< Luke 4 >

1 And, Jesus, full of Holy Spirit, returned from the Jordan, and was led in the Spirit in the desert,
Yesu kuwa cike da Ruhu Mai Tsarki, ya dawo daga Urdun, Ruhu kuma ya kai shi cikin hamada,
2 forty days, —being tempted by the adversary; and he did eat nothing in those days, —and, when they were concluded, he hungered.
inda kwana arba’in, Iblis ya gwada shi. Bai ci kome ba a cikin kwanakin nan, a ƙarshensu kuwa ya ji yunwa.
3 And the adversary said to him—If thou art God’s, Son, speak unto this stone; that it become bread.
Iblis ya ce masa, “In kai Ɗan Allah ne, ka faɗa wa wannan dutse yă zama burodi.”
4 And Jesus made answer unto him—It is written: Not, on bread alone, shall, man, live.
Yesu ya amsa ya ce, “A rubuce yake, ‘Ba da abinci kaɗai mutum zai rayu ba.’”
5 And, leading him up, he shewed him all the kingdoms of the inhabited earth, in a moment of time.
Iblis ya kai shi can kan wani wuri mai tsawo, ya nunnuna masa a ƙyiftawar ido dukan mulkokin duniya.
6 And the adversary said to him—Unto thee, will I give this authority, all together, and their glory; because, unto me, hath it been delivered up, and, to whomsoever I please, I give it:
Ya ce masa, “Zan ba ka dukan ikonsu da darajarsu, gama ni aka danƙa wa, kuma zan bai wa duk wanda na ga dama.
7 Thou, therefore, if thou wilt worship before me, it shall all, be thine.
Saboda haka in ka yi mini sujada, dukan wannan zai zama naka.”
8 And, answering, Jesus said to him—It is written: The Lord thy God, shalt thou worship, and, unto him alone, render divine service.
Yesu ya amsa ya ce, “A rubuce yake, ‘Ka yi wa Ubangiji Allahnka sujada, kuma shi kaɗai za ka bauta wa.’”
9 And he led him into Jerusalem, and set him upon the pinnacle of the temple, —and said [to him]—If thou art God’s, Son, cast thyself, from hence, down;
Sai Iblis, ya kai shi Urushalima ya sa ya tsaya a kan wuri mafi tsayi na haikali ya ce, “In kai Ɗan Allah ne, ka yi tsalle daga nan zuwa ƙasa.
10 for it is written—Unto his messengers, will he give command concerning thee, to keep vigilant watch over thee, —
Gama a rubuce yake, “‘Zai umarci mala’ikunsa game da kai, su kiyaye ka da kyau;
11 And, On hands, will they take thee up, lest once thou strike, against a stone, thy foot.
za su tallafe ka da hannuwansu, don kada ka buga ƙafarka a kan dutse.’”
12 And Jesus, answering, said to him—It is said: Thou shalt not put to the test the Lord thy God.
Yesu ya amsa ya ce, “An ce, ‘Kada ka gwada Ubangiji Allahnka.’”
13 And, having concluded every temptation, the adversary departed from him until a fitting season.
Da Iblis ya gama dukan wannan gwajin, ya bar shi sai lokacin da wata dama ta samu.
14 And Jesus returned, in the power of the Spirit, into Galilee; and, a report, went out along the whole of the region, concerning him;
Yesu ya koma Galili cikin ikon Ruhu. Labarinsa kuwa ya bazu ko’ina a ƙauyuka.
15 and, he, began teaching in their synagogues, being glorified by all.
Ya yi ta koyarwa a majami’unsu, kowa kuwa ya yabe shi.
16 And he came into Nazareth, where he had been brought up, and entered, according to his custom, on the sabbath day, into the synagogue, —and stood up to read.
Ya tafi Nazaret, inda aka yi renonsa. A ranar Asabbaci kuma, ya shiga majami’a kamar yadda ya saba. Sai ya miƙe don yă yi karatu.
