< Nehemiah 3 >
1 Then arose Eliashib the high priest and his brethren the priests, and built the sheep-gate, they, hallowed it, and set up the doors thereof, —even unto the tower of Hammeah, hallowed they it, unto the tower of Hananel;
Eliyashib babban firist da’yan’uwansa firistoci suka tashi suka sāke gina Ƙofar Tumaki. Suka tsarkake ta, suka sa ƙofofinta a wurarensu, suka yi ginin har Hasumiyar Ɗari, wadda suka tsarkake, da kuma Hasumiyar Hananel.
2 and, at his hand, built, the men of Jericho, —and at his [other] hand built Zaccur, son of Imri.
Mutanen Yeriko kuwa suka kama ginin daga mahaɗin, Zakkur ɗan Imri kuma ya fara ginin biye da su.
3 And, the fish-gate, did the sons of Hassenaah build, —they, laid the beams thereof, and set up the doors thereof, the locks thereof, and the bars thereof;
’Ya’yan Hassenaya ne suka gina Ƙofar Kifi. Suka kafa ginshiƙan, suka kuma sa ƙofofinta, da sakatunta, da kuma sandunan ƙarfenta a wurarensu.
4 and, at their hand, repaired, Meremoth son of Uriah son of Hakkoz, and, at their hand, repaired, Meshullum son of Berechiah son of Meshezabel, —and, at their hand, repaired, Zadok son of Baana;
Kusa da su kuma, Meremot ɗan Uriya, ɗan Hakkoz ne ya yi gyare-gyaren. Biye da shi kuma sai Meshullam ɗan Berekiya, ɗan Meshezabel ya yi gyare-gyare. Kusa da shi Zadok ɗan Ba’ana shi ma ya yi gyare-gyare.
5 and, at their hand, repaired, the Tekoites, —but, their chiefs, put not their neck into the service of their lords.
Mutanen Tekowa ne suka yi gyare-gyare biye da shi, amma manyan garinsu suka ƙi su sa hannu cikin aikin da shugabanninsu suka bayar.
6 And, the old gate, did Joiada son of Paseah, and Meshullam, son of Besodeiah, repair, —they, laid the beams thereof, and set up the doors thereof, and the locks thereof, and the bars thereof;
Yohiyada ɗan Faseya, da Meshullam ɗan Besodehiya ne suka gyara Ƙofar Yeshana. Suka kafa katakanta, suka sa ƙyamarenta, da sandunan ƙarfe na kulle ƙofofinta.
7 and, at their hand, repaired, Melatiah the Gibeonite and Jadon the Meronothite, men of Gibeon and of Mizpah, —who pertained to the throne of the pasha Beyond the River;
Biye da su, mutanen Gibeyon da Mizfa Melatiya na Gibeyon da Yadon Meronot waɗanda suke ƙarƙashin ikon gwamnan Kewayen Kogin Yuferites ne suka yi gyare-gyaren.
8 at his hand, repaired, Uzziel son of Harhaiah, goldsmiths, and, at his hand, repaired Hananiah son of the perfumers, —and they fortified Jerusalem, as far as the broad wall;
Uzziyel ɗan Harhahiya, ɗaya daga cikin masu ƙeran zinariya ne ya yi gyare-gyaren sashe na biye; sai Hananiya, ɗaya daga cikin masu yin turare, ya yi gyare-gyaren biye da wannan. Suka gyara Urushalima har zuwa Katanga Mai Faɗi.
9 and, at their hand, repaired, Rephaiah son of Hur, ruler of a half-circuit of Jerusalem;
Refahiya ɗan Hur, mai mulkin rabin yankin Urushalima, ya yi gyare-gyaren sashe na biye.
10 and, at their hand, repaired, Jedaiah son of Harumaph, even over against his own house, —and, at his hand, repaired, Hattush, son of Hashabneiah;
Kusa da Refahiya, Yedahiya ɗan Harumaf ya yi gyare-gyaren daga gaban gidansa, sai Hattush ɗan Hashabnehiya ya yi gyare-gyaren biye da shi.
