< Proverbs 23 >

1 When thou sittest to eat with a ruler, thou shalt consider well, what is before thee;
Sa’ad da ka zauna domin cin abinci da mai mulki, ka lura sosai da abin da yake gabanka,
2 And shalt put a knife to thy throat, if, of great appetite, thou art:
ka kuma sa wuƙa a maƙogwaronka in kai mai ci da yawa ne.
3 Do not crave his dainties, for, the same, are deceitful food.
Kada ka yi marmarin abincinsa mai daɗi gama wannan abinci ruɗu ne.
4 Do not toil to get wealth, of thine own understanding, forbear:
Kada ka gajiyar da kanka don ka yi arziki; ka kasance da hikimar dainawa.
5 Wilt thou let thine eye fly thereupon, when it is nothing? for it will, surely make, itself wings, Like an eagle, will it wing its way across the heavens.
Da ƙyiftawar ido a kan wadata ta ɓace, gama tabbatacce sukan yi fikafikai sukan tashi sama kamar gaggafa.
6 Do not eat the food of him that hath a begrudging eye, neither crave thou his dainties;
Kada ka ci abincin mai rowa, kada ka yi marmarin abincinsa mai daɗi;
7 For, just as he hath thought in his own mind, so, he is: Eat and drink! he may say to thee, but, his heart, is not with thee.
gama shi wani irin mutum ne wanda kullum yana tunani game da tsadar abincin. Zai ce maka, “Ci ka sha,” amma zuciyarsa ba ta tare da kai.
8 As for thy morsel thou hast eaten, thou shalt vomit it, so shalt thou waste thy things so sweet.
Za ka yi amai ɗan abin da ka ci dukan daɗin bakinka kuwa zai tafi a banza.
9 In the ears of a dullard, do not speak, for he will despise the good sense of thy words.
Kada ka yi magana da wawa, gama zai yi wa maganar hikimarka ba’a.
10 Do not move back the ancient boundary, and, into the fields of the fatherless, do not enter;
Kada ka kawar da shaidar iyaka ta dā ko ka ɗiba gonar marayu,
11 For, their near of kin, is strong, he, will plead their cause with thee.
gama mai Kāriyarsu yana da ƙarfi; zai kuwa yi magana dominsu.
12 Bring, to correction, thy heart, and thine ears, to the sayings of knowledge.
Ka mai da hankali ga umarni ka kuma kasa kunne ga kalmomin sani.
13 Do not withhold, from a child, correction, When thou smitest him with the rod, he shall not die:
Kada ka bar yaro ba horo; in ka yi masa horo da sanda, ba zai mutu ba.
14 Thou, with the rod, shalt smite him, and, his soul from hades, shalt thou deliver. (Sheol h7585)
Ka hukunta shi da sanda ka ceci ransa daga mutuwa. (Sheol h7585)
15 My son! if thy heart be wise, my heart shall rejoice, even mine.
Ɗana, in zuciyarka mai hikima ce, to, zuciyata za tă yi murna;
16 So shall my reins exult, when thy lips speak the things that are right.
cikin cikina zai yi farin ciki in leɓunanka suna maganar abin da yake daidai.
17 Let not thy heart be envious of sinners, only of the reverence of Yahweh, all day long;
Kada ka bar zuciyarka tă yi ƙyashin masu zunubi, amma kullum tsoron Ubangiji za ka yi kishi.
18 For surely there is a future, and, thine expectation, shall not be cut off.
Tabbatacce akwai sa zuciya ta nan gaba dominka, kuma sa zuciyarka ba za tă zama a banza ba.
19 Hear, thou, my son, and be wise, and lead forward, in duty, thy heart.
Ka saurara, ɗana, ka zama mai hikima, ka kafa zuciyarka a hanyar da take daidai.
20 Do not be among them who tipple with wine, —among them who are gluttons;
Kada ka haɗa kai da waɗanda suke shan ruwan inabi da yawa ko masu haɗama kansu da abinci,
21 For, the tippler and the glutton, shall come to poverty, and, rags, shall Slumber put on!
gama bugaggu da ruwan inabi da masu yawan ci sukan zama matalauta, gama jiri yakan yi musu sutura da tsummoki.
22 Hearken to thy father here, who begat thee, and despise not, when she is old, thy mother.
Ka kasa kunne ga mahaifinka, wanda ya ba ka rai, kada kuwa ka rena mahaifiyarka sa’ad da ta tsufa.
23 Truth, buy thou, but do not sell, wisdom, and correction, and understanding.
Ka saye gaskiya kada kuwa ka sayar da ita; ka nemi hikima, horo da fahimi.
24 Greatly shall exult, the father of a righteous man, and, he that begetteth a wise son, shall rejoice in him:
Mahaifin adali yana da farin ciki sosai; duk wanda yake da ɗa mai hikima yakan ji daɗinsa.
25 Rejoice shall thy father and thy mother, yea she, shall exult, who bare thee.
Bari mahaifinka da mahaifiyarka su yi murna; bari wadda ta haife ka tă yi farin ciki!
26 Oh give, my son, thy mind unto me, and let, thine eyes, observe, my ways;
Ɗana, ka ba ni zuciyarka bari kuma idanunka su kiyaye hanyoyina,
27 For, a deep chasm, is the unchaste woman, and, a narrow pit, the female unknown;
gama karuwa rami ne mai zurfi mace marar aminci matsattsiyar rijiya ce.
28 Yea, she, as for prey, lieth in wait, and, the treacherous among mankind, she causeth to abound.
Kamar’yan fashi, takan kwanta tana jira tana kuma ninka rashin aminci a cikin maza.
29 Who hath woe? Who hath outcry of pain? Who hath contentions? Who hath complaining? Who hath needless wounds? Who hath dullness of eyes?
Wa yake wayyo? Wa yake baƙin ciki? Wa yake neman fada? Wa yake gunaguni? Wa yake da raunuka ba dalili? Wa yake da jan idanu?
30 They who tarry over wine, they who go in to search for mixed wine.
Waɗanda suke daɗe suna shan ruwan inabi, waɗanda suke neman ƙoƙon damammen ruwan inabi.
31 Do not look on wine when it becometh red, when it giveth in the cup its sparkle, glideth down smoothly.
Kada ka ƙyifce ido a ruwan inabi sa’ad da ya yi ja, sa’ad da yana da kyan gani a cikin ƙwarya, sa’ad da yana gangarawa sumul a maƙogwaro!
32 Its after effect, is that, like a serpent, it biteth, and, like a viper, it doth sting.
A ƙarshe yana sara kamar maciji da kuma dafi kamar gamsheƙa.
33 Thine eyes, will see strange women, and, thy heart, will speak perverse things:
Idanunka za su riƙa gane-gane, zuciyarka kuma za su riƙa tunani abubuwa masu rikitarwa.
34 So shalt thou become, as one lying down in the heart of the sea, —or as one lying down on the top of the mastgear:
Za ka zama kamar wanda yake barci a tsakiyar tekuna, kwance a sama itacen jirgin ruwa.
35 They smote me—I felt no pain, They struck me down—I noticed it not, —When shall I wake up? I will go on, I will seek it, again!
Za ka ce “Sun buge ni, amma ban ji ciwo ba! Sun daddoke ni, amma ba na jin zafinsa! Yaushe zan farka don in ƙara shan wani?”

< Proverbs 23 >