< Nehemiah 4 >
1 But it came to pass, when Sanballat heard that we were building the wall, it angered him, and he was greatly displeased, —and mocked the Jews;
Da Sanballat ya ji cewa muna sāke ginin katangar, sai ya husata, ya haukace ƙwarai. Ya yi wa Yahudawa dariya,
2 and spake before his brethren, and the army of Samaria, and said, What are, these feeble Jews, doing? will they fortify themselves? will they sacrifice? will they make an end in a day? will they bring to life the stones out of the heaps of dust, when, they, have been burned up?
a gaban abokansa da kuma sojojin Samariya ya ce, “Me waɗancan Yahudawan nan marasa ƙarfi suke yi? Za su maido da katangarsu ne? Za su miƙa hadayu ne? Za su gama a rana ɗaya? Za su iya samun duwatsun gini daga tsibin matattun duwatsu?”
3 Now, Tobiah the Ammonite, was beside him, —so he said, Even that which they are building, if a fox should go up, he would break down their stone wall!
Tobiya wakilin mutanen Ammon wanda yake a gefensa ya ce, “Abin nan da suke gini, ko dila ma ya hau, zai rushe shi!”
4 Hear, O our God, for we have become a contempt, and turn thou back their reproach upon their own head, —and give them up as a prey, in the land of captivity;
Ka ji mu, ya Allahnmu, gama an rena mu. Bari zagin da suke yi mana yă koma kansu. Ka sa a kwashe su a kai su bauta a wata ƙasa.
5 and do not cover their iniquity, and, their sin before thee, let it not be blotted out, —for they have caused vexation before them who are building.
Kada ka rufe laifinsu, kada kuwa ka gafarta musu, gama sun ci mutuncinmu, mu da muke gini.
6 So we built the wall, and all the wall was finished unto the half thereof, —and the people had a mind to work.
Sai muka sāke ginin katangar sai da duka ta kai rabin tsayinta, gama mutane sun yi aiki da dukan ƙarfinsu.
7 But it came to pass, when Sanballat and Tobiah and the Arabians and the Ammonites and the Ashdodites heard that the repair of the walls of Jerusalem had gone up, that the breaches began to be stopped, that it angered them exceedingly;
Amma da Sanballat, da Tobiya, da Larabawa, da Ammonawa, da kuma mutanen Ashdod suka ji cewa gyare-gyaren katangar Urushalima yana cin gaba, ana kuma tattoshe wuraren da suka tsattsaga, sai suka husata ƙwarai.
8 and they conspired, all of them together, to come, to fight against Jerusalem, —and to cause it harm;
Dukansu suka ƙulla su zo, su yi yaƙi da Urushalima, su tā da hankali a cikinta.
9 howbeit we prayed unto our God, —and set a watch against them, day and night, because of them.
Amma muka yi addu’a ga Allahnmu muka kuma sa masu tsaro da rana da kuma dare don mu magance wannan barazana.
10 Then said Judah, The strength of the burden-bearer faileth, and, the rubbish, aboundeth, —and, we, are not able to build at the wall;
Ana cikin haka, mutane a Yahuda suka ce, “Ƙarfin ma’aikata yana kāsawa, akwai kuma sauran tarkace da yawa da ba za mu iya sāke gina katangar ba.”
11 and our adversaries have said, They shall not know, neither shall they see, until we come into their midst, and slay them, —so shall we cause the work to cease.
Abokan gābanmu sun ce, “Ba za su sani ba, ba kuwa za su gan mu ba, sai dai kawai su gan mu a cikinsu, za mu karkashe su, mu tsai da aikin.”
12 But it came to pass, when the Jews dwelling near them came in, then said they unto us, ten times, From all places whither ye shall turn, [they will be] upon us!
Sau da yawa Yahudawan da suke da zama kusa da abokan gābanmu sun yi ta zuwa suna yin mana magana, suna cewa “Ko’ina muka juya, za su fāɗa mana.”