11 a second length, did Malchijah son of Harim and Hasshub son of Pahath-moab, repair, —also the tower of the ovens;
Malkiya ɗan Harim, da Hasshub ɗan Fahat-Mowab ya yi gyare-gyaren wani sashe da kuma Hasumiyar Wurin Gashi.
12 and, at his hand, repaired, Shallum son of Hallohesh, ruler of a half-circuit of Jerusalem, —he and his daughters.
Shallum ɗan Hallohesh, mai mulkin ɗayan rabin yankin Urushalima ya yi gyare-gyaren sashe na biye tare da taimakon’ya’yansa mata.
13 The valley-gate, did Hanun and the inhabitants of Zanoah, repair, —they, built it, and set up the doors thereof, the locks thereof, and the bars thereof, —also a thousand cubits in the wall, as far as the dung-gate.
Hanun da mazaunan Zanowa ne suka gyara Ƙofar Kwari. Suka sāke gina ta suka sa ƙofofinta, da sakatunta, da sandunan ƙarfenta a wurarensu. Suka kuma gyara yadi ɗari biyar na katangar har zuwa Ƙofar Juji.
14 And, the dung-gate, did Malchijah son of Rechab, ruler of the circuit of Beth-haccherem, repair, —he, built it, and set up the doors thereof, he locks thereof, and the bars thereof.
Malkiya ɗan Rekab mai mulkin yankin Bet-Hakkerem ne ya yi gyare-gyaren Ƙofar Juji. Ya sāke gina ta ya kuma sa sakatunta, da sanduna ƙarfenta a wurarensu.
15 And, the fountain-gate, did Shallun son of Col-hozeh ruler of the circuit of Mizpah, repair, he, built it, and covered it, and set up the doors thereof, the locks thereof, and the bars thereof, —also the wall of the pool of Shelah, by the garden of the king, even as far as the stairs that go down from the city of David;
Shallum ɗan Kol-Hoze mai mulkin Mizfa ne ya yi gyare-gyaren Ƙofar Maɓuɓɓuga. Ya sāke gina ta, ya yi mata jinƙa yana sa ƙofofinta, da sakatunta, da kuma sandunan ƙarfenta a wurarensu. Ya kuma gyara katangar tafkin Silowam, ta Lambun Sarki, har zuwa matakalan da suka gangara daga Birnin Dawuda.
16 after him, repaired, Nehemiah son of Azbuk, ruler of the half-circuit of Beth-zur, —as far as over against the sepulchres of David, even unto the pool which had been made, and unto the house of heroes;
Gaba da shi, Nehemiya ɗan Azbuk, mai mulkin rabin yankin Bet-Zur ne ya yi gyare-gyaren har zuwa kusa da kaburburan Dawuda, har zuwa haƙaƙƙen tafki da kuma Gidan Jarumawa.
17 after him, repaired, the Levites, Rehum son of Bani, —at his hand, repaired, Hashabiah, ruler of the half-circuit of Keilah, for his circuit;
Biye da shi, Lawiyawa a ƙarƙashin Rehum ɗan Bani ne suka yi gyare-gyaren. Kusa da su, Hashabiya mai mulkin rabin yankin Keyila ne ya yi gyare-gyaren don yankinsa.
18 after him, repaired, their brethren, Bavvai son of Henadad, —ruler of the [other] half-circuit of Keilah;
Biye da shi,’yan’uwansu Lawiyawa ne a ƙarƙashin Binnuyi ɗan Henadad, mai mulkin ɗayan rabin yankin Keyila suka yi gyare-gyaren.
19 and there repaired at his hand, Ezer son of Jeshua, ruler of Mizpah, a second length, —over against the ascent of the armoury, at the corner;
Biye da su, Ezer ɗan Yeshuwa, mai mulkin Mizfa, ya yi gyara wani sashe, daga inda yake fuskantar hawan gidan makamai har zuwa kusurwa.
20 after him, zealously repaired Baruch son of Zabbai, a second length, —from the corner, unto the opening of the house of Eliashib, the high priest;
Biye da shi, Baruk ɗan Zakkai da ƙwazo ya gyara wani sashe, daga kusurwa zuwa mashigin gidan Eliyashib babban firist.
