< Psalms 17 >

1 A Prayer of David. Hear, O Yahweh, the right, Attend to my loud cry, Give ear unto my prayer, on lips that would not deceive:
Addu’a ce ta Dawuda. Ka ji, ya Ubangiji, roƙona na adalci; ka saurari kukata. Ka kasa kunne ga addu’ata, ba ta fitowa daga leɓuna masu ƙarya.
2 From before thee, let my sentence come forth, Thine eyes, behold with equity.
Bari fiffitawata tă zo daga gare ka; bari idanunka su ga abin da yake daidai.
3 Thou hast tested my heart, hast made inspection by night, hast refined me until thou couldst find nothing, Had I devised evil, my mouth should not have transgressed:
Ko ka duba zuciyata, ka kuma bincike ni da dare, ko ka gwada ni, ba za ka sami kome ba; na yanke shawara cewa bakina ba zai yi zunubi ba.
4 As for the workings of men, By the word of thy lips, have, I, taken heed of the paths of the violent one.
Game da ayyukan mutane kuwa, ta wurin maganar leɓunanka na kiyaye kaina daga hanyoyin tashin hankali.
5 Thou hast held fast my goings on to thy ways, My footsteps have not been shaken:
Sawuna sun kama hanyoyinka ƙafafu kuwa ba za su yi santsi ba.
6 I, have called upon thee, for thou wilt answer me, O GOD, —Incline thine ear unto me, Hear thou my speech:
Na kira gare ka, ya Allah, gama za ka amsa mini; ka kasa kunne ka kuma ji addu’ata.
7 Let thy lovingkindness be distinguished, thou Saviour of such as seek refuge from them who lift themselves up against thy right hand.
Ka nuna mini girmar ƙaunarka mai banmamaki, kai da kake ceton waɗanda suke neman mafaka daga abokan gābansu da hannunka na dama.
8 Guard me, as the pupil of the eye, —Under the shadow of thy wings, wilt thou hide me:
Ka kiyaye ni yadda ake kiyaye ido; ka ɓoye ni cikin inuwar fikafikanka
9 From the face of lawless ones who have treated me with violence, the foes of my soul, who come round against me:
daga mugaye waɗanda suke kai mini hari, daga abokan gāba masu mutuwa waɗanda suka kewaye ni.
10 Their own fat [heart], have they shut up, —With their mouth, have they spoken proudly.
Sun rufe zukatansu marar tausayi, da bakunansu suna magana da fariya.
11 As for our own goings, now, have they surrounded us, —Their eyes, they fix, bending to the earth:
Sun sa mini ido, yanzu sun kewaye ni, a shirye suke, su jefa ni a ƙasa.
12 His likeness, is as a lion, that longeth to rend, and as a young lion, lurking in secret places.
Suna kama da zaki mai yunwan abinci, kamar babban zaki mai fako a maɓuya.
13 Rise, Yahweh! Confront his face, Bring him down, Deliver my soul from the lawless one [who is] thy sword:
Ka tashi, ya Ubangiji, ka yi arangama da su, ka durƙusar da su; ka cece ni daga mugaye ta wurin takobinka.
14 From men [who are] thy hand, O Yahweh, From the men of this age, whose portion, is among the living, and, with thy treasure, thou fillest their bosom, —They must be satisfied with sons, And must leave their abundance to their children: —
Ya Ubangiji, da hannunka ka cece ni daga irin mutanen nan, daga mutanen duniyan nan waɗanda ladarsu yana a wannan rayuwa ne. Kakan cika yunwan waɗanda kake so;’ya’yansu suna da isashe suna kuma ajiyar wadata wa’ya’yansu.
15 I, in righteousness, shall behold thy face, Shall be satisfied when awakened by a vision of thee.
Amma ni, cikin adalci zan ga fuskarka; sa’ad da na farka, zan gamsu da ganin kamanninka.

< Psalms 17 >