< Psalms 73 >
1 A Melody of Asaph. Nothing but good, is God, Unto Israel, Unto the pure in heart.
Zabura ta Asaf. Tabbatacce Allah mai alheri ne ga Isra’ila, ga waɗanda suke masu tsabta a zuciya.
2 But, as for me, —My feet had, almost stumbled, My steps had, well-nigh slipped;
Amma game da ni, ƙafafuna suna gab da yin santsi; tafin ƙafana ya yi kusan zamewa.
3 For I was envious of the boasters, At the prosperity of the lawless, used I to look.
Gama na yi kishin masu girman kai sa’ad da na ga cin gaban da masu mugunta suke yi.
4 For they have no pangs in their death, And vigorous is their body;
Ba sa yin wata fama; jikunansu lafiya suke da kuma ƙarfi.
5 Of the toil of weak mortals, have they none, Nor, with the sons of earth, are they hard smitten.
Ba sa shan wata wahalar da sauran mutane ke sha; ba su da damuwa irin na’yan adam.
6 For this cause, doth arrogance deck them as a neck-chain, And a garment of wrong is their attire;
Saboda girman kai ya zama musu abin wuya; tā da hankali ya zama musu riga.
7 Their iniquity, hath proceeded from fatness, They have surpassed the imaginations of the heart;
Daga mugayen zukatansu laifi kan fito mugaye ƙulle-ƙullen da suke cikin zukatansu ba su da iyaka.
8 They mock, and wickedly command oppression, From on high, they command;
Suna ba’a, suna faɗin mugayen abubuwa; cikin girman kan suna barazana yin danniya.
9 They have set, in the heavens, their mouth, And, their tongue, marcheth through the earth.
Bakunansu na cewa sama na su ne, kuma harsunansu sun mallaki duniya.
10 Therefore must his people return thither, And, the waters of abundance, are drained by them;
Saboda haka mutanensu sun juya gare su suna kuma shan ruwa a yalwace.
11 And they say—How doth GOD know? And is there knowledge in the Most High?
Suna cewa, “Yaya Allah zai sani? Mafi Ɗaukaka yana da sani ne?”
12 Lo! these, are the lawless, Who are secure for an age, They have attained unto wealth.
Ga yadda mugaye suke, kullum ba su da damuwa, arzikinsu yana ta ƙaruwa.
13 Altogether in vain, Have I cleansed my heart, And bathed in pureness, my hands;
Tabbatacce a banza na bar zuciyata da tsabta; a banza na wanke hannuwa don nuna rashin laifi.
14 And yet been smitten all the day, And been rebuked morning by morning!
Dukan yini na sha annoba; an hukunta ni kowace safiya.
15 If I had thought, I will relate it thus, Lo! the circle of thy sons, had I betrayed.
Da na ce, “Zan faɗa haka,” da na bashe’ya’yanka.
16 When I reasoned, that I might understand this, A vexation, it was in mine eyes:
Sa’ad da na yi ƙoƙari in gane wannan, sai ya zama danniya a gare ni
17 Until I could enter the holy places of God, —Could give heed to their hereafter: —
sai da na shiga wuri mai tsarki na Allah; sa’an nan na gane abin da ƙarshensu zai zama.
18 Surely, in slippery places, dost thou set them, —Thou hast suffered them to fall into places of danger.
Tabbatacce ka sa su a ƙasa mai santsi; ka jefar da su ga hallaka.
19 How have they become desolate, as in a moment! They have ceased—come to an end, by reason of calamities.
Duba yadda suka hallaka farat ɗaya, razana ta share su gaba ɗaya!
20 As the dream of him that waketh, O my Lord! when rousing thyself up, their shadowy being, wilt thou despise.
Kamar yadda mafarki yake sa’ad da mutum ya farka, haka yake sa’ad da ka farka, ya Ubangiji, za ka rena su kamar almarai.
21 But my heart had grown embittered, And, in my reins, had I received wounds;
Sa’ad da zuciyata ta ɓaci hankalina kuma ya tashi,
22 But, I, was brutish, and could not perceive, Like the beasts, had I become before thee.
na zama marar azanci da jahili; na zama kamar dabba a gabanka.
23 Nevertheless, I, am continually before thee, Thou hast taken hold of my right hand;
Duk da haka kullum ina tare da kai; ka riƙe ni a hannun damana.
24 By thy counsel, wilt thou guide me, And, afterwards, unto glory, wilt thou take me.
Ka bishe ni da shawararka, bayan haka kuma za ka kai ni cikin ɗaukaka.
25 Whom have I in the heavens? And, compared with thee, there is nothing I desire on earth.
Wa nake da shi a sama in ba kai ba? Ba na kuma sha’awar kome a duniya in ban da kai.
26 Failed have my flesh and my heart, The rock of my heart—and my portion, is God unto times age-abiding.
Jikina da zuciyata za su iya raunana, amma Allah ne ƙarfin zuciyata da kuma rabona har abada.
27 For lo! they who are far from thee, shall perish, Thou hast put an end to every one who wandered unchastely from thee.
Waɗanda suke nesa da kai za su hallaka; kakan hallaka dukan waɗanda suke maka rashin aminci.
28 But, as for me, the drawing near of God, is my blessedness, —I have made, of My Lord Yahweh, my refuge, —That I may recount all thy works.
Amma game da ni, yana da kyau in kasance kusa da Allah. Na mai da Ubangiji Mai Iko Duka mafakata; zan yi shelar dukan ayyukanka.