< Psalms 37 >

1 David’s. [An Alphabetical Psalm.] Burn not with vexation because of evil-doers, Be not envious of the workers of perversity;
Ta Dawuda. Kada ka tsorata saboda mugayen mutane ko ka yi kishin waɗanda suka aikata mugunta;
2 For, like grass, soon shall they wither, and, like green herbage, shall they fade.
gama kamar ciyawa za su bushe, kamar ɗanyun ganyaye za su mutu.
3 Trust in Yahweh, and do good, Dwell in the land, and feed on fidelity;
Ka dogara ga Ubangiji ka kuma aikata alheri; yi zama cikin ƙasar ka kuma more makiyaya mai lafiya.
4 Yea, rest thy delight on Yahweh, that he may give thee the requests of thy heart.
Ka ji daɗinka a cikin Ubangiji zai kuwa biya bukatun zuciyarka.
5 Roll on Yahweh thy way, Trust also in him, and, he, will effectually work:
Ka sa kanka a hanyar Ubangiji; ka kuma dogara gare shi zai kuwa yi wannan.
6 So will he bring forth, as the light, thy righteousness, and thy vindication as the noonday.
Zai sa adalcinka yă haskaka kamar hasken safiya, gaskiyarka kuma kamar rana a tsaka.
7 Be resigned to Yahweh, yea wait with longing for him; Burn not with vexation at him who prospereth in his way, —at the man who doeth wickedness.
Ka natsu a gaban Ubangiji ka kuma jira da haƙuri gare shi; kada ka tsorata sa’ad da mutane ke nasara a hanyoyinsu, sa’ad da suke aikata mugayen shirye-shiryensu.
8 Cease from anger, and forsake wrath, Burn not with vexation—[it would be] only to do evil;
Kada ka yi fushi kada kuma ka yi hasala; kada ka tsorata, wannan yakan kai ga mugunta ne kawai.
9 For, evil doers, shall be cut off, but, as for them who wait for Yahweh, they, shall inherit the earth.
Gama za a datse mugayen mutane, amma waɗanda suke sa zuciya ga Ubangiji za su gāji ƙasar.
10 Yet a little, therefore, and the lawless one shall not be, Yea thou shalt look about, over his place—and he shall have vanished!
A ɗan ƙanƙanen lokaci, mugaye za su shuɗe; ko ka neme su, ba za a same su ba.
11 But, the patient oppressed-ones, shall inherit the earth, and shall delight themselves over the abundance of prosperity.
Amma masu tawali’u za su gāji ƙasar su kuma zauna da cikakkiyar salama.
12 Plotting is the lawless one, against the just, and gnashing upon him with his teeth.
Mugaye sukan shirya wa adalai maƙarƙashiya su ciji baki a kansu;
13 My Lord, shall laugh at him, for he seeth, that his day, will come.
amma Ubangiji yakan yi dariyar mugaye, gama ya sani ranarsu tana zuwa.
14 A sword, have the lawless, drawn out, and have trodden their bow, —To bring down the oppressed and the needy, To slaughter the upright in life:
Mugaye sukan zare takobi su ja baka don su kashe matalauta da masu bukata, don su kashe waɗanda hanyoyinsu daidai suke.
15 Their sword, shall enter into their own heart, and, their bow, shall be broken.
Amma takubansu za su soki zukatansu, kuma bakkunansu za su kakkarye.
16 Better the little of the righteous man, than the abundance of the lawless who are mighty;
Ƙanƙanen abin da mai adalci yake da shi ya fi arzikin mugaye yawa;
17 For, the arms of the lawless, shall be broken, But Yahweh is upholding the righteous.
gama za a kakkarya ikon mugaye, amma Ubangiji zai riƙe mai adalci.
18 Yahweh knoweth the days of the blameless, that, their inheritance, unto times age-abiding, shall continue.
Kwanakin marasa zarge suna sane ga Ubangiji, kuma gādonsu zai dawwama har abada.
19 They shall not be ashamed in the time of calamity, and, in the days of famine, shall they be filled.
A lokutan masifu ba za su yanƙwane ba; a kwanakin yunwa za su sami a yalwace.
20 For, the lawless, shall perish, and, the foes of Yahweh, be like the glory of the meadows, They have vanished! In smoke, have they vanished!
Amma mugaye za su hallaka, Abokan gāban Ubangiji za su zama kamar kyan gonaki, za su ɓace, za su ɓace kamar hayaƙi.
