young man there! the arrows [are] from you and beyond go for he has sent away you Yahweh.
Amma in na ce wa yaron, ‘Duba, kibiyoyin suna gaba da kai,’ sai ka tafi, gama Ubangiji ya sallame ka.
23 And the matter which we have spoken I and you here! Yahweh [will be] between me and between you until perpetuity.
Game da al’amarin da muka tattauna da ni da kai kuwa, ka tuna fa Ubangiji ne shaida tsakanina da kai har abada.”
24 And he hid himself David in the field and it was the new moon and he sat down the king (to *Q(K)*) the food to eat.
Dawuda ya tafi ya ɓuya a fili. Sa’ad da ranar Bikin Sabon Wata ta zo, sarki ya zauna don yă ci.
25 And he sat down the king on seat his as time - on time to [the] seat of the wall and he arose Jonathan and he sat down Abner from [the] side of Saul and it was empty [the] place of David.
Ya zauna a kujeransa inda ya saba zama kusa da bango yana fuskantar Yonatan, Abner kuma ya zauna kusa da sarki. Amma kujeran Dawuda ba kowa.
26 And not he spoke Saul anything on the day that for he said [is] an accident it not [is] clean he for not clean.
Shawulu bai ce kome ba a ranar domin ya yi tsammani wataƙila wani abu ya faru da Dawuda ya mai da shi marar tsarki, tabbatacce ba shi da tsarki.
27 And it was from [the] next day of the new moon second and it was empty [the] place of David. And he said Saul to Jonathan son his why? not has he come [the] son of Jesse both yesterday as well as this day to the food.
Amma kashegari, rana ta biyu ga wata, kujeran Dawuda kuma ba kowa, sai Shawulu ya ce wa ɗansa Yonatan, “Me ya sa ɗan Yesse bai zo cin abinci, jiya da yau ba?”
28 And he answered Jonathan Saul certainly he asked for himself David from with me to Beth-lehem.
Yonatan ya ce, “Dawuda ya nemi izinina don yă tafi Betlehem.
29 And he said let go me please for a sacrifice of [the] clan [belongs] to us in the city and he he has commanded to me brother my and therefore if I have found favor in view your let me slip away please so I may see brothers my there-fore not he has come to [the] table of the king.
Ya ce, ‘Bari in tafi gama iyalinmu suna miƙa hadaya a gari,’yan’uwana kuwa sun gayyace ni in kasance a can. In na sami yardarka, bari in tafi in ga’yan’uwana.’ Dalilin ke nan da bai zo ci da sarki ba.”
30 And it burned [the] anger of Saul on Jonathan and he said to him O son of perverse [woman] of rebelliousness ¿ not do I know that [are] choosing you [the] son of Jesse to own shame your and to [the] shame of [the] nakedness of mother your.
Fushin Shawulu ya ƙuna a kan Yonatan, sai ya ce masa, “Kai shege ne, haihuwar banzan mace; ai, na san kana goyon bayan ɗan Yesse don ka wulaƙantar da kanka da mahaifinka.
31 For all the days which [the] son of Jesse he lives on the earth not you will be established you and kingdom your and therefore send and fetch him to me for [is] a son of death he.
Muddin ɗan Yesse yana da rai a duniya, ba za ka kahu ba. Sarautarka kuma ba za tă kahu ba. Yanzu sai ka je ka kawo mini shi. Dole yă mutu.”
32 And he answered Jonathan Saul father his and he said to him why? will he be put to death what? has he done.
Yonatan ya ce wa mahaifinsa, “Me ya sa zai mutu? Me ya yi?”
33 And he threw Saul the spear on him to strike him and he knew Jonathan that it had been determined it from with father his to kill David.
Amma Shawulu ya jefe shi da māshi don yă kashe shi. A nan ne Yonatan ya san lalle mahaifinsa ya yi niyya yă kashe Dawuda.
34 And he arose Jonathan from with the table in [the] heat of anger and not he ate on [the] day of the new moon second food for he was grieved concerning David for he had put to shame him father his.
Yonatan ya tashi daga tebur cin abincin da fushi. A rana ta biyun kuwa bai ci abinci ba, gama yana baƙin ciki game da rashin kunyar mahaifinsa game da Dawuda.
35 And it was in the morning and he went out Jonathan the field to [the] appointed time of David and a lad small [was] with him.
Da safe Yonatan ya tafi domin yă sadu da Dawuda a fili. Ya tafi tare da wani ƙaramin yaro.
36 And he said to lad his run find please the arrows which I [am] about to shoot the lad he ran and he he shot the arrow to make [it] pass beyond him.
Ya ce wa yaron, “Yi ruga da gudu ka nemo kibiyoyin da na harba.” Da yaron ya ruga sai ya harba kibiya a gaba da shi.
37 And he came the lad to [the] place of the arrow which he had shot Jonathan and he called out Jonathan after the lad and he said ¿ not [is] the arrow from you and beyond.
Da yaron ya isa wurin da kibiyan Yonatan ya fāɗi, Yonatan ya kira shi ya ce, “Kibiyan na gabanka fa.”
38 And he called out Jonathan after the lad quickly make haste! may not you delay and he picked up [the] lad of Jonathan (the arrows *Q(K)*) and he came to master his.
Sai ya tā da murya ya ce, “Maza, yi sauri kada ka tsaya.” Yaron ya ɗauko kibiya ya kawo wa maigidansa.
39 And the lad not he knew anything only Jonathan and David they knew the matter.
(Yaron kuwa bai san kome game da wannan abu ba, sai Yonatan da Dawuda kawai.)
40 And he gave Jonathan weapons his to the lad who [belonged] to him and he said to him go take [them] the city.
Yonatan ya ba wa yaron makaman ya ce, “Ka ɗauka ka koma gari.”
41 The lad he went and David he arose from beside the south and he fell to face his [the] ground towards and he bowed down three times and they kissed - each friend his and they wept for each friend his until David he did great things.
Da yaron ya tafi, sai Dawuda ya tashi daga inda ya ɓuya kusa da tarin duwatsu, ya rusuna har sau uku. Sa’an nan suka sumbaci juna, suka yi kuka, Dawuda kuwa ya yi kuka sosai.
42 And he said Jonathan to David go to peace that we have sworn an oath [the] two of us we by [the] name of Yahweh saying Yahweh he will be - between me and between you and between offspring my and between offspring your until perpetuity. And he arose and he went and Jonathan he went the city.
Yonatan ya ce wa Dawuda, “Sauka lafiya, mun riga mun yi rantsuwar abokantaka da juna a cikin sunan Ubangiji cewa, ‘Ubangiji ne shaida tsakanina da kai, tsakanin zuriyarka da zuriyata har abada.’” Sai Dawuda ya tafi, Yonatan kuwa ya koma gari.

< 1 Samuel 20 >