< Malachi 2 >
1 Now, therefore, for you, is this charge, O ye priests: —
“Yanzu fa wannan gargaɗi dominku ne, ku firistoci.
2 If ye will not hear, and if ye will not lay it to heart, to give glory to my Name, saith Yahweh of hosts, then will I send among you the curse, and will curse your blessings, —and indeed I have cursed them, because ye are not at all laying it to heart.
In ba ku saurara ba, in kuma ba ku sa zuciyarku ga girmama sunana ba, zan aukar muku da la’ana, zan kuma la’antar da albarkunku. I, na riga na la’anta su, domin ba ku sa zuciyarku ga girmama ni ba, in ji Ubangiji Maɗaukaki.
3 Behold me! threatening, on your account, the seed, and I will scatter refuse upon your faces, the refuse of your festivals, —and one shall carry you away unto it;
“Saboda ku zan tsawata wa zuriyarku; zan watsa kashin dabbobin hadayunku a fuskokinku, a kuma kwashe ku tare da shi.
4 So shall ye know that I sent unto you this charge, —as being my covenant with Levi, saith Yahweh of hosts.
Za ku kuwa san cewa ni ne na aika muku da wannan gargaɗi domin alkawarina da Lawi yă ci gaba,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
5 My covenant, was with him, Life and Well-being, so I gave them to him—[I] as One to be revered— and he did revere me, — and, before my Name, dismayed, was he.
“Alkawarina da shi, alkawari ne na rai da salama, wanda na ba shi; domin yă girmama ni, ya kuwa girmama ni, ya kuma ji tsoron sunana ƙwarai.
6 The deliverance of truth, was in his mouth, and, perverseness, was not found in his lips, — In well-doing and in uprightness, walked he with me, and, multitudes, did he turn from iniquity.
Umarnin gaskiya yana a bakinsa, ba a kuma sami wani ƙarya a leɓunansa ba. Ya yi tafiya tare da ni cikin salama da adalci, ya kuwa juyo da mutane masu yawa daga zunubi.
7 For, the lips of a priest, should keep knowledge, and, a deliverance, should men seek at his mouth, — for, the messenger of Yahweh of hosts, he is.
“Gama ya kamata leɓunan firist su kiyaye ilimi, ya kamata kuma mutane su nemi umarni daga bakinsa, domin shi ne manzon Ubangiji Maɗaukaki.
8 But, ye, have departed out of the way, ye have caused multitudes to stumble at the deliverance, — ye have violated the covenant of Levi, saith Yahweh of hosts.
Amma sai kuka kauce hanya, ta wurin koyarwarku kuma kuka sa mutane da yawa suka yi tuntuɓe; kun keta alkawarin da na yi da Lawi,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
9 Therefore, I also, will suffer you to be despised and of no account unto all the people, —in proportion as none of you have been keeping my ways, but have had respect to persons, in giving your deliverance.
“Saboda haka na sa a rena ku, a kuma wulaƙanta ku a gaban dukan mutane, domin ba ku bi hanyoyina ba amma kuka nuna sonkai a al’amuran shari’a.”
10 Is there not, one Father, to us all? Did not, one GOD, create us? Wherefore should we deal treacherously one with another, profaning the covenant of our fathers?
Ashe, ba Mahaifi guda dukanmu muke da shi ba? Ba Allah ɗaya ne ya halicce mu ba? Don me muka keta alkawarin kakanninmu ta wurin cin amanar juna?
11 Judah, hath dealt treacherously, and, an abomination, hath been wrought in Israel, and in Jerusalem, — for Judah, had profaned, the holy place of Yahweh, which he had loved, and hath taken to himself the daughter of a foreign GOD.
Yahuda ya ci amana. An yi abin kunya a Isra’ila da kuma a Urushalima. Yahuda ya ƙazantar da wuri mai tsarkin da Ubangiji yake ƙauna, ta wurin auren’yar wani baƙon allah.
12 May Yahweh, cut off, from the man that doeth it—him that crieth out and him that answereth, out of the tents of Jacob, — him also that bringeth near a present to Yahweh of hosts.
Game da mutumin da ya aikata wannan, ko wane ne shi, bari Ubangiji yă yanke shi daga tentunan Yaƙub, ko da ma ya kawo hadayu ga Ubangiji Maɗaukaki.
13 And, this, a second time, will ye do, covering with tears, the altar of Yahweh, weeping and making outcry, —because he will not again turn unto the gift, and receive [it] with acceptance, at your hands?
Ga kuma wani abin da kuke yi. Kukan cika bagaden Ubangiji da hawaye. Kukan yi kuka kuna ihu gama Ubangiji ba ya mai da hankali ga hadayunku ko yă karɓe su da farin ciki.
14 Yet ye say, For what cause? Because, Yahweh, hath been witness between thee and the wife of thy youth, with whom, thou, hast dealt treacherously, though, she, was thy consort, and thy covenant wife.
Kukan ce, “Don me ba ya karɓan hadayunmu?” Ai, domin Ubangiji ya zama shaida tsakaninka da matar ƙuruciyarka, gama ka keta amanar da ka yi mata, ko da yake ita abokiyar zamanka ce, matar aurenka ta alkawari.
15 Now was it not, One, [who] made [you] who had, the residue of the spirit? What, then, of that One? He was seeking a godly seed. Therefore should ye take heed to your spirit, and, with the wife of thy youth, do not thou deal treacherously.
Ashe, Ubangiji bai maishe su ɗaya ba? Cikin jiki da ruhu, su nasa ne. Me ya sa suke ɗaya? Domin yana neman’ya’ya masu tsoron Allah. Saboda haka sai ka lura da kanka, kada kuma ka ci amanar matar ƙuruciyarka.
16 For he hateth divorce, saith Yahweh, God of Israel, him also who covereth with violence his own clothing, saith Yahweh of hosts, —therefore should ye take heed to your spirit, and not deal treacherously.
“Na ƙi kisan aure,” in ji Ubangiji, Allah na Isra’ila. “Na kuma ƙi mutumin da ya rufe kansa da tashin hankali kamar riga,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. Saboda haka sai ka lura da kanka, kada kuma ka ci amana.
17 Ye have wearied Yahweh with your words, and yet ye say, Wherein have we been wearisome? When ye have said, Everyone who doeth wrong, is right in the eyes of Yahweh, and, in them, he hath taken delight, or, Where is the God of justice?
Kun sa Ubangiji Maɗaukaki ya gaji da maganganunku. Sai kuka ce, “Yaya muka sa ya gaji?” Kun yi haka ta wurin cewa, “Duk waɗanda suke aikata mugunta, mutanen kirki ne a gaban Ubangiji, yana kuwa jin daɗinsu,” kuna kuma cewa, “Ina Allah mai adalci yake?”