21 A lawless man borroweth, and will not repay, But, a righteous man, showeth favour and giveth;
Mugaye kan yi rance ba sa kuma biya, amma masu adalci suna bayar hannu sake;
22 For, such as are blessed of him, shall inherit the earth, But, the cursed of him, shall be cut off.
waɗanda Ubangiji ya sa wa albarka za su gāji ƙasar, amma waɗanda ya la’anta, za a kore su.
23 From Yahweh, are the steps of a man made firm, When, with his way, he is well pleased:
In Ubangiji ya ji daɗin hanyar da mutum yake bi, zai sa sawu su kahu;
24 Though he fall, he shall not be hurled headlong, For, Yahweh, is holding his hand.
ko ya yi tuntuɓe, ba zai fāɗi ba, gama Ubangiji yakan riƙe shi da hannunsa.
25 Young, have I been, moreover am old, —Yet have I not seen, A righteous man forsaken, Nor his seed begging bread:
Dā ni yaro ne amma yanzu na tsufa, duk da haka ban taɓa ganin an yashe masu adalci ba ko a ce’ya’yansu suna roƙon burodi.
26 All day long, is he showing favour and lending, his seed, therefore, shall have a blessing.
Kullum suna bayar hannu sake suna kuma ba da bashi ba da wahala ba, za a yi wa’ya’yansu albarka.
27 Turn from evil, and do good, and so settle down, unto times age-abiding.
Ku juyo daga mugunta ku yi alheri; sa’an nan za ku zauna a ƙasar har abada.
28 For, Yahweh, loveth justice, and will not forsake his men of lovingkindness, Unto times age-abiding, have the perverse been destroyed, —and the seed of the lawless, been cut off.
Gama Ubangiji yana ƙaunar masu aikata daidai kuma ba zai yashe amintattunsa ba. Za a hallaka masu aikata mugunta gaba ɗaya,’ya’yan mugaye za su hallaka.
29 The righteous, shall inherit the earth, that they may settle down, to futurity, thereupon.
Masu adalci za su gāji ƙasar su kuma zauna a cikinta har abada.
30 The mouth of a righteous man, softly uttereth wisdom, and, his tongue, speaketh justice:
Bakin mutum mai adalci yakan yi magana da hikima, harshensa kuwa yakan yi maganar abin da yake daidai.
31 The law of his God, is in his heart, his steps shall not swerve.
Dokar Allahnsa tana a cikin zuciyarsa; ƙafafunsa ba sa santsi.
32 The lawless man, lieth in wait, for the just, and seeketh to put him to death:
Mugaye suna fako suna jira masu adalci, suna ƙoƙari neman ransu;
33 Yahweh, will not leave him in his hand, nor condemn him, when he is judged.
amma Ubangiji ba zai bar su a ikonsu ba ko ya bari a hukunta su sa’ad da aka kawo su shari’a ba.
34 Wait for Yahweh, and observe thou his path, that he may exalt thee, to inherit the earth, On the cutting off of the lawless, shalt thou look.
Ku sa zuciya ga Ubangiji ku kuma kiyaye hanyarsa. Zai ɗaukaka ku ku ci gādon ƙasar, sa’ad da aka kawar da mugaye, za ka gani.
35 I have seen a lawless man, a tyrant, and spreading himself out, like a cedar in Lebanon;
Na ga wani mugu, azzalumi, yana yaɗuwa kamar ɗanyen itace a asalin ƙasarsa,
36 Then I passed by, and lo! he had vanished! Yea I sought him, but he could not be found.
amma yakan mutu nan da nan kuma ba ya ƙara kasancewa; ko an neme shi, ba za a same shi ba.
37 Mark the blameless man, and behold the upright, for there is a hereafter for the man of peace;
Ka dubi marasa zargi, ka lura da adali; akwai sa zuciya domin mutum mai salama.
38 But, transgressors, are to be destroyed together, the hereafter of lawless men, is to be cut off.
Amma za a hallaka dukan masu zunubi; za a yanke sa zuciya ta mugaye.
39 But, the deliverance of the righteous, is from Yahweh, their refuge in a time of distress.
Ceton adalai kan zo daga Ubangiji; shi ne mafaka a lokacin wahala.
40 Thus hath Yahweh helped them, thus hath he delivered them, —He will deliver them from the lawless, and will save them, because they have sought refuge in him.
Ubangiji yakan taimake su yă kuma cece su; yakan kuɓutar da su daga mugaye yă kuma cece su, domin sukan nemi mafaka daga gare shi.

< Psalms 37 >