< 1 Chronicles 28 >

1 And he called together David all [the] officials of Israel [the] leaders of the tribes and [the] commanders of the divisions who served the king and [the] commanders of the thousands and [the] commanders of the hundreds and [the] officials of all [the] property and livestock - of the king and of sons his with the court-officials and the mighty [men] and to every mighty [man] of strength to Jerusalem.
Dawuda ya sa aka kira dukan shugabannin Isra’ila su taru a Urushalima, shugabannin kabilu, manyan hafsoshin ɓangarorin hidimar sarki, manyan hafsoshin dubu-dubu da manyan hafsoshin ɗari-ɗari, da kuma shugabanni masu lura da dukan mallaka da dabbobin da suke na sarki da kuma’ya’yansa maza, tare da fadawa, jarumawa da kuma dukan mayaƙa masu kwarjini.
2 And he arose David the king on feet his and he said listen to me O brothers my and people my I [was] with heart my to build a house of rest for [the] ark of [the] covenant of Yahweh and to [the] footstool of [the] feet of God our and I prepared to build.
Sarki Dawuda ya miƙe tsaye ya ce, “Ku saurare ni,’yan’uwana da kuma mutanena. Na yi niyya in gina gida a matsayin wurin hutu domin akwatin alkawarin Ubangiji, domin zatin Allahnmu, na kuma yi shiri don in gina shi.
3 And God he said to me not you will build a house for name my for [are] a man of wars you and blood you have shed.
Amma Allah ya ce mini, ‘Ba za ka gina gida domin Sunana ba, saboda kai mayaƙi ne ka kuma zub da jini.’
4 And he chose Yahweh [the] God of Israel me from all [the] house of father my to become king over Israel for ever for Judah he chose to ruler and among [the] house of Judah [the] house of father my and among [the] sons of father my in me he took pleasure to make [me] king over all Israel.
“Duk da haka Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya zaɓe ni daga dukan iyalina don in zama sarki bisa Isra’ila har abada. Ya zaɓi Yahuda a matsayin shugaba, kuma daga gidan Yahuda ya zaɓi iyalina, daga’ya’yan mahaifina maza kuwa ya gamsu ya mai da ni sarki bisa dukan Isra’ila.
5 And from all sons my for many sons he has given to me Yahweh and he has chosen Solomon son my to sit on [the] throne of [the] kingdom of Yahweh over Israel.
Cikin dukan’ya’yana maza, Ubangiji kuwa ya ba ni su da yawa, ya zaɓi ɗana Solomon yă zauna a kujerar mulkin Ubangiji a bisa Isra’ila.
6 And he said to me Solomon son your he he will build house my and courts my for I have chosen him for myself to a son and I I will become of him a father.
Ya ce mini, ‘Solomon ɗanka shi ne wanda zai gina gidana da filayen da suke kewaye da shi, gama na zaɓe shi yă zama ɗana, ni kuma zan zama mahaifinsa.
7 And I will establish kingdom his until for ever if he will be strong to observe commandments my and judgments my as the day this.
Zan kafa mulkinsa har abada in bai kauce ga kiyaye umarnaina da dokokina ba, yadda ake yi a wannan lokaci.’
8 And therefore to [the] eyes of all Israel [the] assembly of Yahweh and in [the] ears of God our observe and seek all [the] commandments of Yahweh God your so that you may possess the land good and you will give [it] as inheritance to descendants your after you until perpetuity.
“Saboda haka yanzu ina umartanku a gaban dukan Isra’ila da na taron jama’ar Ubangiji, da kuma a kunnuwan Allahnmu. Ku yi hankali ku kiyaye dukan umarnan Ubangiji Allahnku don ku mallaki wannan kyakkyawar ƙasa ku kuma bar wa zuriyarku gādo har abada.
9 And you O Solomon son my know [the] God of father your and serve him with a heart complete and with a being willing for all hearts [is] searching Yahweh and every inclination of thoughts [he is] understanding if you will seek him he will let himself be found by you and if you will forsake him he will reject you for ever.
“Kai kuma ɗana Solomon, ka san Allah na mahaifinka, ka kuma yi masa hidima da dukan zuciya da kuma yardar rai, gama Ubangiji yana binciken zuciya, yana kuma gane dukan aniyar tunani. In ka neme shi, za ka same shi; amma in ka yashe shi, zai ƙi ka har abada.
10 See - now that Yahweh he has chosen you to build a house for the sanctuary be strong and act.
Ka lura fa, gama Ubangiji ya zaɓe ka don ka gina haikali a matsayin wuri mai tsarki. Ka yi ƙarfin hali ka kuma yi aiki.”
