< Psalms 29 >
1 A Melody of David. Give to Yahweh, ye sons of the mighty, —Give to Yahweh, [both] glory and strength:
Zabura ta Dawuda. Ku ba da girma ga Ubangiji, ya ku manya, ku ba da girma ga Ubangiji saboda ɗaukaka da kuma ƙarfinsa.
2 Give to Yahweh, the glory of his Name, Bow down to Yahweh, in the adornment of holiness.
Ku ba da girma ga Ubangiji, ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku bauta wa Ubangiji cikin ɗaukakar tsarkinsa.
3 The voice of Yahweh, is upon the waters, —The GOD of glory, hath thundered, Yahweh, is upon mighty waters;
Muryar Ubangiji tana a bisa ruwaye; Allah Maɗaukaki ya yi tsawa, Ubangiji ya yi tsawa a bisa manyan ruwaye.
4 The voice of Yahweh, is with power, The voice of Yahweh, is with majesty;
Muryar Ubangiji mai iko ce; muryar Ubangiji da girma take.
5 The voice of Yahweh, is breaking cedars, Now hath Yahweh, broken down, the cedars of Lebanon!
Muryar Ubangiji ta kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon. Ubangiji ya kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon kucu-kucu.
6 And hath made them leap like a calf, Lebanon and Sirion, like the bull-calf of wild-oxen;
Ya sa dutsen Lebanon ya yi ta tsalle kamar ɗan maraƙi, Siriyon kuma kamar ɗan jakin jeji.
7 The voice of Yahweh, is cleaving out flames of fire;
Muryar Ubangiji ta buga da walƙatar walƙiya.
8 The voice of Yahweh, bringeth birth-pains upon the wilderness; Yahweh bringeth birth-pains upon the wilderness of Kadesh!
Muryar Ubangiji ta girgiza hamada Ubangiji ya girgiza Hamadan Kadesh.
9 The voice of Yahweh, causeth the gazelles to bring forth, and hath stript forests; and, in his own temple, every one there, is saying, Glory!
Muryar Ubangiji ta murɗa itatuwan oak ya kakkaɓe itatuwan kurmi. Kuma a cikin haikalinsa kowa ya ce, “Ɗaukaka!”
10 Yahweh, at the Flood, was seated, And Yahweh hath taken his seat, as king, unto times age-abiding.
Ubangiji na zaune yana sarauta a bisa rigyawa; Ubangiji yana sarauta kamar Sarki har abada.
11 Yahweh, will give, strength to his people, —Yahweh, will bless his people with prosperity.
Ubangiji kan ba da ƙarfi ga mutanensa; Ubangiji kan albarkace mutanensa da salama.