< 1 Chronicles 5 >
1 And [the] sons of Reuben [the] firstborn of Israel for he [was] the firstborn and when profaned he [the] beds of father his it was given birthright his to [the] sons of Joseph [the] son of Israel and not to have themselves enrolled to the birthright.
’Ya’yan Ruben maza ɗan farin Isra’ila (shi ne ɗan fari, amma sa’ad da ya ƙazantar da gadon auren mahaifinsa, sai aka ba wa’yancin ɗan farinsa wa’ya’yan Yusuf maza ɗan Isra’ila; don kada a lissafta shi a tarihin zuriya bisa ga matsayin haihuwarsa,
2 For Judah he was strong among brothers his and to a leader [was] from him and the birthright [belonged] to Joseph.
ko da yake Yahuda shi ne mafi ƙarfi cikin’yan’uwansa kuma mai mulki ya fito daga gare shi,’yancin zaman ɗan fari na Yusuf ne),
3 [the] sons of Reuben [the] firstborn of Israel Hanoch and Pallu Hezron and Carmi.
’ya’yan Ruben ɗan farin Isra’ila maza su ne, Hanok, Fallu, Hezron da Karmi.
4 [the] descendants of Joel Shemaiah son his Gog son his Shimei son his.
Zuriyar Yowel su ne, Shemahiya, Gog, Shimeyi,
5 Micah son his Reaiah son his Baal son his.
Mika, Reyahiya, Ba’al,
6 Beerah son his whom he took into exile Tiglath-pileser [the] king of Assyria he [was] a leader of the Reubenite[s].
da Beyera, wanda Tiglat-Fileser sarkin Assuriya ya ɗauka zuwa zaman bauta. Beyera shi ne shugaban mutanen Ruben.
7 And relatives his to clans his by genealogical enrolment to generations their [were] the chief Jeiel and Zechariah.
Danginsu bisa ga iyalansu da aka jera bisa ga tarihin zuriyarsu su ne, Yehiyel shi ne sarki, akwai Zakariya,
8 And Bela [the] son of Azaz [the] son of Shema [the] son of Joel he [was] dwelling in Aroer and to Nebo and Baal Meon.
da Bela ɗan Azaz. Azaz ɗan Shema daga dangin Yowel. Yowel ya yi zama a yankin Arower har zuwa Nebo da Ba’al-Meyon.
9 And to the east he dwelt till to [the] entrance of [the] wilderness from the river Euphrates for livestock their they had increased in [the] land of Gilead.
Ta waje gabas sun zauna a ƙasar har zuwa bakin hamadan da ya nausa zuwa Kogin Yuferites, domin dabbobinsu sun ƙaru a Gileyad.
10 And in [the] days of Saul they made war with the Hagrites and they fell by hand their and they dwelt in tents their on all [the] face of [the] east of Gilead.
A zamanin Shawulu zuriyar Ruben sun yi yaƙi da Hagirawa, suka ci su da yaƙi, suka zauna a wuraren zaman Hagirawan ko’ina a dukan yankin gabashin Gileyad.
11 And [the] descendants of Gad to before them they dwelt in [the] land of Bashan to Salecah.
Mutanen Gad sun zauna kusa da mutanen Ruben a Bashan, har zuwa Saleka.
12 Joel [was] the chief and Shapham [was] the second and Janai and Shaphat in Bashan.
Yowel shi ne babba, sai Shafan na biyu, sa’an nan Yanai da Shafat, su ne tushen Bashan.
13 And relatives their to [the] house of ancestors their Michael and Meshullam and Sheba and Jorai and Jakan and Zia and Eber seven.
Danginsu, bisa ga iyalai su ne, Mika’ilu, Meshullam, Sheba, Yorai, Yakan, Ziya da Eber, su bakwai ne duka.
14 These - [were] [the] sons of Abihail [the] son of Huri [the] son of Jaroah [the] son of Gilead [the] son of Michael [the] son of Jeshishai [the] son of Jahdo [the] son of Buz.
Waɗannan su ne’ya’yan Abihayil ɗan Huri, ɗan Yarowa, ɗan Gileyad, ɗan Mika’ilu, ɗan Yeshishai, ɗan Yado, ɗan Buz.
15 Ahi [the] son of Abdiel [the] son of Guni [was] chief of [the] house of ancestors their.
Ahi ɗan Abiyel, ɗan Guni, shi ne kan iyalinsu.
