< 1 Samuel 15 >
1 And he said Samuel to Saul me he sent Yahweh to anoint you to king over people his over Israel and therefore listen to [the] voice of [the] words of Yahweh.
Sama’ila ya ce wa Shawulu, “Ni ne wanda Ubangiji ya aika in shafe ka ka zama sarki bisa mutanensa Isra’ila. Saurara yanzu ka ji saƙo daga wurin Ubangiji.
2 Thus he says Yahweh of hosts I have paid attention to [that] which it did Amalek to Israel [that] which it set to it on the way when came up it from Egypt.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Zan hori Amalekawa saboda abin da suka yi wa Isra’ila sa’ad da suka ba su wahala yayinda suka fito daga Masar.
3 Now go and you will attack Amalek and you will totally destroy all that [belongs] to it and not you must have compassion on it and you will put to death from a man unto a woman from a child and unto a suckling-child from an ox and unto a sheep from a camel and unto a donkey.
Yanzu ka tafi ka yaƙi Amalekawa, ka hallaka kome da yake nasu, kada ka bar su da rai, ka kashe maza, da mata, da yara, da jarirai, da dabbobi, da tumaki, da raƙuma, da kuma jakuna.’”
4 And he summoned Saul the people and he mustered them at Telaim two hundred thousand foot soldier[s] and ten thousand with man of Judah.
Sai Shawulu ya tattara sojoji, ya ƙidaya su a Telayim, ya sami su dubu ɗari biyu da dubu goma daga Yahuda.
5 And he came Saul to [the] city of Amalek and he lay in wait in the wadi.
Shawulu ya tafi birnin Amalek ya yi kwanto a kwari.
6 And he said Saul to the Kenite[s] go depart go down from among [the] Amalekite[s] lest I should destroy you with it and you you did loyalty with all [the] people of Israel when came up they from Egypt and it departed [the] Kenite[s] from among Amalek.
Sai Shawulu ya ce wa Keniyawa, “Ku tashi ku bar Amalekawa don kada in hallaka ku tare da su, saboda kun yi wa dukan Isra’ilawa kirki, lokacin da suka fito daga Masar.” Saboda haka Keniyawa suka tashi suka bar Amalekawa.
7 And he attacked Saul Amalek from Havilah coming you Shur which [is] on [the] face of Egypt.
Sa’an nan Shawulu ya ci Amalekawa da yaƙi tun daga Hawila har zuwa Shur, a gabashin iyakar Masar.
8 And he seized Agag [the] king of Amalek alive and all the people he totally destroyed to [the] mouth of [the] sword.
Ya kama Agag sarkin Amalekawa da rai. Ya kuma hallaka dukan mutanensa da takobi.
9 And he had compassion Saul and the people on Agag and on [the] best of the sheep and the cattle and the second and on the lambs and on all the good and not they were willing to totally destroy them and all the property despised and worthless it they totally destroyed.
Amma Shawulu da sojojinsa suka bar Agag, da tumaki, da shanu, da’yan maruƙa masu ƙiba da kuma duk abin da yake mai kyau da rai. Waɗannan ba su so su hallaka su gaba ɗaya ba, amma duk abin da ba a so da kuma marar amfani suka hallaka.
10 And it came [the] word of Yahweh to Samuel saying.
Sai Ubangiji ya yi magana da Sama’ila ya ce,
11 I regret that I have made king Saul to king for he has turned back from after me and words my not he has carried out and it burned to Samuel and he cried out to Yahweh all the night.
“Na damu da na naɗa Shawulu sarki, domin ya juya mini baya, bai kuma bi umarnina ba.” Sama’ila ya damu ƙwarai, ya yi kuka ga Ubangiji dukan dare.
12 And he rose early Samuel to meet Saul in the morning and it was told to Samuel saying he came Saul Carmel towards and there! [he was] setting up for himself a monument and he turned and he passed on and he went down Gilgal.