17 And there was handed to him a scroll of the prophet Isaiah; and unfolding the scroll, he found the place where it was written:
Aka kuwa ba shi naɗaɗɗen littafin annabi Ishaya. Da ya buɗe, sai ya sami wurin da aka rubuta,
18 The Spirit of the Lord, is upon me, because he hath anointed me—to tell glad tidings unto the destitute; He hath sent me forth, —To proclaim, to captives, a release, and, to the blind, a recovering of sight, —to send away the crushed, with a release;
“Ruhun Ubangiji yana kaina, domin ya shafe ni, in yi wa matalauta wa’azin bishara. Ya aiko ni in yi shelar’yanci ga’yan kurkuku, in kuma buɗe idanun makafi, in ba da’yanci ga waɗanda aka danne.
19 To proclaim the welcome year of the Lord.
In yi shelar shekarar tagomashin Ubangiji.”
20 And, folding up the scroll, he handed it to the attendant, and sat down; and, the eyes of all, in the synagogue, were intently fixed upon him;
Sai ya naɗe naɗaɗɗen littafin ya mayar wa mai hidimar, ya kuma zauna. Dukan idanun waɗanda suke a majami’ar, suka koma a kansa.
21 and he began to be saying to them—This day, is fulfilled this scripture, in your ears.
Sai ya fara ce musu, “A yau, Nassin nan, ya cika a kunnenku.”
22 And, all, were bearing witness to him, and marvelling at the words of favour which were proceeding out of his mouth; and they were saying—Is not, this, the, son of Joseph?
Duk suka yabe shi, suka yi mamakin kalmomin alheri da suke fitowa daga bakinsa. Suka yi tambaya, suna cewa, “Anya, wannan ba ɗan Yusuf ba ne?”
23 And he said unto them—By all means, ye will speak to me this similitude: Physician! heal, thyself, —Whatsoever things we have heard of coming to pass in Capernaum, do here also, in thine own country.
Yesu ya ce musu, “Tabbatacce, na san za ku faɗa mini karin maganan nan, ‘Likita, warkar da kanka! Ka kuma yi abin da muka ji ka yi a Kafarnahum, a nan garinka.’”
24 And he said—Verily, I say unto you, No prophet, is, welcome, in his own country,
Ya ci gaba, da ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, babu annabin da ake yarda da shi a garinsa.
25 And, of a truth, I say unto you—Many widows, were in the days of Elijah, in Israel, when the heaven was shut up three years and six months, when there came a great famine upon all the land;
Ina tabbatar muku a zamanin Iliya, akwai gwauraye da yawa a Isra’ila, sa’ad da aka rufe sararin sama har shekara uku da rabi, aka kuma yi yunwa mai tsanani ko’ina a ƙasar.
26 And, unto none of them, was Elijah sent, save unto Sarepta of Sidonia, unto a woman that was a widow.
Duk da haka, ba a aiki Iliya ga ko ɗaya a cikinsu ba. Sai dai zuwa ga wata gwauruwa da take a Zarefat, a yankin Sidon.
27 And, many lepers, were in Israel, in the time of Elisha the prophet, and, not one of them, was cleansed, save Naaman the Syrian.
Akwai kuma mutane da yawa a Isra’ila masu kuturta a zamanin annabi Elisha, amma ba ko ɗayansu da aka tsarkake sai Na’aman mutumin Suriyan nan kaɗai.”
28 And all were filled with wrath, in the synagogue, as they heard these things.
Dukan mutanen da suke cikin majami’a suka fusata ƙwarai da jin wannan.
29 And, rising up, they thrust him forth outside the city, and led him as far as a brow of the hill on which their city was built, —so that they might throw him down headlong.
Suka tashi, suka fitar da Yesu bayan gari, suka kai shi goshin tudun da aka gina garin, don su ture shi ƙasa,
30 But, he, passing through the midst of them, went his way.
amma sai ya bi ta tsakiyar taron ya yi tafiyarsa.