21 after him, repaired, Meremoth son of Uriah son of Hakkoz, a second length, —from the opening of the house of Eliashib, even unto the end of the house of Eliashib;
Biye da shi, Meremot ɗan Uriya, ɗan Hakkoz, ya yi gyaran wani sashe, daga mashigin gidan Eliyashib zuwa ƙarshensa.
22 and, after him, repaired, the priests, the men of the Circuit;
Firistoci daga kewayen yankin ne suka yi gyare-gyaren biye da shi.
23 after him, repaired, Benjamin and Hasshub, over against their own house, —after him, repaired, Azariah son of Maaseiah son of Ananiah, beside his own house;
Can gaba da su, Benyamin da Hasshub ne suka yi gyare-gyaren a gaban gidansu, biye da su kuwa, Azariya ɗan Ma’asehiya, ɗan Ananiya ne ya yi gyare-gyaren kusa da gidansa.
24 after him, repaired, Binnui son of Henadad, a second length, —from the house of Azariah, unto the corner, even unto the pinnacle:
Biye da shi, Binnuyi ɗan Henadad ya yi gyaran wani sashe, daga gidan Azariya zuwa kusurwa,
25 Palal, son of Uzai, from over against the corner, and the tower that projecteth from the upper house of the king, which belongeth to the court of custody, —after him, Pedaiah son of Parosh.
sai Falal ɗan Uzai ya yi aiki ɗaura da kusurwa da kuma doguwar hasumiya daga fadar da take bisa kusa da shirayin masu tsaro. Biye da shi, Fedahiya ɗan Farosh
26 Now, the Nethinim, were dwelling in Ophel, —as far as over against the water-gate, on the east, and the tower that projecteth;
da masu hidimar haikali da suke zama a tudun Ofel ne suka yi gyare-gyaren har zuwa wani wuri ɗaura da Ƙofar Ruwa wajen gabas da kuma doguwar hasumiya.
27 after him, repaired, the Tekoites, a second length, —from over against the great tower that projecteth, even unto the wall of Ophel:
Biye da su, mutanen Tekowa suka yi gyaran wani sashe, daga babbar doguwar hasumiya zuwa katangar Ofel.
28 from beside the horse-gate, repaired the priests, every one over against his own house;
Daga Ƙofar Doki, firistoci ne suka yi gyare-gyaren, kowanne a gaban gidansa.
29 after him, repaired, Zadok son of Immer, over against his own house, —and, after him, repaired, Shemaiah son of Shecaniah, keeper of the east-gate;
Biye da su, Zadok ɗan Immer ya yi gyare-gyaren ɗaura da gidansa. Biye da shi, Shemahiya ɗan Shekaniya, mai tsaron Ƙofar Gabas ya yi gyare-gyare.
30 after him, repaired, Hananiah son of Shelemiah, and Hanun sixth son of Zalaph, a second length, —after him, repaired, Meshullam son of Berechiah, over against his chamber;
Biye da shi, Hananiya ɗan Shelemiya, da Hanun, ɗa na shida na Zalaf, suka gyara wani sashe. Biye da su, Meshullam ɗan Berekiya ya yi gyare-gyaren ɗaura da wurin zamansa.
31 after him, repaired, Malchijah son of Zorphi, as far as the house of the Nethinim, and the traders, —over against the muster-gate, even unto the ascent of the pinnacle;
Biye da shi, Malkiya, ɗaya daga cikin masu ƙera zinariya ya yi gyare-gyaren har zuwa gidan masu hidimar haikali da kuma’yan kasuwa, ɗaura da Ƙofar Bincike, har zuwa ɗakin da yake bisa kusurwar.
32 and, between the ascent of the pinnacle and the sheep-gate, repaired, the goldsmiths, and the traders.
Maƙeran zinariya da’yan kasuwa suka gyara wani sashi tsakanin ɗakin da yake bisa kusurwa da Ƙofar Tumaki.