Kashegari da sassafe sai Sama’ila ya tashi ya tafi domin yă sadu da Shawulu, amma aka gaya masa cewa Shawulu ya tafi Karmel. A can ya yi wa kansa abin tunawa don yă girmama kansa, daga can kuma ya juya ya gangara zuwa Gilgal.
13 And he came Samuel to Saul and he said to him Saul [be] blessed you by Yahweh I have carried out [the] word of Yahweh.
Da Sama’ila ya kai wurinsa, sai Shawulu ya ce, “Ubangiji yă albarkace ka, na aikata umarnin Ubangiji.”
14 And he said Samuel and what? [is] [the] sound of the sheep this in ears my and [the] sound of the cattle which I [am] hearing.
Amma Sama’ila ya ce, “Ashe, waɗannan ba kukan tumaki ke nan nake ji a kunnena ba? Wane kuka shanu ke nan nake ji?”
15 And he said Saul from [the] Amalekite[s] people brought them that it had compassion the people on [the] best of the sheep and the cattle so as to sacrifice [them] to Yahweh God your and the rest we totally destroyed.
Shawulu ya amsa ya ce, “Sojoji ne suka kawo su daga Amalekawa. Sun bar tumaki da shanu masu kyau da rai don su yi wa Ubangiji Allahnka hadaya, amma sauran mun hallaka duka.”
16 And he said Samuel to Saul be quiet so let me tell to you [that] which he said Yahweh to me this night (and he said *Q(K)*) to him speak.
Sama’ila ya ce, “Dakata, bari in faɗa maka abin da Ubangiji ya ce mini jiya da dare.” Shawulu ya ce, “Gaya mini.”
17 And he said Samuel ¿ not though [were] small you in own eyes your [the] head of [the] tribes of Israel [are] you and he anointed you Yahweh to king over Israel.
Sama’ila ya ce, “Ko da yake kana ganin kanka kai ba wani abu ne ba, ashe, ba kai ne yanzu shugaban kabilan Isra’ila ba? Ubangiji ya shafe ka ka zama sarkin Isra’ila.
18 And he sent you Yahweh on a journey and he said go and you will totally destroy the sinners Amalek and you will wage war against it until destroy they them.
Shi kuma ya aika, ya umarce ka cewa, ‘Tafi ka hallaka Amalekawa mugayen mutanen nan duka, ka yaƙe su sai ka share su ƙaf.’
19 And why? not did you listen to [the] voice of Yahweh and did you rush? to the plunder and did you do? the evil in [the] eyes of Yahweh.
Me ya sa ba ka bi umarnin Ubangiji ba? Me ya sa ka sa hannu a ganima, ka kuma yi mugun abu a gaban Ubangiji?”
20 And he said Saul to Samuel that I listened to [the] voice of Yahweh and I went on the journey which he sent me Yahweh and I brought Agag [the] king of Amalek and Amalek I totally destroyed.
Shawulu ya ce, “Amma na bi umarnin Ubangiji. Na bi saƙon da Ubangiji ya ba ni. Na hallaka Amalekawa, na kuma kamo Agag sarkinsu.
21 And it took the people from the plunder sheep and cattle [the] choicest of the object[s] for destruction to sacrifice [them] to Yahweh God your in Gilgal.
Sojoji suka kawo tumaki da shanu mafi kyau daga cikin ganimar domin a miƙa hadaya ga Ubangiji Allahnka a Gilgal.”
22 And he said Samuel ¿ [does] delight [belong] to Yahweh in burnt offerings and sacrifices like listening to [the] voice of Yahweh here! to obey more than sacrifice [is] good to pay attention more than [the] fat of rams.
Amma Sama’ila ya ce, “Ubangiji yana murna da sadaka da hadaya fiye da biyayya ga maganar Ubangiji? Yin biyayya ta fi hadaya a kula kuma ta fi ƙibabbun raguna.
23 For [is the] sin of divination rebellion and [is] wickedness and teraphim presumption because you have rejected [the] word of Yahweh and he has rejected you from king.
