< Psalms 122 >

1 A Song of Ascents. David’s. I was glad, when they were saying unto me, Unto the house of Yahweh, let us go!
Waƙar haurawa. Ta Dawuda. Na yi farin ciki tare da waɗanda suka ce da ni, “Bari mu tafi gidan Ubangiji.”
2 Standing are our feet, within thy gates, O Jerusalem!
Ƙafafunmu suna tsaye a ƙofofinki, ya Urushalima.
3 Jerusalem! that hath been builded, A true city, all joined together as one:
An gina Urushalima kamar birnin da aka yi a harhaɗe wuri guda.
4 Whither have come up the tribes, The tribes of Yah, A testimony to Israel, To give thanks unto the Name of Yahweh:
A can ne kabilu suke haurawa, kabilan Ubangiji, don su yabi sunan Ubangiji bisa ga farillan da aka ba wa Isra’ila.
5 For there are set—Thrones for justice, Thrones for the house David.
A can kursiyoyin shari’a yake tsaye, kursiyoyin gidan Dawuda.
6 Ask ye for the peace of Jerusalem, They shall prosper, who love thee!
Ku yi addu’a don salamar Urushalima, “Bari waɗanda suke ƙaunarki su zauna lafiya.
7 Peace be within thy walls, prosperity within thy palaces:
Bari salama ta kasance a katangarki zaman lafiya kuma a fadodinki.”
8 For the sake of my brethren and friends, Oh, might I speak [saying], Peace be within thee!
Saboda’yan’uwana da kuma abokaina, zan ce, “Salama tă kasance tare da ke.”
9 For the sake of the house of Yahweh our God, will I seek blessing for thee.
Saboda gidan Ubangiji Allahnmu, zan nemi wadatarki.

< Psalms 122 >