< Psalms 40 >

1 To the Chief Musician. David’s. A Melody. I waited patiently for Yahweh, —And he inclined, unto me, and heard my cry for help;
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Na jira da haƙuri ga Ubangiji; ya juya wurina ya kuma ji kukata.
2 So he brought me up, Out of the destroying pit, Out of the swampy mire, —And set, upon a cliff, my feet, Making firm my steps:
Ya ɗaga ni daga rami marar fāɗi, daga laka da taɓo; ya sa ƙafafuna a kan dutse ya kuma ba ni tsayayyen wuri don in tsaya.
3 Then put he, into my mouth, a new song, Praise to our God, —Many shall see and revere, And shall trust in Yahweh.
Ya sa sabuwar waƙa a bakina, waƙar yabo ga Allahna. Da yawa za su gani su tsorata su kuma dogara ga Ubangiji.
4 How happy the man, Who hath made Yahweh his confidence, who hath not turned unto the haughty, nor gone aside unto falsehood.
Mai albarka ne mutumin da ya mai da Ubangiji abin dogararsa, wanda ba ya kula da masu girman kai, waɗanda suka juya ga allolin ƙarya.
5 Mighty things, hast thou done—Thou, Yahweh my God, Thy wonderful doings and thy purposes towards us, There is no setting them in order unto thee—I would tell, and would speak!—They are too great to rehearse.
Da yawa ne, ya Ubangiji Allahna, abubuwan banmamakin da ka aikata. Abubuwan da ka shirya mana. Ba wanda zai iya faɗa maka su; a ce zan yi magana in faɗe su, za su wuce gaban misali a furta.
6 Sacrifice and meal-offering, thou didst not delight in, Ears, didst thou pierce for me, —Ascending-sacrifice and sin-bearer, thou didst not ask:
Hadaya da sadaka ba ka sha’awa, amma kunnuwana ka huda; hadayun ƙonawa da hadayun zunubi ba ka bukata.
7 Then, said I—Lo! I am come, In the written scroll, is it prescribed for me;
Sa’an nan na ce, “Ga ni, na zo, kamar yadda yake a rubuce game da ni cikin littafi.
8 To do thy good-pleasure, O my God, is my delight, And, thy law, is in the midst of mine inward parts:
Ina sha’awar aikata nufinka, ya Allahna; dokar tana cikin zuciyata.”
9 I have told the good-tidings of righteousness in a great convocation, Lo! my lips, do I not restrain, O Yahweh, thou, knowest:
Na yi shelar adalcinka cikin babban taro; ba na rufe leɓunana, kamar yadda ka sani, ya Ubangiji.
10 Thy righteousness, have I not hid in the midst of my heart, Thy faithfulness and thy salvation, have I spoken, I have not concealed thy lovingkindness and thy truthfulness from the great convocation.
Ba na ɓoye adalcinka cikin zuciyata; ina maganar amincinka da cetonka. Ban ɓoye ƙaunarka da gaskiyarka a gaban taron jama’arka mai girma ba.
11 Thou, O Yahweh, wilt not restrain thy compassions from me, Thy lovingkindness and thy truthfulness, shall continually watch over me.
Kada ka hana mini jinƙanka, ya Ubangiji; bari ƙaunarka da gaskiyarka kullum su kāre ni.
12 For there have closed in upon me, misfortunes beyond number, Mine iniquities have overtaken me, and I cannot see, They have become more than the hairs of my head, And, my courage, hath forsaken me!
Gama damuwoyin da suka wuce misali sun kewaye ni; zunubaina sun mamaye ni, kuma ba na iya gani. Sun fi gashin kaina yawa, har ma na fid da zuciya.
13 Be pleased, O Yahweh, to rescue me, O Yahweh! to help me, make haste!
Ka ji daɗin cetona, ya Ubangiji; Ya Ubangiji, ka zo da sauri ka taimake ni.
14 Let them turn pale and then at once blush, who are seeking my life to snatch it away, —Let them draw back, and be confounded, who are taking pleasure in my calamity;
Bari masu neman raina su sha kunya su kuma rikice; bari dukan waɗanda suke neman lalacewata su koma baya da kunya.
15 Let them be astonished on account of their own shame, who are saying of me, Aha! Aha!
Bari masu ce mini, “Allah yă ƙara!” Su sha mamaki saboda kunyar da za su sha.
16 Let all them be glad and rejoice in thee, who are seekers of thee. Let them say continually—Yahweh be magnified! who are lovers of thy salvation.
Amma bari dukan masu nemanka su yi farin ciki su kuma yi murna a cikinka; bari waɗanda suke ƙaunar cetonka kullum su ce, “Ubangiji mai girma ne!”
17 But, I, being oppressed and needy, May My Lord devise for me, —My help and my deliverer, thou art! O my God, do not tarry!
Ni dai matalauci ne da mai bukata; bari Ubangiji yă tuna da ni. Kai ne taimakona da mai cetona; Ya Allahna, kada ka jinkirta.

< Psalms 40 >