< Revelation 8 >

1 And, as soon as he opened the seventh seal, there came to be silence in heaven, as it were half an hour.
Sa’ad da ya buɗe hatimi na bakwai, sai aka yi shiru a sama na kusan rabin sa’a.
2 And I saw the seven messengers which, before God, do stand; and there were given unto them seven trumpets.
Sai na ga mala’iku bakwai da suke tsayawa a gaban Allah, a gare su kuwa aka ba da ƙahoni bakwai.
3 And, another messenger, came, and took his stand at the altar, having a censer of gold: and there was given unto him much incense, that he might give [it] unto the prayers of all the saints, upon the altar of gold that is before the throne.
Wani mala’ika, da yake da kaskon zinariyar da ake zuba turare, ya zo ya tsaya kusa da bagaden. Aka ba shi turare da yawa don yă miƙa tare da addu’o’in dukan tsarkaka a bisa bagaden zinariya a gaban kursiyin.
4 And the smoke of the incense went up, with the prayers of the saints, out of the hand of the messenger before God.
Hayaƙin turaren tare da addu’o’in tsarkaka, suka hau zuwa gaban Allah daga hannun mala’ikan.
5 And the messenger at once took the censer, and filled it from the fire of the altar, and cast unto the earth; and there came to be thunderings, and voices, and lightnings, and an earthquake.
Sai mala’ikan ya ɗauki kaskon, ya cika shi da wuta daga bagaden, ya kuma wurga shi bisan duniya; sai aka yi ta yin tsawa, ƙararraki, walƙiya, da kuma girgizar ƙasa.
6 And, the seven messengers who had the seven trumpets, prepared themselves, that they might sound.
Sai mala’iku bakwai ɗin nan da suke da ƙahoni bakwai suka shirya don su busa su.
7 And, the first, sounded; and there came to be hail and fire mingled with blood, and it was cast unto the earth; and, the third of the earth, was burned up, and, the third of the trees, was burned up, and, all green herbage, was burned up.
Mala’ika na fari ya busa ƙahonsa, sai ga ƙanƙara da wuta haɗe da jini, aka kuma wurga su bisan duniya. Kashi ɗaya bisa uku na duniya ya ƙone, kashi ɗaya bisa uku na itatuwa suka ƙone, dukan ɗanyar ciyawa kuma ta ƙone.
8 And, the second messenger, sounded; and, as it were a great mountain burning with fire, was cast into the sea; and the third of the sea became blood,
Mala’ika na biyu ya busa ƙahonsa, sai ga wani abu kamar babban dutse mai cin wuta, aka jefa cikin teku. Kashi ɗaya bisa uku na teku ya zama jini,
9 and the third of the creatures which were in the sea, which had life, died, the third of the ships, was destroyed.
kashi ɗaya bisa uku na halittu masu rai da suke cikin tekun suka mutu, kashi ɗaya bisa uku kuma na jiragen ruwa kuma suka hallaka.
10 And, the third messenger, sounded; and there fell, out of heaven, a great star, burning as a torch, and it fell upon the third of the rivers, and upon the fountains of waters.
Mala’ika na uku ya busa ƙahonsa, sai wani babban tauraro mai cin wuta kamar toci, ya fāɗi daga sararin sama, a kan kashi ɗaya bisa uku na koguna da kuma a bisa maɓulɓulan ruwa
11 And, the name of the star, is called Wormwood; and the third of the waters became wormwood, and many of the men died of the waters, because they were made bitter.
sunan tauraron kuwa Maɗaci. Kashi ɗaya bisa uku na ruwaye ya zama mai ɗaci, mutane da yawa kuma suka mutu saboda shan ruwan, don ɗacinsa.
12 And, the fourth messenger, sounded; and the third of the sun was smitten, and the third of the moon, and the third of the stars, —in order that the third of them might be darkened, and the day might not shine for the third of it, and the night, in like manner.
Mala’ika na huɗu ya busa ƙahonsa, sai aka bugi kashi ɗaya bisa uku na rana, kashi ɗaya bisa uku na wata, da kashi ɗaya bisa uku na taurari, har kashi ɗaya bisa uku nasu ya duhunta. Kashi ɗaya bisa uku na yini ya kasance babu haske, haka ma kashi ɗaya bisan uku na dare.
13 And I saw, and I heard one eagle, flying in mid-heaven, saying with a loud voice—Woe! woe! woe! unto them that are dwelling upon the earth, by reason of the remaining voices of the trumpet, of the three messengers who are about to sound.
Yayinda nake kallo, sai na ji gaggafar da take tashi sama a tsakiyar sararin sama ta yi kira da babbar murya ta ce, “Kaito! Kaito! Kaiton mazaunan duniya, in an yi busan sauran ƙahonin da mala’ikun nan uku suke shirin busawa!”

< Revelation 8 >