11 And he gave David to Solomon son his [the] pattern of the porch and houses its and treasuries its and upper rooms its and rooms its inner and [the] house of the atonement cover.
Sa’an nan Dawuda ya ba ɗansa Solomon tsari domin shirayin haikalin, gine-ginensa, ɗakunan ajiyarsa, ɓangarorin bisansa, ɗakunan cikinsa da kuma wurin kafara.
12 And [the] pattern of all that it was in the spirit with him for [the] courts of [the] house of Yahweh and for all the rooms all around for [the] storehouses of [the] house of God and for [the] storehouses of the holy things.
Ya ba shi tsarin dukan abin da Ruhu ya sa a zuciyarsa saboda filayen haikalin Ubangiji da ɗakunan kewaye, da ma’ajin haikalin Allah da kuma baitulmali na kayayyakin da aka keɓe.
13 And for [the] divisions of the priests and the Levites and for all [the] work of [the] service of [the] house of Yahweh and for all [the] articles of [the] service of [the] house of Yahweh.
Ya ba shi tsari game ɓangarori na firistoci da Lawiyawa, da game dukan aikin hidima a cikin haikalin Ubangiji, da kuma game da dukan kayayyakin da za a yi amfani da su a hidima.
14 For the gold by the weight of the gold for all articles of service and service for all [the] articles of silver by weight for all articles of service and service.
Ya kimanta yawan zinariya don dukan kayayyakin zinariyar da za a yi amfani a kowane irin hidima, da yawan azurfa don dukan kayayyakin azurfan da za a yi amfani a kowace irin hidima.
15 And [the] weight of [the] lampstands of gold and lamps their gold by weight of a lampstand and a lampstand and lamps its and of [the] lampstands of silver by weight of a lampstand and lamps its according to [the] service of a lampstand and a lampstand.
Da yawan zinariya don wurin ajiye fitilan fitilu da fitilunsu, da yawan zinariyan da za a yi amfani don kowace fitila da wurin ajiye fitilanta; da kuma yawan azurfa don kowane wurin ajiye fitila da fitilunsa bisa ga yadda za a yi amfani da kowane wurin ajiye fitila;
16 And the gold weight for [the] tables of the row for a table and a table and silver for [the] tables of silver.
yawan zinariya don kowane tebur saboda burodi mai tsaki; da kuma yawan azurfa saboda teburin azurfa;
17 And the forks and the bowls and the jugs gold pure and for [the] bowls of gold by weight for a bowl and a bowl and for [the] bowls of silver by weight for a bowl and a bowl.
yawan zinariya zalla, don cokula masu yatsu, kwanonin yayyafawa ruwa da kuma tuluna; yawan zinariya don kowane kwanon zinariya; yawan azurfa don kowane kwanon azurfa;
18 And for [the] altar of incense gold purified by weight and [the] pattern of the chariot the cherubim gold for spreading out and covering over [the] ark of [the] covenant of Yahweh.
da kuma yawan tacecciyar zinariya don bagaden turare. Ya kuma ba shi tsari don keken yaƙi, wato, kerubobin zinariyar da suka miƙe fikafikansu suka inuwantar da akwatin alkawarin Ubangiji.
19 Everything in writing from [the] hand of Yahweh on me he made clear all [the] works of the pattern.
Dawuda ya ce, “Dukan wannan, ina da shi a rubuce daga hannun Ubangiji zuwa gare ni, ya kuma ba ni ganewa cikin dukan tsarin fasalin, filla-filla.”
20 And he said David to Solomon son his be strong and be brave and act may not you be afraid and may not you be dismayed for Yahweh God God my [is] with you not he will abandon you and not he will forsake you until is complete all [the] work of [the] service of [the] house of Yahweh.
Dawuda ya kuma ce wa Solomon ɗansa, “Ka yi ƙarfin hali, ka kuma yi aikin. Kada ka ji tsoro ko ka fid da zuciya, gama Ubangiji Allah, Allahna, yana tare da kai. Ba zai bari ka ji kunya ko yă yashe ka ba, sai an gama dukan aikin saboda hidimar haikalin Ubangiji.
21 And there! [the] divisions of the priests and the Levites for all [the] service of [the] house of God and [will be] with you in all [the] work every willing [person] with skill for every service and the officials and all the people [are] to all words your.
Sassan firistoci da na Lawiyawa suna a shirye domin dukan aiki a haikalin Allah, kuma kowane gwani mai niyya a kowace sana’a, zai taimake ka a cikin dukan aikin. Shugabanni da dukan mutane za su yi biyayya da kowane umarninka.”

< 1 Chronicles 28 >