< 1 Chronicles 18 >

1 And it was after thus and he struck down David [the] Philistines and he subdued them and he took Gath and daughters its from [the] hand of [the] Philistines.
Ana nan sai Dawuda ya ci Filistiyawa ya kuma rinjaye su, ya ƙwace Gat da ƙauyukan kewayenta daga mulkin Filistiyawa.
2 And he struck down Moab and they became Moab subjects of David bearers of tribute.
Dawuda ya kuma ci Mowabawa, suka zama bayinsa suka kuma biya haraji.
3 And he struck down David Hadadezer [the] king of Zobah Hamath towards when went he to establish monument his at [the] river of Euphrates.
Ban da haka, Dawuda ya yaƙi Hadadezer sarkin Zoba, har can Hamat, sa’ad da ya je don yă kafa mulkinsa a wajen Kogin Yuferites.
4 And he captured David from him one thousand chariot[s] and seven thousand horsemen and twenty thousand man on foot and he hamstrung David all the chariotry and he left of it one hundred chariot[s].
Dawuda ya kame keken yaƙinsa dubu ɗaya, da mahayan kekunan yaƙi dubu bakwai da sojojin kafa guda dubu ashirin. Ya yayyanke dukan agaran dawakansa, amma ya bar dawakai da suka isa jan kekunan yaƙi ɗari.
5 And it came Aram Damascus to help Hadadezer [the] king of Zobah and he struck down David in Aram twenty and two thousand man.
Da Arameyawan Damaskus suka zo su taimaki Hadadezer sarkin Zoba, sai Dawuda ya bugi dubu ashirin da biyunsu.
6 And he put David in Aram Damascus and it became Aram of David subjects bearers of tribute and he gave victory Yahweh to David in every where he went.
Ya sa ƙungiyoyin sojoji a masarautar Arameyawan Damaskus. Arameyawan kuwa suka zama bayinsa, suka kuma kawo haraji. Ubangiji ya ba Dawuda nasara a ko’ina da ya tafi.
7 And he took David [the] shields of gold which they were on [the] servants of Hadadezer and he brought them Jerusalem.
Dawuda ya kwashe garkuwoyin zinariyan da shugabannin sojojin Hadadezer suke riƙe, ya kawo su Urushalima.
8 And from Tibhath and from Kun [the] cities of Hadadezer he took David bronze much very with it - he made Solomon [the] sea of bronze and the pillars and [the] articles of bronze.
Daga Teba da Kun, garuruwan da suke ƙarƙashin Hadadezer, Dawuda ya kwashe tagulla da yawa sosai, wanda Solomon ya yi amfani don yă yi Tekun tagulla, ginshiƙai da kuma kayayyakin tagulla dabam-dabam.
9 And he heard Tou [the] king of Hamath that he had struck down David all [the] army of Hadadezer [the] king of Zobah.
Sa’ad da Towu sarkin Hamat ya ji cewa Dawuda ya ci mayaƙan Hadadezer sarkin Zoba gaba ɗaya,
10 And he sent Hadoram son his to the king David (to ask *Q(k)*) of him to welfare and to bless him on that he had fought against Hadadezer and he had defeated him for man of wars of Tou he was Hadadezer and all articles of gold and silver and bronze.
sai ya aiki ɗansa Hadoram zuwa wurin Sarki Dawuda yă gaishe shi yă kuma yi masa barka da nasara a yaƙi a kan Hadadezer, wanda yake yaƙi da Towu. Hadoram ya kawo kowane irin kayayyakin zinariya da na azurfa da na tagulla.
11 Also them he consecrated the king David to Yahweh with the silver and the gold which he had taken away from all the nations from Edom and from Moab and from [the] people of Ammon and from [the] Philistines and from Amalek.
Sarki Dawuda ya miƙa waɗannan kayayyakin ga Ubangiji, kamar yadda ya yi da azurfa da kuma zinariyan da ya kwaso daga dukan waɗannan al’ummai. Edom da Mowab, Ammonawa da Filistiyawa, da kuma Amalek.
12 And Abishai [the] son of Zeruiah he struck down Edom in [the] Valley of Salt eight-teen thousand.
Abishai ɗan Zeruhiya ya bugi mutanen Edom dubu goma sha takwas a Kwarin Gishiri.
13 And he put in Edom garrisons and they became all Edom subjects of David and he gave victory to Yahweh David in every where he went.
Ya sa ƙungiyoyin sojoji a Edom, dukan mutanen Edom kuwa suka zama bayin Dawuda. Ubangiji ya ba Dawuda nasara a ko’ina da ya tafi.
14 And he reigned David over all Israel and he was doing justice and righteousness for all people his.
Dawuda ya yi mulki a bisa dukan Isra’ila, yana yin abin da yake daidai da kuma gaskiya saboda dukan mutanensa.
15 And Joab [the] son of Zeruiah [was] over the army and Jehoshaphat [the] son of Ahilud [was the] recorder.
Yowab ɗan Zeruhiya shi ne shugaban mayaƙa; Yehoshafat ɗan Ahilud shi ne marubuci;
16 And Zadok [the] son of Ahitub and Abimelech [the] son of Abiathar [were] priests and Shavsha [was the] scribe.
Zadok ɗan Ahitub da Abimelek ɗan Abiyatar su ne firistoci; Shafsha shi ne magatakarda;
17 And Benaiah [the] son of Jehoiada [was] over the Kerethite[s] and the Pelethite[s] and [the] sons of David [were] the first to [the] side of the king.
Benahiya ɗan Yehohiyada shi ne shugaban Keretawa da Feletiyawa;’ya’yan Dawuda maza su ne manyan ma’aikata a gefen sarki.

< 1 Chronicles 18 >