13 So I set—on the lower slopes of the place behind the wall in the waste grounds, —yea I set the people, by their families, with their swords, their spears and their bows.
Saboda haka na sa jama’a su ja ɗamara bisa ga iyalinsu a bayan katanga, a wuraren da ba a gina ba. Suna riƙe da takuba, da māsu, da bakkuna.
14 Then I looked and rose up, and said—unto the nobles and unto the deputies and unto the rest of the people, Do not ye fear because of them, —the great and fearful Lord, remember ye, so shall ye fight for your brethren, your sons and your daughters, your wives, and your houses.
Bayan na dudduba abubuwa, sai na miƙe tsaye na ce wa manyan gari da shugabanni da kuma sauran jama’a, “Kada ku ji tsoronsu. Ku tuna da Ubangiji, wanda yake mai girma da banrazana, ku yi yaƙi don’yan’uwanku, da’ya’yanku maza da mata, da matanku da kuma gidajenku.”
15 And it came to pass, when our enemies heard that it was known to us, and that God had overturned their counsel, then returned we, all of us, unto the wall, every man unto his work.
Da abokan gābanmu suka ji muna sane da shirinsu, Allah kuma ya wargaje shirin nan, sai duk muka dawo ga katangar, kowa ya kama aikinsa.
16 And it came to pass, from that day, the half of my young men, were working in the work, and, the half of them, were grasping the spears, the bucklers, and the bows, and the coats of mail, —but, the rulers, were behind all the house of Judah.
Daga wannan rana zuwa gaba, rabin mutane suka yi aiki, yayinda sauran rabin suka kintsa da māsu, da garkuwa, da bakkuna da makamai. Shugabanni suka goyi bayan dukan mutanen Yahuda
17 They who were building at the wall and they who were carrying burdens, they who were lifting, [each man], with his one hand, was working at the work, and, with the other, was grasping the weapon.
waɗanda suke ginin katanga. Waɗanda suke ɗaukan kaya suka yi aikinsu da hannu ɗaya, suna kuma riƙe da makami a ɗaya hannun,
18 Even they who were building, every man, had his sword girded upon his loins, and so was building, —and, he that sounded the horn, was by my side.
kuma kowane mai gini ya ɗaura takobinsa a gefe yayinda yake aiki. Amma mutum mai busa ƙaho ya kasance tare da ni.
19 So I said unto the nobles and unto the deputies, and unto the rest of the people, The work, is great and large, —and, we, are separated upon the wall, far away, each man from his brother:
Sai na ce wa manyan gari, da shugabanni, da sauran jama’a, “Aikin nan babba ne kuma mai yawa, ga shi muna a rarrabe nesa da juna a katangar.
20 In what place soever ye shall hear the sound of the horn, thither, gather yourselves unto us, —our God, will fight for us.
Duk inda kuka ji an busa ƙaho, sai ku taru a wurin. Allahnmu zai yi yaƙi dominmu!”
21 So, we, were working at the work, —one half of them, grasping the spears, from the uprisings of the dawn, until the coming out of the stars.
Saboda haka muka ci gaba da aiki, rabin mutane suna riƙe da māsu, daga wayewar gari har zuwa fitowar taurari.
22 Moreover, at that time, I said to the people, Let, every one with his young man, lodge for the night in the midst of Jerusalem, —so shall they serve us, in the night, as a watch, and, the day, for work.
A wannan lokaci na kuma ce wa mutane, “A sa kowane mutum da mataimakinsa su zauna a Urushalima da dare, domin a yi tsaro da dare, da safe kuma a kama aiki.”
23 So neither I, nor my brethren, nor my young men, nor the men of the watch that followed me, none of us, put off our clothes, —every one [went] with his weapon to the water.
Saboda haka ni, da’yan’uwana, da bayina, da matsaran da suke tare da ni, ba wanda ya tuɓe tufafinsa; kowa ya rataye makaminsa, ko ya je shan ruwa ma.