31 And he came down into Capernaum, a city of Galilee. And he was teaching them on the sabbath;
Sai ya tafi Kafarnahum, wani gari a Galili, a ranar Asabbaci kuma, ya fara koya wa mutane.
32 and they were being struck with astonishment at his teaching, because, with authority, was his word.
Suka yi ta mamakin koyarwarsa, domin saƙonsa yana da iko.
33 And, in the synagogue, was a man having a spirit of an impure demon; and he cried out with a loud voice—
A cikin majami’ar, akwai wani mutum mai aljani, wani mugun ruhu. Mutumin ya ɗaga murya da ƙarfi ya ce,
34 Let be! What have we in common with thee, O Jesus, Nazarene! Hast thou come to destroy us? I know thee, who thou art, —The Holy One of God.
“Wayyo! Ina ruwanka da mu, Yesu Banazare? Ka zo ne don ka hallaka mu? Na san wane ne kai, Mai Tsarki na Allah!”
35 And Jesus rebuked it, saying—Hold thy peace! and go forth from him. And the demon, throwing him into the midst, went forth from him, doing him no hurt.
Yesu ya tsawata masa da ƙarfin cewa, “Yi shiru! Ka fita daga cikinsa!” Sai aljanin ya fyaɗa mutumin da ƙasa a gabansu duka, sa’an nan ya fita, ya bar shi ba wani rauni.
36 And amazement came upon all, and they began to converse one with another, saying—What is this word, that, with authority and power, he giveth orders unto the impure spirits, and they go forth?
Dukan mutanen suka yi mamaki, suka ce wa junansu, “Wace irin koyarwa ce haka? Da ƙarfi da iko, yana ba wa mugayen ruhohin umarni suna kuma fita!”
37 And a noise concerning him began to go out into every place of the country around.
Labarinsa kuwa ya bazu ko’ina a cikin ƙasar.
38 And, rising up, from the synagogue, he went into the house of Simon. Now, the mother-in-law of Simon, was in distress with a great fever; and they made request to him concerning her.
Yesu ya fita daga majami’ar, ya tafi gidan Siman. Surukar Siman kuwa tana fama da zazzaɓi mai tsanani, sai suka roƙi Yesu yă taimake ta.
39 And, standing over her, he rebuked the fever, and it left her; and, instantly arising, she began to minister unto them.
Sai ya sunkuya kusa da ita, ya kuma tsawata wa zazzaɓin, sai zazzaɓin ya sāke ta. Nan take ta tashi, ta yi musu hidima.
40 But, as the sun was going in, they one and all, as many as had any sick with divers diseases, brought them unto him; and, he, upon each one of them laying, his hands, was curing them.
Rana tana fāɗuwa, sai mutane suka yi ta kawo wa Yesu dukan waɗanda suke da cuta iri-iri, sai ya ɗibiya wa kowannensu hannuwansa, ya warkar da su.
41 And demons also were going forth from many; crying aloud, and saying—Thou, art the Son of God. And, rebuking them, he suffered them not be talking; because they knew him to be, The Christ.
Bugu da ƙari, aljanu suka fiffita daga cikin mutane da yawa suna ihu suna cewa, “Kai Ɗan Allah ne!” Amma ya kwaɓe su, ya hana su magana, don sun san cewa shi ne Kiristi.
42 And, when it was day, going forth, he journeyed into a desert place; and, the multitudes, were seeking after him, and they came unto him, and would have detained him, that he might not depart from them.
Da gari yana wayewa, sai Yesu ya je inda ba kowa. Mutane suka yi ta nemansa, da suka zo inda yake, sai suka yi ƙoƙari su hana shi barinsu.
43 But, he, said unto them—To the other cities also, I must needs tell the good-news of the kingdom of God, because, hereunto, was I sent forth.
Amma ya ce, “Dole in yi wa’azin bisharar mulkin Allah ga sauran garuruwa, saboda wannan ne aka aiko ni.”
44 And he was proclaiming in the cities of Judaea.
Sai ya dinga yin wa’azi a majami’un Yahudiya.

< Luke 4 >