16 And they dwelt in Gilead in Bashan and in daughters its and in all [the] pasture lands of Sharon on (extremities their. *LA(bh)*)
Mutanen Gad sun zauna a Bashan da ƙauyukan da suke kurkusa da shi, da kuma a dukan makiyayan Sharon har zuwa iyaka inda suka kai.
17 All of them they had themselves enrolled in [the] days of Jotham [the] king of Judah and in [the] days Jeroboam [the] king of Israel.
Dukan waɗannan sun shiga tarihin zuriya a lokacin mulkin Yotam sarkin Yahuda da Yerobowam sarkin Isra’ila.
18 [the] descendants of Reuben and [the] Gadite[s] and [the] half of [the] tribe of Manasseh from [the] sons of strength men [who] carried shield and sword and [who] bent a bow and [who] were trained of warfare forty and four thousand and seven hundred and sixty [those who] went forth of war.
Mutanen Ruben, mutanen Gad da rabin kabilar Manasse sun kasance da mutane 44,760 shiryayyu don aikin soja, jarumawan da za su iya riƙe garkuwa da takobi, waɗanda suke iya yin amfani da baka, waɗanda kuma aka horar don yaƙi.
19 And they made war with the Hagrites and Jetur and Naphish and Nodab.
Suka yi yaƙi da Hagirawa, Yetur, Nafish da Nodab.
20 And they were helped on them and they were given in hand their the Hagrites and all [those] who [were] with them for to God they had cried out in the battle and he was entreated by them for they trusted in him.
Aka taimake su a yaƙin, Allah kuma ya ba da Hagirawa da dukan abokansu gare su, domin sun yi kuka gare shi a lokacin yaƙin. Ya amsa addu’o’insu, domin sun dogara gare shi.
21 And they took captive livestock their camels their fifty thousand and sheep two hundred and fifty thousand and donkeys two thousand and person[s] of humankind one hundred thousand.
Suka ƙwace dabbobin Hagirawa, raƙuma dubu hamsin, tumaki dubu ɗari biyu da hamsin da kuma jakuna dubu biyu. Suka kuma kame mutane dubu ɗari ɗaya,
22 For slain [ones] many they fell for [was] from God the battle and they dwelt in place of them until the exile.
waɗansu suka mutu, domin yaƙin na Allah ne. Suka zauna a ƙasar har lokacin da aka kai su zaman bauta.
23 And [the] descendants of [the] half of [the] tribe of Manasseh they dwelt in the land from Bashan to Baal Hermon and Senir and [the] mountain of Hermon they they multiplied.
Mutanen rabin kabilar Manasse sun yi yawa; suka zauna a ƙasar daga Bashan har zuwa Ba’al-Hermon, wato, zuwa Senir (Dutsen Hermon).
24 And these [were] [the] chiefs of [the] house of ancestors their and Epher and Ishi and Eliel and Azriel and Jeremiah and Hodaviah and Jahdiel men mighty of strength men of names chiefs of [the] house of ancestors their.
Waɗannan su ne kawunan iyalansu. Efer, Ishi, Eliyel, Azriyel, Irmiya, Hodawiya da Yadiyel. Su jarumawa ne, sanannu, su ne kuma kawunan iyalansu.
25 And they acted unfaithfully against [the] God of ancestors their and they played [the] prostitute after [the] gods of [the] peoples of the land which he had destroyed God from before them.
Amma ba su yi aminci da Allahn kakanninsu ba, suka kuma yi karuwanci ga waɗansu allolin mutanen ƙasar, waɗanda Allah ya hallaka a gabansu.
26 And he stirred up [the] God of Israel [the] spirit of - Pul [the] king of Assyria and [the] spirit of Tiglath-pileser [the] king of Assyria and he took into exile them to the Reubenite[s] and to the Gadite[s] and to [the] half of [the] tribe of Manasseh and he brought them to Halah and Habor and Hara and [the] river of Gozan until the day this.
Saboda haka Allah na Isra’ila ya zuga ruhun Ful sarkin Assuriya (wato, Tiglat-Fileser sarkin Assuriya), wanda ya kwashe mutanen Ruben, mutanen Gad da rabin kabilar Manasse zuwa zaman bauta. Ya kwashe su zuwa Hala, Habor, Hara da kuma kogin Gozan, inda suke har wa yau.