< Psalms 90 >

1 A Prayer by Moses, the Man of God. Lord! a dwelling-place, hast, thou, become to us, From generation to generation:
Addu’ar Musa Mutumin Allah. Ubangiji kai ne mazauninmu cikin dukan zamanai.
2 Before, the mountains, were born, Or thou hadst brought forth the earth and the world, Even, from age to age, thou, [wast] GOD.
Kafin a haifi duwatsu ko a fid da ƙasa da duniya, daga madawwami zuwa madawwami kai Allah ne.
3 Thou causest man to return unto dust, And hast said—Return, ye sons of Adam!
Ka komar da mutane zuwa ƙura, kana cewa, “Ku koma ƙura, ya ku’ya’yan mutane.”
4 For, a thousand years, in thine eyes, [are], As yesterday, in that it passed away, Or [as] a watch in the night.
Gama shekaru dubu a gabanka kamar kwana ɗaya ne da ya wuce, ko sa’a guda na dare.
5 Thou hast snatched them away, A sleep, do they become, In the morning, [they are] like grass that shooteth up,
Ka share mutane cikin barcin mutuwa; suna kama da sabuwa ciyawar safiya,
6 In the morning, it sprouteth and shooteth up, By the evening, it is cut down and withered.
ko da yake da safe takan yi sabuwar huda da yamma sai ta bushe ta kuma yanƙwane.
7 For we are consumed in thine anger, And, in thy wrath, are we dismayed;
An cinye mu ta wurin fushinka mun kuma razana ta wurin hasalarka.
8 Thou hast set, Our iniquities before thee, Our secret near the luminary of thy face.
Ka ajiye laifinmu a gabanka, asirin zunubanmu a hasken kasancewarka.
9 For, all our days, decline in thy wrath, —We end our years like a sigh.
Dukan kwanakinmu sun wuce ƙarƙashin fushinka; mun gama shekarunmu da nishi.
10 The days of our years, have, in them, three score years and ten, And, if, by reason of strength, they have fourscore years, Yet, their boast, is labour and sorrow, For it hath passed quickly, and we have flown away.
Tsawon kwanakinmu shekaru saba’in ne, ko tamanin, in muna da ƙarfi; duk da haka tsawonsu wahaloli ne kawai da ɓacin rai, gama da sauri suke wucewa, ta mu kuma ta ƙare.
11 Who knoweth the strength of thine anger? Even, according to the fear of thee, is thy wrath!
Wa ya san ƙarfin fushinka? Gama hasalarka tana da girma kamar tsoron da ya dace da kai.
12 How to number our days, so grant us to know, That we may win us a heart that hath wisdom.
Ka koya mana yawan kwanakinmu daidai, don mu sami zuciyar hikima.
13 Return, Yahweh, oh how long? And have compassion upon thy servants;
Ka ji mu, ya Ubangiji! Har yaushe zai ci gaba? Ka ji tausayin bayinka.
14 Satisfy us, in the morning, with thy lovingkindness, That we may shout aloud and be glad, Throughout all our days.
Ka ƙosar da mu da safe da ƙaunarka marar ƙarewa, don mu rera don yabo, mu kuma yi murna dukan kwanakinmu.
15 Make us glad, according to, The days thou hast humbled us, The years we have seen misfortune:
Faranta mana zuciya kamar yawan kwanakin da muka sha azaba, kamar yawan shekarun da muka ga wahala.
16 Let thy work, appear unto thy servants, And, thy majesty, upon their children;
Bari a nuna ayyukanka ga bayinka, darajarka ga’ya’yansu.
17 And let the delightfulness of Adonay our God be upon us, —And, the work of our hands, establish thou upon us, Yea, the work of our hands, establish thou it.
Bari alherin shugabanmu Allah yă kasance a kanmu; ka albarkaci mana aikin hannuwanmu, I, ka albarkaci aikin hannuwanmu.

< Psalms 90 >