Gama tawaye yana kama da zunubi na duba, girman kai kuma yana kama da bautar gumaka. Saboda ka ƙi maganar Ubangiji, shi ma ya ƙi ka da zaman sarki.”
24 And he said Saul to Samuel I have sinned for I have transgressed [the] mouth of Yahweh and words your for I feared the people and I listened to voice their.
Sai Shawulu ya ce wa Sama’ila, “Na yi zunubi, na ƙi bin umarnin Ubangiji, na kuma ƙi bin maganarka. Na ji tsoron mutane ne shi ya sa na bi maganarsu.
25 And therefore forgive please sin my and return with me so I may bow down to Yahweh.
Yanzu fa, ina roƙonka ka yafe mini zunubina, ka koma tare da ni, domin in yi wa Ubangiji sujada.”
26 And he said Samuel to Saul not I will return with you for you have rejected [the] word of Yahweh and he has rejected you Yahweh from being king over Israel.
Amma Sama’ila ya ce, “Ba zan koma tare da kai ba. Ka ƙi maganar Ubangiji, Ubangiji kuma ya ƙi ka da zama sarki a bisa Isra’ila.”
27 And he turned round Samuel to go and he took hold on [the] skirt of robe his and it tore.
Da Sama’ila ya juya zai tafi, sai Shawulu ya kama bakin rigarsa, sai rigar ta yage.
28 And he said to him Samuel he has torn Yahweh [the] kingdom of Israel from with you this day and he will give it to neighbor your good more than you.
Sama’ila ya ce masa, “Ubangiji ya yage masarautar Isra’ila daga gare ka yau, ya ba wa wani daga cikin maƙwabtanka wanda ya fi ka.
29 And also [the] eminence of Israel not he will deal falsely and not he will regret for not [is] a man he to regret.
Shi wanda yake Ɗaukakar Isra’ila ba ya ƙarya ko yă canja zuciyarsa, gama shi ba mutum ba ne da zai canja zuciyarsa.”
30 And he said I have sinned now honor me please before [the] elders of people my and before Israel and return with me and I will bow down to Yahweh God your.
Shawulu ya ce, “Na yi zunubi. Amma ina roƙonka ka ba ni girma a gaban dattawan mutanena da kuma a gaban Isra’ila, ka koma tare da ni domin in yi wa Ubangiji Allahnka sujada.”
31 And he turned back Samuel after Saul and he bowed down Saul to Yahweh.
Saboda haka sai Sama’ila ya koma tare da Shawulu, Shawulu kuwa ya yi wa Ubangiji sujada.
32 And he said Samuel bring near to me Agag [the] king of Amalek and he came to him Agag bonds and he said Agag truly it has departed [the] bitterness of death.
Sa’an nan Sama’ila ya ce, “Kawo mini Agag sarkin Amalekawa.” Agag kuwa ya zo wurinsa daure da sarƙa, yana tunani cewa, “Tabbatacce zancen mutuwa dai ya wuce.”
33 And he said Samuel just as it has made childless women sword your so she will become childless from women mother your and he cut to pieces Samuel Agag before Yahweh in Gilgal.
Amma Sama’ila ya ce, “Yadda takobinka ya sa mata suka rasa’ya’ya, haka mahaifiyarka za tă zama marar’ya’ya a cikin mata.” Sama’ila kuwa ya kashe Agag a Gilgal a gaban Ubangiji.
34 And he went Samuel Ramah towards and Saul he went up to house his Gibeah of Saul.
Sai Sama’ila ya tafi Rama, amma Shawulu ya haura zuwa gidansa a Gibeya na Shawulu.
35 And not he repeated Samuel to see Saul until [the] day of death his for he mourned Samuel concerning Saul and Yahweh he regretted that he had made king Saul over Israel.
Daga wannan rana Sama’ila bai ƙara saduwa da sarki Shawulu ba, har rasuwar Sama’ila, amma ya yi baƙin ciki sosai a kan Shawulu. Ubangiji kuwa ya damu da ya sa Shawulu ya zama Sarkin Isra’ila ba.